← Book details Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 64

Sashe 36

Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ban san sunan garin ba, amma dai garin babu sauƙi suna da wahalar sha'ani ya ce, koyaushe za'a iya jin dawowarsa a wayar da mukai dashi jiya" sai ta ɗan ɓata fuska kuma ta ce "Wait, meye ne kake nemansa har haka?" Mu'allim ya harareta kafin ya ce "kuɗin aure zai kai mini ne in sha Allah"

"Oh really?"

"Yeah.... In sha Allah"

"Allahumma barik, wace matar her name?"

"Ban san sunanta ba for now"

Da rashin fahimta Diyanah ta ce "Are you kidding me? Taya hakan zai faru?" Ya ɓata fuska ya ce "Ƙaddara. Yarinyar tana kitchen ɗinku, please ki sama mini sunanta da number waya har ma da address me gabaɗaya nake so a yi, rana ɗaya za'ayi bikinmu da Akhy Liman" sai Diyanah ta rage tafiya kaɗan ba tare data ce komai ba suka sauka ƙasa. Gidan babu hayaniya sanda suka sakko Mamy bata nan sai Nadiyaah da Azizah wacce take ta yi wa Nadiyaah magana tana amsata jifa-jifa yaran basa shiri da Azizah tunda suka ji ita zata auri Baffansu, suna ganin kamar age mate suke da Azizah a nasu tunanin,kuma bata dace da Baffa ba, infact basa buƙatar Baffansu ya yi aure idan akwai abin da Nadiyaah da Diyanah suka tsana suke yin kuka a kan shi sosai da kwanciya ciwo, su ji ance Baffa am ɗinsu zai yi aure, wani irin mugun son shi suke yi da kishinsa mai tsanani, kishin da ya kamata ace murgayiya mahaifiyarsu ita za ta yi wannan kishin, sai ta tafi ta bar musu suke damawa. Suna ganin abin kunya ne a gare su ace Baffa am ɗinsu ya yi mata kuma har ta haifi baby, ta haifi little sis or brother. Basu da sani da cewa, shi Baffa da kan shi baya ra'ayin auren, uwa uba bashi da lafiya ta kasance da mace a dalilin hatsarin da ya taɓa yi shekarun baya. Baya jin feelings na kowacce mace, kamar yadda bai taɓa ganin kyawun ko wacce ɗiya mace a idanunsa ba, babu wata mace data taɓa burge shi a rayuwa.

Diyanah ko Azizah bata kalla ba ta shige Kitchen tana shiga aroma ɗin girki na shiga hancinta, ta ƙarasa idanunta akan Iftihal ta ce "sannu da aiki sister?" Cikin sauri Iftihal ta durƙusa ta ce "Barka da yamma" sosai Diyanah ta ji rashin jin daɗi ta ɗagota ta ce

"Ki bar durƙusawa babu kyau. Sunana Diyanah Sayyadi Baffa. Kefa?" Ta ce

"Iftihal, sunana Iftihal"

"Ma sha Allah. Kin kammala ne?" Iftihal ta ce

"Eh Anty"

"Who's Anty abeg? Call me by my name" zuba mana abincin a babban plate with 2 spoon me and Nadiyaah than you, Nadia bata cin abinci da spoon irin Baffa am ce "A'a nikam Allahamdulillah, bari na zuba muku" Diyanah gefe kawai ta koma ta zubawa fuskar Iftihal ido, bakyau ne ke bata mamaki ba, itama kyau gadon nasu gidanne, amma ta rasa me take kallo a fuskar Iftihal. "Kina wacce unguwa ne?" A hankali ta ce "Kankarofi" sai Diyanah ta buɗe ido ta ce "Ya rabb, tun daga can sannu sister. Give me your number so that muke gaisawa lokaci zuwa lokaci" murmushin da ake kira da yaƙe kawai Iftihal ta yi ta ce "Bani da waya, sai dai ya yayana idan kina so" wani irin rashin jin daɗi ya wanzu a zuciyar Diyanah ta ce "Ba damuwa saka mini" wayarta ƙirara iPhone 15 ta miƙawa Iftihal ta ce "Saka mini number tasa, ki kira yanzu ki faɗa masa sunana ya yi saving" Bayan ta saka number Yaa Jaheed nan take kira, abinka da talaka wanda yake nema ya ɗauka customer ne tuni ya ɗauki kiran ya ce "Hello...." A hankali muryarsa ta sauka a kunnen Diyanah ta yi shiru tana saurare.

"Yaa Jaheed ni ce Iftihal"

"Masoyiyyar" ta ce "Na'am"

"Kina ina? Wayar wacece wannan kika kira da ita?"

"Wani gida Yaa Jaheed ka yi saving number nan ka ji" ta cikin wayar ya ce "Bangane ba, number wanne ƙaton kika samu da za ki ce na yi saving? Ya sunansa Tanimu ko? Wayar ma na san rakani kashi ce yasin, to ba zan saka number nan a Vivo ta me capacity ba" Murmushi kawai Diyanah ta yi, Iftihal kuma ciro wayar ta yi a kunnenta tana jujjuyawa ta kalli Diyanah ta ce

"Ya sunanta?'

"IPhone 15"

"Kan uba IPhone 15, masoyiya wayar waye wannan maza bashi a barsa kar ki fasa ki ja mana masifa muna lallaɓa rayuwarmu" a hankali ta ce "In sha Allah. Ka yi saving ka saka Diynaah" a fili ya ce "Wow, sunan larabawa ne, Diynaah wa kar Innti taga number ta ɗauka lalacewa na yi na fara kula ƴan'matan Kano" Diynaah ce ta amshi wayar ta ce "Ahky Jaheed ka saka Diynaah Sayyadi Baffa" ji ya yi komai nasa ya tsaya cak, Sayyadi Baffa kamar fa babban malamin da ake tutiya dashi a Kano da Nigeria bakiɗaya.

"To. In sha Allah" ya amsa a saɓule yana kashe kiran. Aka ce da Iftihal ko ta bar abincin za'a iya a sarar shi ta tabi dashi gida, da farko taƙi amma data tuna yanayin gidan sai ta tattara abincin da nama fal da kayan fruits. Lokacin ana kiran sallar issha ne, sai da ta yi sallah kafin nan. Da ƙyar Mamy ta lallaɓa Iftihal akan Mu'alim ya kawo ta gida.

*

Tunda suka dawo gida Engineer yake ta jera mata sannu, ita kuma sai langwaɓe masa take yi da kukan shagwaɓa. "Kin gani ko baby? Ai na faɗa babu inda ba'a san Golden voice ba a faɗin Kano, ina da tabbacin sai kin zama babbar ƴar jaridar da za'ayi ko yi da ita wacce zata shiga kundin tarihi kuma ta zama abar tunawa. Wannan ma ɗaukaka ce kuma ta ɓangarena ba zan bari abin da akai miki ya tafi a banza ba, tunda naga gidan rediyon taku ba ta yi yunƙurin komai ba" Ahlam ta ce "Abban Mufeed, ni wannan abin ya yi mini daɗi duk da ya cuce ni daya ɓare mini baki gida biyu ai daya cuce ni ya cuci masu ƙauna ta wallahi" Engineer ya ce

"Kuma da ya cuci mijinki ma" sai ta yi saurin sauya maganar da faÉ—in. "Zan koma gidan matar na yi hira da ita, zan É—ora hirar a wani sabon program É—inmu na MU FARKA MATA" cikin jin daÉ—i da nuna goyon baya ya ce

"A'a ka da ki koma gidan nan baby, haka kawai su danne mini ke su yanka na shiga uku" ta É—an murmusa kaÉ—an ta ce "Uhm"

"Be careful my love ok?"

"By the grace of God"

Miƙewa ta yi ta musu sai da safe ya shige ɗakinta, wayarta ta ɗakko ta kunna cikin sa'a tana shiga WhatsApp taga Nurse ɗin ta tura mata vedion, kai tsaye ta shiga Facebook ta yi positng vedion da caption ɗin. "Beging a Journalist isn't easy" cikin ƙaramin lokaci ta tara comments ɗin mutane sama da dubu biyu wanda kusan duka rabinsa jaje suke yi mata da ƙara mata ƙarfin zuciya da confidence, bata taɓa tunanin haka aka santa a social media ba sai yau ɗin nan. Ta shiga tambayar kanta kenan muryarta bata tafi a banza ba? Kenan duk ƙoƙarin da take yi bai shuɗe a banza ba, sannu a hankali take jin nutsuwa na sauka a zuciyarta, nutsuwar data haɗo mata da wani wish and hope, suka cure waje guda tare da zama big dream ɗinta na rayuwa, hakan ya sake tunatar mata da burinta na ɗaukaka a duniyar aikin jarida, ba zata taɓa manta wulaƙanci da cin mutumcin da Yussy ta yi mata. Ko kalaman data jefe ta dasu bata buƙatar tunawa, balle ita kanta Yussy ɗin. Sai dai me? Abin ya zame mata kamar yadda a duk sanda ta runtse idanunta ko kuma tazo kwanciya bacci sai maganganun sun dawo cikin kanta, sun maimaita kan su.

Hakan ɗin ce ta kasance a yanzu ma, ji ta yi kamar a daidai wannan lokacin ne komai ke faruwa tsakaninta da Yussy muryarta ta ji tana sauka a kunnenta. "Ai Ahlam ko za ki ƙarar da duk abin da kika mallaka ba za ki taɓa bin layin dana bi ba, balle ki huce ni. Na ba ki shawara ba ki ɗauka ba, zan sake ba ki a yanzu wataƙila ki yi aiki da ita zuwa gaba sai ki gode mini" a wancan lokacin Ahlam na tsaye fitowar ta kenan daga office ɗin Editor-in-chief taje kai masa wani labari data samu akan hanyarta ta zuwa gidan rediyon, lokacin tana matsayin News Gatherer, sai ya nuna labarin bai yi ba, ba balle ya samu ƙarbuwa ba. A lokacin har kuka ta kusa yi saboda baƙinciki labarin wani dattijo ne da ya yi wa yarinya ƴar 3 years fyaɗe, amma saboda bata ɗauki rahoton murya ba ya yi watsi da ita. "Sir wallahi yanzu labarin nan ya faru babu wata gidan jarida da suka wallafa ko gidan rediyon da suka sanar, Bright Fm ce zata zama ta farko ka yarda dani akan idanuna aka kama dattijon" wani kallo ya yi mata irin na bata isa ba, yaushe ma ta shigo aikin?

"Look Ahlam, bawai da ka muke watsa labarai ba, abu muke na ilimi wanda mutane za su yarda dashi. Idan muka yi saken da aka saka wannan labarin mutane da yawa za su daina sauranmu" cikin rawar murya ta ce "Sir don me ya sa za su daina?" A taƙaice ya ce
Chapter 36 · 0% Book details