Sashe 21
Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Innti ta ce “Education is a gift; muddin ɗalibi yana da fahimta, they can achieve anything. Kuma ya danganta da koyarwar Malami"
"Innti ni dai kece Malamata, kowa yana jin daÉ—in koyarwarki kafin ki daina teaching"
Abinci suka fara ci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da soyayyar juna, a ƙa'ida idan suna cin abinci babu wanda yake yin magana har su kammala. Yanzu ma haka ne, Babban yaya ne ya fara kammalawa ya ɗauki ruwa ya sha yana kammala sha Ifti ta ɗauka ta sha, sauran ma duk suka sha, bayan sun wanke hannunsu tas Ifti ta kwashe kayan ta ajjiye wajan da suke ajjiye marasa kyau. Akan shimfiɗar suke zaune ta fara yi musu tatsuniya kamar yadda ta saba me cike da hikayoyi da alamar, bayan ta kammala zata tambayi kowa abin da ya koya na darasi daga tatsuniyar. A hankali ta ɗaga kai ta kalle su, zuciyarta cike da fargaba da kuma soyayyar yaranta, an ce dukkan yaran da suka yi nasara a rayuwa, akwai jajirtattun iyaye a bayansu, ita a rayuwar yaranta ita kaɗai ce tsaye a bayansu, ita ce ta ɗauki responsibilities na uwa, kuma ta haɗa tana uba, ta sake ɗaukan ɗawainiyyar dangin uba, bata gajiya da dukkan ɗawainiyyar dake kanta ta sake haɗawa dana dangin uwa. Ta dubi hannunta babu komai sai farcen sosa, bata da komai sai dattin alijuhu. A ƙarƙashin tsoron daya cukukuye zuciyarta harɗa bauɗaɗɗan halin Ana, yarinya ce mafi soyowa a ranta, yarinyar da take matuƙar so fiye da sauran.
A ƙarƙashin wannan son, ta koyi yadda zata sarrafa shi ba tare da mahaɗin haihuwarta ta gane ya haddasa mata damuwa ba, a madadin ta nuna soyayyar Ana a fili sai ta danne tsaf. Ita ce ma wace tafi Addabawa da faɗa a ciki. Gyaran murya ta yi gabaɗaya suka kalle ta, kaifafan idanunsu masu huda zuciyarta da ƙauna ne ke kallon ta. "Ina sake tuna muku ku ba kowa bane a duniya, ba kowa bane a dangin mahaifinku, ku iya talaucinku, ku ɗauke ranku tsam daga kan abun wani, ku yi rayuwa da abin da kuke dashi, watarana sai labarin... Ko ba yau ba, ko ba yanzu ba, za ku ji daɗi za ku zama kune masu ƙarfafa wasu da taimakon su, kun ji me ma ce ko?"
Murmushi Jaheed ya yi cikin ladabi ya ce "Idan hadda ce wannan da tuni mun sauke mun sake ruɓanya saukar sau shurun masaƙi uwar arziƙi. Kalamanki kai tsaye umarni ne ba kawai wa'azi ba. Mu masu biyayya ne a gare ki, Allah Ya bamu ikon kulawa dake" nauyayyiyar ajjiyar zuciya Innti ta sauke, tana jin dole ta sake zage damtse tare da humɓasawa akan sana'ar da take saboda yaranta musamman matan. Yanayin fuskar Jaheed ya sauya zuwa damuwa kafin ya ce "Bana son arziƙin da zan yi wanda Daada zai amfana dashi..,"
Marin da Innti ta ɗauke Jaheed dashi ne ya hana shi ƙarasa faɗar abin da yake ƙwarzabar zuciyarsa, ya yi saurin dafe kuncinsa da hannun dama idanun ya yi jajur duk da duhun dare ya yi ba'a ganin fuskarsa balle cikin idanunsa. Raɗaɗin da ƙonar marin da Jaheed ya ji ya sauka a zuciyar abokin haihuwarsa Jadid, shima runtse idanun nasa ya yi a hankali kuma ya miƙa hannunsa ya ɗora akan na Jaheed
Alamar rarrashi.
"Dukkan arziƙin da ɗayanku zai samu wanda mahaifinku ba zai amfana dashi ba nima ya zama haramiyata, bana buƙata bana muku addu'ar ku samu, ƙwara mu zauna cikin babu ko ƙasa za mu ƙwaba mu dinga ci saboda yunwa na aminci da hakan" da ƙyar take maganar tana jin raɗaɗin marin da ta yi wa Jaheed yana sauka a ƙasan zuciyarta yana cinta. Ta yi saurin yin ƙasa da kanta tare da goge hawayen da yake zuba daga cikin idanunta. Ta ɗora da
"Hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar, ko baku ƙaunaci Daada a Matsayin uba ba, ba za ku hana duniya faɗar cewa ku ƴaƴansa bane. Ko muguwar kalma ɗaya daga cikinku ya yi masa, ko ina raye ko bana yare ko akan idanuna ko a bayan idanuna wallahi tallahi ban yafe ba, biyayya a gare shi umarnina ne, shi mijina ne, garkuwata kuma uban ƴaƴana, duk yadda zai kai da addaba mini ko aibata ku, haka zan cigaba da yi masa addu'a, haka kuma kullum cikin addu'oinku umarni ne akan ku yi masa addu'a" a karo na farko Jadid ya kalle ta.
Ya ce "Innti rawar zata sauya zani ne?" Muryarsa shima a raunace take sosai
"Kin san kallon da jama'a suke yi mana akan Daada? Kin san raɗaɗin da muke ji a cikin zuciyarmu? Kin san yadda muka sha bambam da sauran yara a duniyar nan?" Ya runtse idanunsa yana jin yadda komai baya yi masa daɗi, yana ƙoƙarin fidda rai da rayuwa me tsayi yana da yaƙinin ciwon nan ba zai bar shi ba. A fusge ya ce "Innti mutane basu da adalci, sun kasa yi mana adalci cewa, bamu da laifi ko saka hannu a cikin al'ummaran Daada, ya za mu yi ne? Ya za mu yi da ranmu, a wajanki kawai muke jin iska me daɗi, a wajanki muke samun inuwar da za mu raɓa mu ji sa'ida. Na karaya na fara karaya ina tsoron in ji cewa kamar ba mu yi sa'ar uba ba....,"
"Jadid!"
Ta dakatar dashi da ƙarfi ta hanyar kiran sunansa, ya yi ƙasa da kan shi a hankali yace. "Ki yafe mini Innti kar ki yi fushi damu, ke kaɗai muke da ƙwarin gwiwar buɗe ba ki mu faɗawa halin da zuciyarmu take ciki, ina tsoron kar matsalolin Daada ya yi wa'adin ɗaya daga cikin zuri'arki, dauriya kike, na sani na san da wannan Innti shiru bashi ne ba" Ta zubawa Jadid idanu, sai yanzu ta lura da sauyawar da ya yi, wanda ya ci tun a jiya ta gane saboda bata da wasa wajan fahimtar yanayin yaran nata. Ta ja numfashi ta sauke ta kasa cewa komai sai ƙirjinta da ya yi mata nauyi, wani abu ya tsaya mata.
Wayar Jaheed ce ta fara ƙara alamar shigowar kira, number wanda ya gani ce ta saka shi yin murmushi, murmushin daya saka Jadid sauke ajjiyar zuciya me nauyi ko babu komai ganin abokiyar haihuwarsa cikin farinciki ya sauƙaƙa masa ciwon da yake ji a jikinsa. "Mutumin rigimammiya ne"
"Yaa Sam?" Inji Iftihal tana dariya.
"Haysaam, kin canka masoyiya"
Jaheed ya bata amsa, yana miƙa mata wayar ya ce "Jeki kai mata, na san dai ita yake nema" Iftihal ta amshi wayar da hannu biyu cike da ladabi ta juya zuwa ɗakin nasu. "Wannan wayar da suke yi da Haysaam da Ana babu damuwa a cikinta dai ko? Kun san irin maganganun da suke yi a tsakaninsu?"
Jadid ya ce "Babu in sha Allah, hirar dai ba zata shige ta masoya ba idan ta yi ƙamari"
"Soyayya? Sonta yake yi?"
Yadda Jaheed ya yi tambayar ya bawa Jadid dariya ya ce "Kusanci idan ya yi yawa tsakanin mace da namiji ai soyayya ce kawai, wata rigimar da Shalelen Innti Babban yaya da Innti sai shi Haysaam ɗin kawai ne suke tanƙwara mana ita, kafirin taurin kai kamar matar kuturu da iyayin tsiya kamar jikar ƙaruna. Ga yauƙi kamar kuɓewa" Innti ta girgiza kai tana murmushi ta ce "Allah Ya shirya ka Jadid ya shirya mini zuri'a baki ɗaya, ka je ka sha maganinka ka kwanta haka nan" Kamar zai ce mata maganin ya ƙare sai kawai ya yi shiru ya miƙe tare da cewa "Mu kwana lafiya Sahibata" ta jinjina masa kai. Jaheed miƙe ƙafafuwa ya yi yana bawa Innti labarin shago, gabaɗaya ya mance da abin da ya faru na sharrin da aka yi wa Shalelen Innti.
Babban yaya daman kamar baya wajan, wayarsa kawai yake dannawa ba tare daya san mema yake yi dannawa É—in ba, tunaninsa kamar ba nasa ba, hatta shi É—in jinsa yake kamar ba shi ba. Sai ya dinga gani ko ji a ran shi cewa; yana da bambanci da Æ´an'uwansa. Bambancin da yake sake nisanta shi da al'umma, baya samun nutsuwa muddin zai jisa a cikin mutane. Wannan rayuwar jejin da yake tsintar kan shi a ciki idan ya yi bacci tafi masa daÉ—i.
Iftifal da fara'a ta shiga ɗakin tana saukar da ganinta a shimfiɗarsu, domin ta ɗauka mahaɗinta ta jima da yin bacci.. turus ta yi ganin Ana zaune a ƙasa a inda ta yi sallar issha ko tashi ba ta yi ba, ta zubawa waje guda idanu. Har Ifti ta ƙarasu inda take ta tsuguna bata sani ba, alamar ta yi nisa cikin tunaninta. "Ana!" Ta kira sunanta da ƙarfi.
Tana jijjigata kafaÉ—unta biyun.
"Tunanin me kike yi mahaÉ—ita?"
A hankali taja manyan idanunta ta lumshe su bata jima ba ta ware su a fuskar Ifti ba tare da ta ce komai ba. Ajjiyar zuciya Ifti ta sauke a sanyaye ta ce "Ba damuwa Daada kika sakawa ranki ba ina fata rabin rai?"
"Daada....?
Yadda ta yi furucin da yadda ta ambaci sunan Daada zaka ɗauka bata taɓa jin sunan ba sai a lokacin. Furucin da Ana ta yi ya daskarar da jinin jikin Ifti da wani irin sabon tashin hankali ta ce "Kin san me kika ce? Kin san abin da kalmominki ke nufi?"
Ana ta girgiza kai ta ce "A'a"
"Waye Daada? Da gaske ban waye shi ba?" Iftihal ta ce
"Ina tunanin Sunanki Ayshatul-Haleeym Ana Daada, wannan sunan da yake maƙale da sunanki kamar rai da ajali, wannan sunan da idan babu shi ba ki gama zama cikakkiyar ƴar sunna ba, wannan sunan da zai ta bibiyarki har yaranki da za su amsa sunan jikokin Daada.. wannan Daada mahaifinki"
Ana ta bubbuɗe idanunta kafin ta juya ƙwayar idanun ta ce "Oh! Idan na fahimta wannan mutumin mai dukan matarsa, wannan dai mutumin me shigo mana gida tsirara cikin talatainin dare, hakazalika wannan mutumin me bin manta banza wanda yake da karuwa me suna Tani, wannan dai mutumin me yin caca shi kenan nufi? Shine Daadan da kike magana akai?"
"Ana!"
"Iftihal....
Ta kira sunanta itama cikin sanyin muryarta mara son hayaniya da rashin É—aukan raini.
"Innti ni dai kece Malamata, kowa yana jin daÉ—in koyarwarki kafin ki daina teaching"
Abinci suka fara ci cikin nutsuwa da kwanciyar hankali da soyayyar juna, a ƙa'ida idan suna cin abinci babu wanda yake yin magana har su kammala. Yanzu ma haka ne, Babban yaya ne ya fara kammalawa ya ɗauki ruwa ya sha yana kammala sha Ifti ta ɗauka ta sha, sauran ma duk suka sha, bayan sun wanke hannunsu tas Ifti ta kwashe kayan ta ajjiye wajan da suke ajjiye marasa kyau. Akan shimfiɗar suke zaune ta fara yi musu tatsuniya kamar yadda ta saba me cike da hikayoyi da alamar, bayan ta kammala zata tambayi kowa abin da ya koya na darasi daga tatsuniyar. A hankali ta ɗaga kai ta kalle su, zuciyarta cike da fargaba da kuma soyayyar yaranta, an ce dukkan yaran da suka yi nasara a rayuwa, akwai jajirtattun iyaye a bayansu, ita a rayuwar yaranta ita kaɗai ce tsaye a bayansu, ita ce ta ɗauki responsibilities na uwa, kuma ta haɗa tana uba, ta sake ɗaukan ɗawainiyyar dangin uba, bata gajiya da dukkan ɗawainiyyar dake kanta ta sake haɗawa dana dangin uwa. Ta dubi hannunta babu komai sai farcen sosa, bata da komai sai dattin alijuhu. A ƙarƙashin tsoron daya cukukuye zuciyarta harɗa bauɗaɗɗan halin Ana, yarinya ce mafi soyowa a ranta, yarinyar da take matuƙar so fiye da sauran.
A ƙarƙashin wannan son, ta koyi yadda zata sarrafa shi ba tare da mahaɗin haihuwarta ta gane ya haddasa mata damuwa ba, a madadin ta nuna soyayyar Ana a fili sai ta danne tsaf. Ita ce ma wace tafi Addabawa da faɗa a ciki. Gyaran murya ta yi gabaɗaya suka kalle ta, kaifafan idanunsu masu huda zuciyarta da ƙauna ne ke kallon ta. "Ina sake tuna muku ku ba kowa bane a duniya, ba kowa bane a dangin mahaifinku, ku iya talaucinku, ku ɗauke ranku tsam daga kan abun wani, ku yi rayuwa da abin da kuke dashi, watarana sai labarin... Ko ba yau ba, ko ba yanzu ba, za ku ji daɗi za ku zama kune masu ƙarfafa wasu da taimakon su, kun ji me ma ce ko?"
Murmushi Jaheed ya yi cikin ladabi ya ce "Idan hadda ce wannan da tuni mun sauke mun sake ruɓanya saukar sau shurun masaƙi uwar arziƙi. Kalamanki kai tsaye umarni ne ba kawai wa'azi ba. Mu masu biyayya ne a gare ki, Allah Ya bamu ikon kulawa dake" nauyayyiyar ajjiyar zuciya Innti ta sauke, tana jin dole ta sake zage damtse tare da humɓasawa akan sana'ar da take saboda yaranta musamman matan. Yanayin fuskar Jaheed ya sauya zuwa damuwa kafin ya ce "Bana son arziƙin da zan yi wanda Daada zai amfana dashi..,"
Marin da Innti ta ɗauke Jaheed dashi ne ya hana shi ƙarasa faɗar abin da yake ƙwarzabar zuciyarsa, ya yi saurin dafe kuncinsa da hannun dama idanun ya yi jajur duk da duhun dare ya yi ba'a ganin fuskarsa balle cikin idanunsa. Raɗaɗin da ƙonar marin da Jaheed ya ji ya sauka a zuciyar abokin haihuwarsa Jadid, shima runtse idanun nasa ya yi a hankali kuma ya miƙa hannunsa ya ɗora akan na Jaheed
Alamar rarrashi.
"Dukkan arziƙin da ɗayanku zai samu wanda mahaifinku ba zai amfana dashi ba nima ya zama haramiyata, bana buƙata bana muku addu'ar ku samu, ƙwara mu zauna cikin babu ko ƙasa za mu ƙwaba mu dinga ci saboda yunwa na aminci da hakan" da ƙyar take maganar tana jin raɗaɗin marin da ta yi wa Jaheed yana sauka a ƙasan zuciyarta yana cinta. Ta yi saurin yin ƙasa da kanta tare da goge hawayen da yake zuba daga cikin idanunta. Ta ɗora da
"Hannunka baya taɓa ruɓewa ka yanke ka yar, ko baku ƙaunaci Daada a Matsayin uba ba, ba za ku hana duniya faɗar cewa ku ƴaƴansa bane. Ko muguwar kalma ɗaya daga cikinku ya yi masa, ko ina raye ko bana yare ko akan idanuna ko a bayan idanuna wallahi tallahi ban yafe ba, biyayya a gare shi umarnina ne, shi mijina ne, garkuwata kuma uban ƴaƴana, duk yadda zai kai da addaba mini ko aibata ku, haka zan cigaba da yi masa addu'a, haka kuma kullum cikin addu'oinku umarni ne akan ku yi masa addu'a" a karo na farko Jadid ya kalle ta.
Ya ce "Innti rawar zata sauya zani ne?" Muryarsa shima a raunace take sosai
"Kin san kallon da jama'a suke yi mana akan Daada? Kin san raɗaɗin da muke ji a cikin zuciyarmu? Kin san yadda muka sha bambam da sauran yara a duniyar nan?" Ya runtse idanunsa yana jin yadda komai baya yi masa daɗi, yana ƙoƙarin fidda rai da rayuwa me tsayi yana da yaƙinin ciwon nan ba zai bar shi ba. A fusge ya ce "Innti mutane basu da adalci, sun kasa yi mana adalci cewa, bamu da laifi ko saka hannu a cikin al'ummaran Daada, ya za mu yi ne? Ya za mu yi da ranmu, a wajanki kawai muke jin iska me daɗi, a wajanki muke samun inuwar da za mu raɓa mu ji sa'ida. Na karaya na fara karaya ina tsoron in ji cewa kamar ba mu yi sa'ar uba ba....,"
"Jadid!"
Ta dakatar dashi da ƙarfi ta hanyar kiran sunansa, ya yi ƙasa da kan shi a hankali yace. "Ki yafe mini Innti kar ki yi fushi damu, ke kaɗai muke da ƙwarin gwiwar buɗe ba ki mu faɗawa halin da zuciyarmu take ciki, ina tsoron kar matsalolin Daada ya yi wa'adin ɗaya daga cikin zuri'arki, dauriya kike, na sani na san da wannan Innti shiru bashi ne ba" Ta zubawa Jadid idanu, sai yanzu ta lura da sauyawar da ya yi, wanda ya ci tun a jiya ta gane saboda bata da wasa wajan fahimtar yanayin yaran nata. Ta ja numfashi ta sauke ta kasa cewa komai sai ƙirjinta da ya yi mata nauyi, wani abu ya tsaya mata.
Wayar Jaheed ce ta fara ƙara alamar shigowar kira, number wanda ya gani ce ta saka shi yin murmushi, murmushin daya saka Jadid sauke ajjiyar zuciya me nauyi ko babu komai ganin abokiyar haihuwarsa cikin farinciki ya sauƙaƙa masa ciwon da yake ji a jikinsa. "Mutumin rigimammiya ne"
"Yaa Sam?" Inji Iftihal tana dariya.
"Haysaam, kin canka masoyiya"
Jaheed ya bata amsa, yana miƙa mata wayar ya ce "Jeki kai mata, na san dai ita yake nema" Iftihal ta amshi wayar da hannu biyu cike da ladabi ta juya zuwa ɗakin nasu. "Wannan wayar da suke yi da Haysaam da Ana babu damuwa a cikinta dai ko? Kun san irin maganganun da suke yi a tsakaninsu?"
Jadid ya ce "Babu in sha Allah, hirar dai ba zata shige ta masoya ba idan ta yi ƙamari"
"Soyayya? Sonta yake yi?"
Yadda Jaheed ya yi tambayar ya bawa Jadid dariya ya ce "Kusanci idan ya yi yawa tsakanin mace da namiji ai soyayya ce kawai, wata rigimar da Shalelen Innti Babban yaya da Innti sai shi Haysaam ɗin kawai ne suke tanƙwara mana ita, kafirin taurin kai kamar matar kuturu da iyayin tsiya kamar jikar ƙaruna. Ga yauƙi kamar kuɓewa" Innti ta girgiza kai tana murmushi ta ce "Allah Ya shirya ka Jadid ya shirya mini zuri'a baki ɗaya, ka je ka sha maganinka ka kwanta haka nan" Kamar zai ce mata maganin ya ƙare sai kawai ya yi shiru ya miƙe tare da cewa "Mu kwana lafiya Sahibata" ta jinjina masa kai. Jaheed miƙe ƙafafuwa ya yi yana bawa Innti labarin shago, gabaɗaya ya mance da abin da ya faru na sharrin da aka yi wa Shalelen Innti.
Babban yaya daman kamar baya wajan, wayarsa kawai yake dannawa ba tare daya san mema yake yi dannawa É—in ba, tunaninsa kamar ba nasa ba, hatta shi É—in jinsa yake kamar ba shi ba. Sai ya dinga gani ko ji a ran shi cewa; yana da bambanci da Æ´an'uwansa. Bambancin da yake sake nisanta shi da al'umma, baya samun nutsuwa muddin zai jisa a cikin mutane. Wannan rayuwar jejin da yake tsintar kan shi a ciki idan ya yi bacci tafi masa daÉ—i.
Iftifal da fara'a ta shiga ɗakin tana saukar da ganinta a shimfiɗarsu, domin ta ɗauka mahaɗinta ta jima da yin bacci.. turus ta yi ganin Ana zaune a ƙasa a inda ta yi sallar issha ko tashi ba ta yi ba, ta zubawa waje guda idanu. Har Ifti ta ƙarasu inda take ta tsuguna bata sani ba, alamar ta yi nisa cikin tunaninta. "Ana!" Ta kira sunanta da ƙarfi.
Tana jijjigata kafaÉ—unta biyun.
"Tunanin me kike yi mahaÉ—ita?"
A hankali taja manyan idanunta ta lumshe su bata jima ba ta ware su a fuskar Ifti ba tare da ta ce komai ba. Ajjiyar zuciya Ifti ta sauke a sanyaye ta ce "Ba damuwa Daada kika sakawa ranki ba ina fata rabin rai?"
"Daada....?
Yadda ta yi furucin da yadda ta ambaci sunan Daada zaka ɗauka bata taɓa jin sunan ba sai a lokacin. Furucin da Ana ta yi ya daskarar da jinin jikin Ifti da wani irin sabon tashin hankali ta ce "Kin san me kika ce? Kin san abin da kalmominki ke nufi?"
Ana ta girgiza kai ta ce "A'a"
"Waye Daada? Da gaske ban waye shi ba?" Iftihal ta ce
"Ina tunanin Sunanki Ayshatul-Haleeym Ana Daada, wannan sunan da yake maƙale da sunanki kamar rai da ajali, wannan sunan da idan babu shi ba ki gama zama cikakkiyar ƴar sunna ba, wannan sunan da zai ta bibiyarki har yaranki da za su amsa sunan jikokin Daada.. wannan Daada mahaifinki"
Ana ta bubbuɗe idanunta kafin ta juya ƙwayar idanun ta ce "Oh! Idan na fahimta wannan mutumin mai dukan matarsa, wannan dai mutumin me shigo mana gida tsirara cikin talatainin dare, hakazalika wannan mutumin me bin manta banza wanda yake da karuwa me suna Tani, wannan dai mutumin me yin caca shi kenan nufi? Shine Daadan da kike magana akai?"
"Ana!"
"Iftihal....
Ta kira sunanta itama cikin sanyin muryarta mara son hayaniya da rashin É—aukan raini.