Sashe 34
Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Sai ya mayar da furar cikin rubar, ta ƙasan ido take kallon shi sai ta ce "Zan sha fa" Yana jinta ya share sai daya kammala tura saƙo da keyboard ɗin wayarsa ya sake ɗebo furar ya nufi bakinta, ta buɗe ƙaramin bakin ya shiga bata, idanunta a cikin nasa, kamar yadda shima yake kallon ta. Murmushi ta yi masa, shima ya sakar mata murmushin, ta lumshe idanunta shima yaja idanun ya lumshe. Idanu ɗaya ta kashe masa, a hankali yaja idanunsa na dama ya kashe mata. "Yaa Sam ɗina" ya murmusa ya ce
"Nanaata"
"Na ƙoshi"
Tissue ya ɗakko ya ɗora hannunsa a kanta ya ɗan matso da ita ya shiga goge mata bakin, bayan ya kammala ya ɗauki hijab ɗinta da Babban yaya ya kawo ya saka mata. Sauran furar ya fara sha shima yana cikin sha Babba yaya ya shigo. Kallonsu ya yi su biyun babu wanda ya yi wa magana ya kwashi kayansu zuwa waje. Sakkowa ya yi ya miƙa mata hannunsa ta saka nata a ciki suka nufi fita daga asibitin suna zuwa waje Yaa Sam ya yi saurin sakin hannun Ana. Napep suka shiga Ana da Yaa Sam na baya, Babban yaya a gaba suka nufi Kankarofi.
***
Ta shafe awanni huɗu a bakin ruwan, tun tana saka rana zata sake ganinsa har ya fitar da rai. Hannunta ta miƙa kaɗan ta share hawayen da yake bin fuskarta a sanyaye ta ce "Yau ma kaɗo bai zo ba, ina kaɗona? Yana ina?"
Taja idanunta ta lumshe a raunace ta ce "Innata.....
"Su waye suka kashe mini Innata?" Ta fashe da kukan halin maraican da take ciki.
***
YARI.
Yau tunda Gana ta tashi, sai ta tashi da wata kalar maita kamar ta ci babu ga ranar rugar yau a buɗe take ta rasa inda zata saka kanta ta ji daɗi, idan ta juya nan sai ta yi karta da haƙori idan ta sake juya sai ta karta haƙori idanunta ya yi jajur har barkono ta watsa a bakinta ɗanye jawaur dashi amma ƙanƙarar maitar bata lafa ba. Burin da ta ci na samu kuɗi ya rushe ta shiga ɗakinta can uwar ɗaka taja ƙofa ta rufe, inda take ajjiye kayan tsafinta ta sunkuya ta ɗakko ta zaro wani baƙin ƙyalle ta ciro wata ƴar ƙaramar aba, mai kama da tsokar nama ta dunƙule a hannunta ta shiga surutai yana yafa jan yadi, nan take sai ga kurwar jaririn Kulu ta koma ɗanshila wanda ba'a jima da ƙinƙishewa ba. Ta kwantar dashi ta murɗe kan ta yi cilli dashi kamar idanunta za su faɗo waje, ta cilla shi cikin ruwan zafi ta fiffige gashi ta ɗora sulale da jini-jini a jikinsa ta dinga ɗauka tana ci tsabar masifar da ta yi mata yawa. "Wayyo.... Wayyo daɗi, naman jariri akwai Musulmin daɗi wallahi"
Soyawa ta yi tana gamawa ta juye a ƙaramin filast ta tsiyaye man soyar a ƙaramar roba. "Naman jariri yafi kowanne daɗi, dashi da tayin da ba'a haifa ba. Inama Kulu ta sake haihuwar wani. Oh ni Gana ina zanga wani jinjirin yanzu da zan ci? Waye ke da ciki?"
"Gafaranku dai"
"Allah yai mana" ta amsa sallamar tana buɗe ƙofa ta fito waje. Washe baki ta yi ta ce "A'a wa nake gani kamar Hindatu"
"Ni ce rana tsaka Gana"
Gana ta ce "Lale maraba da Hindatu" Ta shimfiɗa assabari a gefen inuwa ta ce "Yada zango mana Hindatu, jiyan nan kika faɗo mini a rai nace muna maƙwabta amma ba zumunci walle kunya ta yi mana yawa"
Hindatu ta ce "Bari ke dai Gana, surfe da casa ne ya azo ni gaba. Yanzu ma ina zaune ina taɗin zuci na ji ƙamshi ta saman kanta shine na leƙo nima ayi dani, ko me gidan ya yi miki tsaraba" Gana ta zubawa Hindatu ido na wani lokaci kafin ta ce "kayya, Ƙamshin man ƙuli dana soya da albasa kika ji. Bari na kawo miki ruwa da abinci ko?" Miƙewa ta yi ta zuba mata wake da gero da ƙuli ta ɗauki man data soya jaririn Kulu dashi ta kelaya saman abincin ta ajjiye mata ta kawo ruwan tulo me sanyi a kofi ta ajjiye.
"Bisimillah Hindatu"
"Hadda wahala haka Gana?" Bakinta har dalalar da yawo yake tsabar kwaɗayi ta fara cin abincin. "Gana wai ni kowa ina Batty ana ta raɗe-raɗin yaro hura mata iskar balo a ciki shi ne kika ɗauke ta, wasu ma sun ce saboda uwarta bata raye kin kasa riƙe marainiyyar Allah" Gana ta fashe da kuka tana kunce bakin zani ta ce
"Na shiga uku kuma ni Gana, duk ɗawainiyyar da nake da Batty babu wanda ya yaba sai yanzu da jarrabawa ta same ni? Yadda naga Saleh yana turmushe Batty a zaure da murje ƴan ƙirjinta Allah Ya nuna mini Annabi. Ki faɗa mini da ban ɗauki matakin ɗauke Batty ba ai da tuni ya hura mata iska a ciki mun shiga uku. Da uwar uwar Batty dani nono ɗaya muka sha fa?" Hindatu ta ce "Sai haƙuri, mutane akwai su da gadon zancen wasu. Gana kin ji abincin nan inda ya yi daɗi? Ban taɓa jin man ƙuli da daɗi irin wannan ba, ko nama aka bani ba lalle ya yi daɗin wannan man ba" Gana ta yi murmushi ta fara tunanin yadda zata sawa Hindatu ƙanƙarar maita ta yi maganin shegen kwaɗayinta. Ta ce "Naman ma ina dashi, kuma idan kikai biyayya ma irin wannan kullum dashi za ki ci abinci na rantse" Hindatu ta waro ido waje ta ce
"Don Manzo?"
"Taso muje na ba ki nama da wani man" cewar Gana tana miƙewa tsaye ta yi cikin ɗakinta zumbur Hindatu ta miƙe tare da bin bayan Gana tana tafe tana riƙe zani da suɗe yatsun hannunta tana tunanin kakarta ta yanke saƙa daman ta biyu ta shigo gidan....
Littafin HIYAAM na kuÉ—i ne akan 1500. Muna tsarin discount akan mutanen farko da suka fara payment, daga book 1 2 3 za su biya 1k kacal. Wannan Discount É—in ana kammala free pages an rufe.
Mutanen farko da suka fara payment na HIYAAM za su biya 1k kacal ne.
Idan mukai limit da yawa za mu yi Hiyaam a WhatsApp ne, idan ba'a samu limit ba, za'ayi a Telegram da ArewaPen. Kana da ikon siyawa ƙawayenka, ko ka yi sponsoring wa jama'a domin Allah ko kuma a tallata maka business ɗinka.
Wannan tafiyar sabuwa ce, baku taɓa cin karo da ita ba.
0116886423
Union Bank
Na'ima Sulaiman S
Shaidar biya.
08164069385 ko
08082101373
A yi weekend lafiya.
*H I Y A A M*
Page 10: The Girl Wagered Away
Bright pens
Yota/001
Distance means so little when someone means so much. May Allah watch over you wherever you are. NAZEEFAH SABO NASHE.
Mun yi chapter 14 a ArewaPen.
Turus Gana ta tsaya a bakin ƙofar tana nazari sai kuma ta juya da murmushi ta ce "Hindatu ina ganin ki bari zan shigo na kawo miki, tunda har man ya yi miki daɗi" a zuciyarta kuma ta ce "Sai na ba ki ƙanƙarar maitar ki ji idan maitar daɗi gare ta shasha" ta yi furucin haɗe da yin gatsine tana me haɗawa da ƙwafa a lokaci guda.
*
MD a baƙin ƙofar room ɗin da aka ajjiye Ahlam ya tsaya ya harɗe hannayensa a ƙirji zaka rantse da Allah ba sashin dasu Ahlam da nurse ɗin yake kallo ba. Hawayen azaba ne kawai yake fita daga cikin idanun Ahlam yana bin kumatunta. Nurse dake riƙe da kayan Treatment ta ce "Sannu Golden voice" "Kin sanni ne?" Ahlam ta furta da ƙyar tana cije laɓɓanta da yarfar da hannunta sbd zafi
Nurse ta ce "E. Bake ce Ahlam Abdallah Kurmi ba, me yin dandalin nishaɗi program ɗin samari da ƴan mata a Bright Fm? Ina bibiyar shafinki na Facebook da Tiktok" duk da a cikin halin ciwo Ahlam take sai ta ji wani irin farinciki mara misaltuwa bata taɓa tunanin zata je wani waje a nuna an santa ba a dalilin aikinta na jarida, sai ta ji wani irin courage da confidence sun haɗe mata waje guda, ga wani hope data samu a furucin Nurse. Ta ɗan yi yaƙe ta ce "Thanks"
"Muke da godiya ai Golden voice" ta faÉ—a da zumuÉ—i na farinciki
"Idan an kammala treatment ɗin sai ku ƙarasa hirar taku ko?" Cewar Dr yana riƙe almaƙashi a hannunsa. Shiru Nurse ta yi ita kuma Golden voice ta kalli Dr a hankali cikin ƙasa da murya saboda har lokacin jini ke zuba a wuyanta ta ce "Sister ko za ki ara mini wayarki na yi vedio sai ki tura mini ta WhatsApp?" Cikin sauri Nurse ta ce "da gudu ma, Golden voice guda yadda nake mutuwar son programs ɗinki babu wanda bai san sunanki ba a bakina musamman ƴan gidanmu" wani yalwataccen murmushi Ahlam ta saki cike da jin daɗi da alfahari ta ce. "Ai har photo za mu yi, zan yi inviting naki zuwa shirin dandalin nishaɗi sister"
"Nanaata"
"Na ƙoshi"
Tissue ya ɗakko ya ɗora hannunsa a kanta ya ɗan matso da ita ya shiga goge mata bakin, bayan ya kammala ya ɗauki hijab ɗinta da Babban yaya ya kawo ya saka mata. Sauran furar ya fara sha shima yana cikin sha Babba yaya ya shigo. Kallonsu ya yi su biyun babu wanda ya yi wa magana ya kwashi kayansu zuwa waje. Sakkowa ya yi ya miƙa mata hannunsa ta saka nata a ciki suka nufi fita daga asibitin suna zuwa waje Yaa Sam ya yi saurin sakin hannun Ana. Napep suka shiga Ana da Yaa Sam na baya, Babban yaya a gaba suka nufi Kankarofi.
***
Ta shafe awanni huɗu a bakin ruwan, tun tana saka rana zata sake ganinsa har ya fitar da rai. Hannunta ta miƙa kaɗan ta share hawayen da yake bin fuskarta a sanyaye ta ce "Yau ma kaɗo bai zo ba, ina kaɗona? Yana ina?"
Taja idanunta ta lumshe a raunace ta ce "Innata.....
"Su waye suka kashe mini Innata?" Ta fashe da kukan halin maraican da take ciki.
***
YARI.
Yau tunda Gana ta tashi, sai ta tashi da wata kalar maita kamar ta ci babu ga ranar rugar yau a buɗe take ta rasa inda zata saka kanta ta ji daɗi, idan ta juya nan sai ta yi karta da haƙori idan ta sake juya sai ta karta haƙori idanunta ya yi jajur har barkono ta watsa a bakinta ɗanye jawaur dashi amma ƙanƙarar maitar bata lafa ba. Burin da ta ci na samu kuɗi ya rushe ta shiga ɗakinta can uwar ɗaka taja ƙofa ta rufe, inda take ajjiye kayan tsafinta ta sunkuya ta ɗakko ta zaro wani baƙin ƙyalle ta ciro wata ƴar ƙaramar aba, mai kama da tsokar nama ta dunƙule a hannunta ta shiga surutai yana yafa jan yadi, nan take sai ga kurwar jaririn Kulu ta koma ɗanshila wanda ba'a jima da ƙinƙishewa ba. Ta kwantar dashi ta murɗe kan ta yi cilli dashi kamar idanunta za su faɗo waje, ta cilla shi cikin ruwan zafi ta fiffige gashi ta ɗora sulale da jini-jini a jikinsa ta dinga ɗauka tana ci tsabar masifar da ta yi mata yawa. "Wayyo.... Wayyo daɗi, naman jariri akwai Musulmin daɗi wallahi"
Soyawa ta yi tana gamawa ta juye a ƙaramin filast ta tsiyaye man soyar a ƙaramar roba. "Naman jariri yafi kowanne daɗi, dashi da tayin da ba'a haifa ba. Inama Kulu ta sake haihuwar wani. Oh ni Gana ina zanga wani jinjirin yanzu da zan ci? Waye ke da ciki?"
"Gafaranku dai"
"Allah yai mana" ta amsa sallamar tana buɗe ƙofa ta fito waje. Washe baki ta yi ta ce "A'a wa nake gani kamar Hindatu"
"Ni ce rana tsaka Gana"
Gana ta ce "Lale maraba da Hindatu" Ta shimfiɗa assabari a gefen inuwa ta ce "Yada zango mana Hindatu, jiyan nan kika faɗo mini a rai nace muna maƙwabta amma ba zumunci walle kunya ta yi mana yawa"
Hindatu ta ce "Bari ke dai Gana, surfe da casa ne ya azo ni gaba. Yanzu ma ina zaune ina taɗin zuci na ji ƙamshi ta saman kanta shine na leƙo nima ayi dani, ko me gidan ya yi miki tsaraba" Gana ta zubawa Hindatu ido na wani lokaci kafin ta ce "kayya, Ƙamshin man ƙuli dana soya da albasa kika ji. Bari na kawo miki ruwa da abinci ko?" Miƙewa ta yi ta zuba mata wake da gero da ƙuli ta ɗauki man data soya jaririn Kulu dashi ta kelaya saman abincin ta ajjiye mata ta kawo ruwan tulo me sanyi a kofi ta ajjiye.
"Bisimillah Hindatu"
"Hadda wahala haka Gana?" Bakinta har dalalar da yawo yake tsabar kwaɗayi ta fara cin abincin. "Gana wai ni kowa ina Batty ana ta raɗe-raɗin yaro hura mata iskar balo a ciki shi ne kika ɗauke ta, wasu ma sun ce saboda uwarta bata raye kin kasa riƙe marainiyyar Allah" Gana ta fashe da kuka tana kunce bakin zani ta ce
"Na shiga uku kuma ni Gana, duk ɗawainiyyar da nake da Batty babu wanda ya yaba sai yanzu da jarrabawa ta same ni? Yadda naga Saleh yana turmushe Batty a zaure da murje ƴan ƙirjinta Allah Ya nuna mini Annabi. Ki faɗa mini da ban ɗauki matakin ɗauke Batty ba ai da tuni ya hura mata iska a ciki mun shiga uku. Da uwar uwar Batty dani nono ɗaya muka sha fa?" Hindatu ta ce "Sai haƙuri, mutane akwai su da gadon zancen wasu. Gana kin ji abincin nan inda ya yi daɗi? Ban taɓa jin man ƙuli da daɗi irin wannan ba, ko nama aka bani ba lalle ya yi daɗin wannan man ba" Gana ta yi murmushi ta fara tunanin yadda zata sawa Hindatu ƙanƙarar maita ta yi maganin shegen kwaɗayinta. Ta ce "Naman ma ina dashi, kuma idan kikai biyayya ma irin wannan kullum dashi za ki ci abinci na rantse" Hindatu ta waro ido waje ta ce
"Don Manzo?"
"Taso muje na ba ki nama da wani man" cewar Gana tana miƙewa tsaye ta yi cikin ɗakinta zumbur Hindatu ta miƙe tare da bin bayan Gana tana tafe tana riƙe zani da suɗe yatsun hannunta tana tunanin kakarta ta yanke saƙa daman ta biyu ta shigo gidan....
Littafin HIYAAM na kuÉ—i ne akan 1500. Muna tsarin discount akan mutanen farko da suka fara payment, daga book 1 2 3 za su biya 1k kacal. Wannan Discount É—in ana kammala free pages an rufe.
Mutanen farko da suka fara payment na HIYAAM za su biya 1k kacal ne.
Idan mukai limit da yawa za mu yi Hiyaam a WhatsApp ne, idan ba'a samu limit ba, za'ayi a Telegram da ArewaPen. Kana da ikon siyawa ƙawayenka, ko ka yi sponsoring wa jama'a domin Allah ko kuma a tallata maka business ɗinka.
Wannan tafiyar sabuwa ce, baku taɓa cin karo da ita ba.
0116886423
Union Bank
Na'ima Sulaiman S
Shaidar biya.
08164069385 ko
08082101373
A yi weekend lafiya.
*H I Y A A M*
Page 10: The Girl Wagered Away
Bright pens
Yota/001
Distance means so little when someone means so much. May Allah watch over you wherever you are. NAZEEFAH SABO NASHE.
Mun yi chapter 14 a ArewaPen.
Turus Gana ta tsaya a bakin ƙofar tana nazari sai kuma ta juya da murmushi ta ce "Hindatu ina ganin ki bari zan shigo na kawo miki, tunda har man ya yi miki daɗi" a zuciyarta kuma ta ce "Sai na ba ki ƙanƙarar maitar ki ji idan maitar daɗi gare ta shasha" ta yi furucin haɗe da yin gatsine tana me haɗawa da ƙwafa a lokaci guda.
*
MD a baƙin ƙofar room ɗin da aka ajjiye Ahlam ya tsaya ya harɗe hannayensa a ƙirji zaka rantse da Allah ba sashin dasu Ahlam da nurse ɗin yake kallo ba. Hawayen azaba ne kawai yake fita daga cikin idanun Ahlam yana bin kumatunta. Nurse dake riƙe da kayan Treatment ta ce "Sannu Golden voice" "Kin sanni ne?" Ahlam ta furta da ƙyar tana cije laɓɓanta da yarfar da hannunta sbd zafi
Nurse ta ce "E. Bake ce Ahlam Abdallah Kurmi ba, me yin dandalin nishaɗi program ɗin samari da ƴan mata a Bright Fm? Ina bibiyar shafinki na Facebook da Tiktok" duk da a cikin halin ciwo Ahlam take sai ta ji wani irin farinciki mara misaltuwa bata taɓa tunanin zata je wani waje a nuna an santa ba a dalilin aikinta na jarida, sai ta ji wani irin courage da confidence sun haɗe mata waje guda, ga wani hope data samu a furucin Nurse. Ta ɗan yi yaƙe ta ce "Thanks"
"Muke da godiya ai Golden voice" ta faÉ—a da zumuÉ—i na farinciki
"Idan an kammala treatment ɗin sai ku ƙarasa hirar taku ko?" Cewar Dr yana riƙe almaƙashi a hannunsa. Shiru Nurse ta yi ita kuma Golden voice ta kalli Dr a hankali cikin ƙasa da murya saboda har lokacin jini ke zuba a wuyanta ta ce "Sister ko za ki ara mini wayarki na yi vedio sai ki tura mini ta WhatsApp?" Cikin sauri Nurse ta ce "da gudu ma, Golden voice guda yadda nake mutuwar son programs ɗinki babu wanda bai san sunanki ba a bakina musamman ƴan gidanmu" wani yalwataccen murmushi Ahlam ta saki cike da jin daɗi da alfahari ta ce. "Ai har photo za mu yi, zan yi inviting naki zuwa shirin dandalin nishaɗi sister"