Sashe 25
Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
A cikin jerin estate dake Maitama sule Baffas Estate daban yake, gida ne da aka yanki gininsa na musamman tsarinsa komai ya bambanta da sauran, an yi masa ado da zane irin na gidan sarauta wanda bai san asalin BAFFA ba, zai ɗauka iyalinsa da shi kan shi jinin sarauta ne madadin sanin da aka yi masa na kasancewarsa Babban Malamin Addinin Musulunci dashi da zuri'arsa. Mabiyin Izala (Jama'atu Izalatil Bidi'a Wa lqamatis sunna) Ta dalilin SHEIKH HAFIZZ HAFIZZ BAFFA jama'ar da suka koma ɓangaren Izala suna da matuƙar yawan gaske al'amarin daya kawo ruɗu da ceceku ce tsakanin bambanta Addinai al'amarin daya yi ƙamari kenan yaja hankalin mabiya Shi'a (Shi'a Islam) a wani wa'azi da ya yi ya ya taɓo su, ya yi musu caccakar da taɓa har ƙasar Iran. Sheikh Hafizz Hafizz Baffa bai yi zaton girman abin ya kai har haka ba. Sai da aka wayi gari an kashe Sheikh Hafizz Hafizz Baffa, kisan da ba'a san su waye ba, tun daga lokacin har kawo yanzu, an kashe shi tare da babbar ƴarsa a kan hanyarsu ta zuwa Qatar. Sai jaririnta guda biyu ne suka tsira, wanda a ranar ne kuma ta haife su ba tare data san me ta haifa ba, aka yi mata yankan ragu aka ƙune Sheikh Hafizz Hafizz Baffa. Wannan jinin dake jikin Diyanah, jini ne da har abada ba zai taɓa fita daga zuƙatan BAFFAS FAMILY ba. Wannan jinin shine abu na farko da yake cin zuciyar mutumin da bai taɓa buɗe baki ya yi kukan rashin DIYANAH HAFIZZ HAFIZZ BAFFA ba.
Ba tsoran jinin yake ba, domin ya yi imani da Ubangijin Al'arshi kowanne rai zai ɗanɗani ɗacin dake cikin zare rai daga gangar jiki, ya yi imani da Allah da kuma ƙaddarar dake zane a rayuwar kowanne bawa. Baya tsoron dukkan abin da zai faru dashi muddin Ubangiji ne ya ƙaddaro masa.
"Wani rai ba zai sake salwanta ba ta dalilin Baffas Family, zai raini jinin DIYANAH HAFIZZ HAFIZZ BAFFA da soyayya da kulawa, zai ƙarar da rayuwarsa, shekarunsa wajan ingata jinin Diyanah Hafizz Hafizz" Ya ɗora da "Zai danne feelings da emotions ya manta cewa shi namiji ne, ya manta daɗin daya taɓa ji sau ɗaya a rayuwarsa" Shine abin da zuciya take faɗa masa a koyaushe. Daman zuri'ar daya samu da Diyanah Hafizz Hafizz Hafizz Baffa unexpected ne, ba zai iya tuna yadda ma komai ɗin ya kasance ba, shuɗewar shekara goma sha Bakwai kenan cif, a cikin shekarun 17 ɗin zai ware kwana ɗaya kawai, a wannan daren juma'ar ya kasance da Diyanah Baffa, kyakkywar yarinya fara tas kamar ita ta zaɓi yadda kyawunta zai kasance, ko a cikin daren ita ce wacce taja ra'ayinsa ita ce wacce komai nata ya yi tasiri a jikinsa ba'a zuciyarsa ba, daga wannan daren kuma sai komai ya lalace ya rasa kan shi a matsayin ɗa namiji ta dalilin hatsarin motar daya samu wanda yaja aka yi masa aiki a mararsa. Sai ya zama dashi da mace basu da bambanci sai na suna da suffa. Daga ranar ne kuma SAYYADI BAFFA ya fara kallon kowacce mace a suffar Garzali.
A hankali take sakkowa daga steps ɗin benen fuskarta ɗauke da yalwar murmushi tana sanye da atamfa ruwan ƙasa me zanen ɗawisu ta ɗora Jalbab a saman a atamfar wanda ya saukar mata har ƙasa hannunta ɗaya riƙe da counter tana tafe idanunta na kallon direction ɗaya tana sake faɗaɗa murmushinta wanda yafi maganarta yawa a koyaushe a haka har ta kammala sakkowa daga saman benen tana nufar kujera me cin mutum biyu ta zauna bakinta ɗauke da Bisimillah. "Barka da sakkowa Hajiya Umaimah" juyawa ta yi a nutse ta kalle shi, kamar ba zata ce komai ba sai ta jinjina kai
"Kana ta jira a downstairs Alhaji Sadi?" Ta ce a tausashe tana mai gyara zaman nata sosai. Ya jinjina kai yana murmushi ya ce
"Bai zama damuwa ba zaman ai Hajiya Umaimah nasan uzuri ne ya zaunar dake a can saman, ni abin kari ma nake jira a nan" É—an É—aga kai ta yi sai taga gabaÉ—aya 11:12 na safiya ta sake yin murmushi can ya ce "Gidan shiru yau É—in" A nutse ta sake cewa
"Nadiyah Baffa ce babu lafiya"
Alhaji Sadi ya buɗe idanunsa cike da damuwa da tsoron jin abin da ya samu Nadiyah ɗin, dukkan wata damuwar da zata sake bawa Baffa damar shiga ƙunci baya son ta, yana jin kai tsaya damuwar Sayyadi Baffa ne na sauka a zuciyarsa tana haifar masa da rashin kuzari da walwala. Ya dubi Hajiya Umaimah a nutse ya ce "Nadiyah fa?"
"Nadiyah Sayyadi Baffa" ta bashi amsa. "Ikon Allah, mene ya same ta har haka? Ban taɓa jin ta yi lalura har ta kwanta ba, dama dai Diyanah ce wannan tana da laulayi" baya Hajiya Umaimah ta yi tana ɗauke kanta zuwa gefe kamar bata ji me yake cewa ba, a hankali ta ce "Ya za'ayi da lamarin Ubangiji Alhaji Sadi? Ciwo ai waraka ce" shima ɗin jinjina kai kawai ya yi ya ce
"Mun je nema wa Liman aure kamar yadda ya buƙata, to my surprise basu bamu matsala ba iyayen yarinyar akwai karamci sosai da alama"
"Allah Ya sa ba ƴar ƙananun mutane Liman ya ɗakko mana ba" yadda ta yi maganar tana neman wajan zama kai tsaye ya bawa Alhaji Sadi mamaki ya juya ya kalle ta na wani lokaci sai bai ce komai ba, ya mayar da idanunsa kan Umaimah ya ce "Sun amshi kuɗin, an kuma saka rana nan da watanni biyar masu zuwa"
"Allah Ya nuna mana, ya sa abokiyar zama ce" Hajiya Umaimah ta furta a sanyaye tana lumshe idanunta, bawai haka tasu ba, ba kuma hakan ta buƙata ba, yaronta namiji guda ɗaya tal a duniya ta yi masa buri da kwaɗayin auren ƴa gidan manyan mutane, wacce ubanta yake wani a garin nan a Jihar ko a ƙasar bakiɗaya. Sai gashi ya ɗakko wacce tsabar takaici bata iya tsayawa ta tambayi wacece ita ba, balle ta san ƴar wacece. "Ina so a yi mini iso wajan Baffa"
"Baffa...." Umaimah ta maimaita
"Sayyadi Baffa kake nufi?"
Cikin sauri matashiyar yarinyar dake zaune taja idanunta ta lumshe su, ji ta yi duk wani raɗaɗin zuciyarta ya kau, nauyin da ƙirjinta yake mata ta ragu wani sanyi da nutsuwa na saukar mata a jikinta ta dalilin kiran sunan Sayyadi Baffa da aka yi. Ta ɗauke kai gefe guda tana murmushi duk sun lura da hakan suka share. Alhaji Sadi ya ce "Ina son ganawa dashi ne" da mamaki Umaimah ta dube shi kafin ta ce "Babu shi aka je neman auren na Liman daman Alhaji Sadi?"
"E, daga ni sai Sheikh Nurain da Malami da Alhaji Huzaifa Abdallah muka je tafiyar ai"
"Na ɗauka girma da ƙimar Baffa suka duba wajan amincewa da batun auren Liman? Ashe dai kawai.....," cikin sauri ya dakatar da Hajiya Umaimah da faɗin "Mu bamu wadatar mu nema wa Liman aure ba sai dole akwai Baffa a ciki tafiyar? Ko mu ƙima da mutuncin ne bamu dashi? Sayyadi Baffa ɗa ne kawai a wajan Sheikh Hafiz Hafiz Baffa, mu kuma ƙannnen Sheikh Hafizz ne idan kika ɗauke Alhaji Huzaifa da yake yayanki, kenan duk wata martaba da kike tunanin Sayyadi Baffa na da ita sai data fara shafar mu kafin ta ruski inda Sayyadi Baffa yake"
Hajiya Umaimah kallon shi kawai take yi ganin yadda ya juya mata manufarta a fili.
"Alhaji Sadi ko dai kana son faÉ—a..," ya katse da faÉ—in
"Babu abin da zan faÉ—a miki Hajiya Umaimah wanda ya shige ce miki an bawa É—anki Liman auren yarinyar da yake so"
Ta jinjina kai da girmamawa ta ce
"Na gode"
Alhaji Sadi ya miƙe tsaye yana ƙoƙarin barin haɗaɗɗan parlourn ƙasan da ya gama gajiya da haɗuwa wanda shine main parlour na kowa da kowa. "Barka da Safiya uncle" kamilalliyar muryarsa ta riga shi zuwa
"Yawwa Mu'allim kana gida ashe?" Hannunsa ɗaya cikin aljihun wandon shaddar jikinsa sai ƙamshi yake da nutsuwa da kulawa ya ce
"Ina hutawa ne"
"Ga Liman nan ya tura maka Buzu" Uncle ya faÉ—a da sigar zolaya a fuskarsa
Mu'allim yaja idanunsa ya lumshe bayan ya zauna a kujera ya rungume hannunsa a ƙirji bai fahimci maganar Alhaji Sadi ba a gajarce ya ce "Buzu kuma Uncle?" Uncle Sadi ya ce "E, kuɗin aure muka kai masa yau ɗin nan, nan da wata Biyar za'ayi auren Liman fa" Mu'allim ya jinjina kai yana ciro wayarsa a cikin Aljihu a tausashe ya furta "Ahky yana da budurwa daman har ake maganar Nikkah?" Uncle Sadi ya buɗe hannayensa wajan faɗin "Yanzu da ta yi wari ba gashi kowa ya ji ba? Sai fatan Allah Ya sa Albarka"
"Sayyadi Baffa yana sashensa ne?"
"Ya je Da'awa"
Mu'allim ya bashi amsa.
"Wanne gari? Wacce ƙasar?"
Ba tsoran jinin yake ba, domin ya yi imani da Ubangijin Al'arshi kowanne rai zai ɗanɗani ɗacin dake cikin zare rai daga gangar jiki, ya yi imani da Allah da kuma ƙaddarar dake zane a rayuwar kowanne bawa. Baya tsoron dukkan abin da zai faru dashi muddin Ubangiji ne ya ƙaddaro masa.
"Wani rai ba zai sake salwanta ba ta dalilin Baffas Family, zai raini jinin DIYANAH HAFIZZ HAFIZZ BAFFA da soyayya da kulawa, zai ƙarar da rayuwarsa, shekarunsa wajan ingata jinin Diyanah Hafizz Hafizz" Ya ɗora da "Zai danne feelings da emotions ya manta cewa shi namiji ne, ya manta daɗin daya taɓa ji sau ɗaya a rayuwarsa" Shine abin da zuciya take faɗa masa a koyaushe. Daman zuri'ar daya samu da Diyanah Hafizz Hafizz Hafizz Baffa unexpected ne, ba zai iya tuna yadda ma komai ɗin ya kasance ba, shuɗewar shekara goma sha Bakwai kenan cif, a cikin shekarun 17 ɗin zai ware kwana ɗaya kawai, a wannan daren juma'ar ya kasance da Diyanah Baffa, kyakkywar yarinya fara tas kamar ita ta zaɓi yadda kyawunta zai kasance, ko a cikin daren ita ce wacce taja ra'ayinsa ita ce wacce komai nata ya yi tasiri a jikinsa ba'a zuciyarsa ba, daga wannan daren kuma sai komai ya lalace ya rasa kan shi a matsayin ɗa namiji ta dalilin hatsarin motar daya samu wanda yaja aka yi masa aiki a mararsa. Sai ya zama dashi da mace basu da bambanci sai na suna da suffa. Daga ranar ne kuma SAYYADI BAFFA ya fara kallon kowacce mace a suffar Garzali.
A hankali take sakkowa daga steps ɗin benen fuskarta ɗauke da yalwar murmushi tana sanye da atamfa ruwan ƙasa me zanen ɗawisu ta ɗora Jalbab a saman a atamfar wanda ya saukar mata har ƙasa hannunta ɗaya riƙe da counter tana tafe idanunta na kallon direction ɗaya tana sake faɗaɗa murmushinta wanda yafi maganarta yawa a koyaushe a haka har ta kammala sakkowa daga saman benen tana nufar kujera me cin mutum biyu ta zauna bakinta ɗauke da Bisimillah. "Barka da sakkowa Hajiya Umaimah" juyawa ta yi a nutse ta kalle shi, kamar ba zata ce komai ba sai ta jinjina kai
"Kana ta jira a downstairs Alhaji Sadi?" Ta ce a tausashe tana mai gyara zaman nata sosai. Ya jinjina kai yana murmushi ya ce
"Bai zama damuwa ba zaman ai Hajiya Umaimah nasan uzuri ne ya zaunar dake a can saman, ni abin kari ma nake jira a nan" É—an É—aga kai ta yi sai taga gabaÉ—aya 11:12 na safiya ta sake yin murmushi can ya ce "Gidan shiru yau É—in" A nutse ta sake cewa
"Nadiyah Baffa ce babu lafiya"
Alhaji Sadi ya buɗe idanunsa cike da damuwa da tsoron jin abin da ya samu Nadiyah ɗin, dukkan wata damuwar da zata sake bawa Baffa damar shiga ƙunci baya son ta, yana jin kai tsaya damuwar Sayyadi Baffa ne na sauka a zuciyarsa tana haifar masa da rashin kuzari da walwala. Ya dubi Hajiya Umaimah a nutse ya ce "Nadiyah fa?"
"Nadiyah Sayyadi Baffa" ta bashi amsa. "Ikon Allah, mene ya same ta har haka? Ban taɓa jin ta yi lalura har ta kwanta ba, dama dai Diyanah ce wannan tana da laulayi" baya Hajiya Umaimah ta yi tana ɗauke kanta zuwa gefe kamar bata ji me yake cewa ba, a hankali ta ce "Ya za'ayi da lamarin Ubangiji Alhaji Sadi? Ciwo ai waraka ce" shima ɗin jinjina kai kawai ya yi ya ce
"Mun je nema wa Liman aure kamar yadda ya buƙata, to my surprise basu bamu matsala ba iyayen yarinyar akwai karamci sosai da alama"
"Allah Ya sa ba ƴar ƙananun mutane Liman ya ɗakko mana ba" yadda ta yi maganar tana neman wajan zama kai tsaye ya bawa Alhaji Sadi mamaki ya juya ya kalle ta na wani lokaci sai bai ce komai ba, ya mayar da idanunsa kan Umaimah ya ce "Sun amshi kuɗin, an kuma saka rana nan da watanni biyar masu zuwa"
"Allah Ya nuna mana, ya sa abokiyar zama ce" Hajiya Umaimah ta furta a sanyaye tana lumshe idanunta, bawai haka tasu ba, ba kuma hakan ta buƙata ba, yaronta namiji guda ɗaya tal a duniya ta yi masa buri da kwaɗayin auren ƴa gidan manyan mutane, wacce ubanta yake wani a garin nan a Jihar ko a ƙasar bakiɗaya. Sai gashi ya ɗakko wacce tsabar takaici bata iya tsayawa ta tambayi wacece ita ba, balle ta san ƴar wacece. "Ina so a yi mini iso wajan Baffa"
"Baffa...." Umaimah ta maimaita
"Sayyadi Baffa kake nufi?"
Cikin sauri matashiyar yarinyar dake zaune taja idanunta ta lumshe su, ji ta yi duk wani raɗaɗin zuciyarta ya kau, nauyin da ƙirjinta yake mata ta ragu wani sanyi da nutsuwa na saukar mata a jikinta ta dalilin kiran sunan Sayyadi Baffa da aka yi. Ta ɗauke kai gefe guda tana murmushi duk sun lura da hakan suka share. Alhaji Sadi ya ce "Ina son ganawa dashi ne" da mamaki Umaimah ta dube shi kafin ta ce "Babu shi aka je neman auren na Liman daman Alhaji Sadi?"
"E, daga ni sai Sheikh Nurain da Malami da Alhaji Huzaifa Abdallah muka je tafiyar ai"
"Na ɗauka girma da ƙimar Baffa suka duba wajan amincewa da batun auren Liman? Ashe dai kawai.....," cikin sauri ya dakatar da Hajiya Umaimah da faɗin "Mu bamu wadatar mu nema wa Liman aure ba sai dole akwai Baffa a ciki tafiyar? Ko mu ƙima da mutuncin ne bamu dashi? Sayyadi Baffa ɗa ne kawai a wajan Sheikh Hafiz Hafiz Baffa, mu kuma ƙannnen Sheikh Hafizz ne idan kika ɗauke Alhaji Huzaifa da yake yayanki, kenan duk wata martaba da kike tunanin Sayyadi Baffa na da ita sai data fara shafar mu kafin ta ruski inda Sayyadi Baffa yake"
Hajiya Umaimah kallon shi kawai take yi ganin yadda ya juya mata manufarta a fili.
"Alhaji Sadi ko dai kana son faÉ—a..," ya katse da faÉ—in
"Babu abin da zan faÉ—a miki Hajiya Umaimah wanda ya shige ce miki an bawa É—anki Liman auren yarinyar da yake so"
Ta jinjina kai da girmamawa ta ce
"Na gode"
Alhaji Sadi ya miƙe tsaye yana ƙoƙarin barin haɗaɗɗan parlourn ƙasan da ya gama gajiya da haɗuwa wanda shine main parlour na kowa da kowa. "Barka da Safiya uncle" kamilalliyar muryarsa ta riga shi zuwa
"Yawwa Mu'allim kana gida ashe?" Hannunsa ɗaya cikin aljihun wandon shaddar jikinsa sai ƙamshi yake da nutsuwa da kulawa ya ce
"Ina hutawa ne"
"Ga Liman nan ya tura maka Buzu" Uncle ya faÉ—a da sigar zolaya a fuskarsa
Mu'allim yaja idanunsa ya lumshe bayan ya zauna a kujera ya rungume hannunsa a ƙirji bai fahimci maganar Alhaji Sadi ba a gajarce ya ce "Buzu kuma Uncle?" Uncle Sadi ya ce "E, kuɗin aure muka kai masa yau ɗin nan, nan da wata Biyar za'ayi auren Liman fa" Mu'allim ya jinjina kai yana ciro wayarsa a cikin Aljihu a tausashe ya furta "Ahky yana da budurwa daman har ake maganar Nikkah?" Uncle Sadi ya buɗe hannayensa wajan faɗin "Yanzu da ta yi wari ba gashi kowa ya ji ba? Sai fatan Allah Ya sa Albarka"
"Sayyadi Baffa yana sashensa ne?"
"Ya je Da'awa"
Mu'allim ya bashi amsa.
"Wanne gari? Wacce ƙasar?"