← Book details Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 64

Sashe 38

Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Rabani da Bala ɗiyar arziƙi, Bala fa? Tabɗim" Iftihal ta zubawa Yaa Jadid dake kwance idanu kan shi a kan cinyar Innti tana masa addu'a da firfita da mafici. Da rawar muryar sosai jikinta na rawa Iftihal ta ce

"Ko za ki siyar da kan kekenki sai a nemi ciko?"

"Wanne keken? Kan nan ko dubu goma ba zai yi ba, asara ce siyar dashi, kuma dashi nake amfani me hamsin ɗari ina mana abin da ya sawwaƙe na kai wa baka, ga mai atamfar can da ɗinkin ya lalace tana ta sintiri na rasa mene ya lalata ɗinkin lafiya ƙalau na kammala" Iftihal ta fashe da wani irin kuka jikinta na rawa ta kasa cewa komai, Yaa Jaheed ma shirun ya yi yana lissafin rayuwa da inda zai iya samu kuɗi akai ɗan'uwan nasa asibiti, duk inda ya yi tunani sai yaga a rufe hanyar take babu sauƙi ko kaɗan a lamarin. Hatta ogansa na wajan aiki ya tambaya yace babu kuɗi a wajansa

A daidai wannan lokacin kuma Ana ce a cikin ɗaki zaune ta rungume hannayenta a ƙirji idanunta rufe, sai ka ɗauka bata da rai sannu a hankali ƙirjin nata ke ɗagawa. Tunani take yi ita da zuciyarta, wacce hanya za ta bi wajan ƙwatuwa Innti haƙƙinta, da matsayinta? Wanni littafi da Zainab Alƙali ta karanta ne ya faɗo mata, ta tuna yadda matar takai mijinta ƙara ofishin ƴan Hisba, har aka hukunta mijin akan kuskuren da ya yi, hukunci irin wanda Shari'a ta tanata. A fili ta ce

"Ina ne ofishin ƴan Hisba a nan? Ina zan samu kuɗin mota?" Ita kam ko a ƙafa ne zata iya zuwa muddin zata samu ganin jama'an hisbar.

Sallama ake ta rafkawa a ƙofar gidan sai Babban yaya wanda yanzu ya shigo ya miƙe domin ganin waye, yana fita ya yi turus ganin Alhaji Baita, kallo ɗaya ya yi masa ya kawar da kai, ba ɗabi'ar zuri'ar Innti bace raina na gaba don haka a ladabce ya gai da Alhaji Baita cikin kamilalliyar muryarsa wacce sai a lokacin Baita ya taɓa jinta. "Yawwa nace ina Ayshatul-Iftihal ɗin? Na biyo sawu ne na gaza haƙuri naga har war haka ba'a kawo ta gidana ba, kamar yadda muka yi da Daada"

Da rashin fahimta Babban yaya ya juya idanunsa alamar "Wacce Aysha? Wanne gidan kuma?"

A fusace Baita ya ce "kai bana son shiririta uban naku bai baku labarin ya saka Iftihal a caca ba, kuma nine wanda na yi nasara, idan baka da labari yanzu ina baka, akan naira miliyan ashirin ya saka Iftihal a caca, kuma nine wanda ya yi nasara na riƙe kuɗaɗena, kuma na ci yarinya. Ka shiga ka fito mini da ita yanzu mu shige, tun safe nake jiƙe-jiƙe a takure nake ta ciki, banda yayyu babu abin da nake yi. Yau ranar hutawa ta ce Allah ya kashe ya kuma bani"

Babban yaya ji ya yi komai ya tsaya masa ya kuma daina fahimta, ya kalli Alhaji Baita sama da ƙasa, iya haƙorinsa kaɗai tayar masa da zuciya yake yi, ga cikinsa kamar an yi masa ajjiyar yara goma, ko kuma wanda mayu sukai masa ajjiya. "Yanzu ita Iftihal kaza ɗauka?" Haka kallon Yaya ya bawa Alhaji Baita raddi. Alhaji Baita ya ce "A rubuce wannan take"

Sai ya yi baya kaɗan ya jinjina kai alamar "Tana ciki, jeka ɗauke ta" abu kamar wasa yaga Alhaji Baita yana ƙoƙarin shigewa cikin gidan da sauri ya saka hannunsa ya tura shi baya da wata kakkausar muryar data motsa zuciyar Baita saboda kwarjinin da take dashi ya ce "Ashe girman biredi ne kawai da kai, baka da saiti har haka? Bari na faɗa maka gaskiya, yadda kukai cacarku babu wanda ya sani haka yanzu zaku ƙare ta iya ku. Muddin ina numfashi kuma ɗan halak ne ni wallahi Iftihal ta haramta a gare ka, ni kaina da kake ganina ɗan wahala ne ni, rashin sanin waye ni zai saka ka yi maganar nan....," bai ƙarasa faɗa ba ya ji an ɗauke shi da mari, kafin Babba yaya ya dawo hayyacinsa cike da ƙonar rai Yaa Jaheed ya wankawa Alhaji Baita mari, ya rama marin da Daada ya yi wa Babban yaya, da gudu kuma ya arce cikin gidan.

Alhaji Baita ya kalli Daada ya ce "Ashe yaranka basu da tarbiyya?" Daada ya ce "Ina suka ganta daman? Ko wani ya faɗa maka suna da ita?" Sai ya juya kan Babban yaya ya ce "Kai kuma muddin kai ba ɗan shege bane, bada cikinka uwarka ta shigo gidana ba, ka yi gigin hana shi tafiya da ita mu gani, sakarai wawa tasono hanci duk majina, kana tafiya kamar mace lusari. Ai tunda ka fito daga cikin Innti babu yadda za'ayi ka zama wani abu a rayuwa, babu yadda za'ayi ka yi nasara a rayuwa sai ka lalace ka zama annoba wa jama'a, dukkaku lalatattu ne billahi" saboda tsananin ɓacin rai idanun Babban yaya har wani rawa suke bayan firfitowa waje da sukai jijiyoyin kan shi suka mimmiƙe, sai yanayinsa ya fara sauya da sauri ya fice daga cikin gidan gabaɗaya.

Daada ya kalli Baita ya ce "Jira na fito da ita"

A can cikin gidan kuma bayan Yaa Jaheed ya shiga a guje bai iya tsayawa a wajansu ba, ɗaki ya shige kai tsaye ya rufe ya fashe da wani irin matsanancin kuka, wai Iftihal aka saka a caca? Har lusari bagidajen mutumin na iƙirarin zai huta da ita. Ji yake yi kamar ya haɗiye zuciya ya huta.

"Sannu ƙaunata ba dai jikin bane ko?"

Cewar Iftihal tana kallon Ana.

A hankali ta lumshe idanunta cikin sanyin murya ta ce "Yaa Sam ya ce zai zo kuma shiru" murmushi Iftihal ta yi kafin ta ce "Allah dai ya nuna mana wannan rana"

Da rashin fahimta ta juya idanunta ta ce "Heee, wacce rana?" Harara Iftihal ta watsa mata kafin ta ce "Kinga wacce na yi aiki a gidansu yau" ta nunawa Ana picture ɗin Nadiyaah da Diyanah ta yi status dashi, a tunaninta Diyanah ɗince. Ana ta zubawa photon Nadiyaah idanu musamman idanunta a hankali ta ce "Idanunta manya masu kyau dasu" sai kuma ta taɓe bakinta.

Iftihal itama zubawa idanun ido ta yi a fili ta ce "Tubarakallah ma sha Allah kam dasu"

"Kina ina fito don uwarki wannan mara amfanin a duniya, wannan wacce ta yi asarar haihuwa duniya da lahira wannan mara rabon, sai kun farraƙa in sha Allah" muryarsa kaɗai tsayar da numfashin Innti da yaranta yake idan ka ɗauke Ana da Babban yaya. Wani irin masifar tsoron Daada suke yi kamar sun ga mala'ika.

Jikin Iftihal na rawa ta miƙe tsaye, ana kam ko motsi ba ta yi ba, domin hargagin zautaccen mutumin nan ya daina zama damuwarta. Ɗaki Daada ya shige yana sababi. Ana ta kalli Iftihal sosai ta ce

"Wai meye kike rawar ɗari, kifa daina saka damuwar bugaggen mutumin nan akan ki. Wallahi idan ba haka ba, watarana sai ya zama ajalinki sai ya kashe ki da baƙinciki ya rabaki da duniya. I'm telling you ki share shi" Da wani irin ƙarfi da firgitacciyar murya Iftihal ta ce "Mahaɗita na shiga uku, a caca Daada ya saka ni, yanzu haka gidan Alhaji Baita zai kai ni, ni Daada ya saka a caca kuma an yi nasara akan shi. Ya hanamu zuwa makaranta a sanda zamu rubuta jarrabawa ta shiga SS1. Burinmu ya rushe Ana, mafarkanmu sun zama tarihi Ana, ba zan taɓa zama ƴar jarida ba, ba za ki taɓa zama marubuciya ba. Ya ce zai tsine mana idan muka je makaranta ko a bayan idanunsa ne" zumbur Ana ta miƙe jikinta duka rawa da ɓari yake idanunta na lumshewa yana ƙaƙƙafewa numfashinta na ƙoƙarin tsayawa ta futar da kalmar bakinta a wahalce

"Kan uba, uban kuturu ya yi kaÉ—an balle na makaho, wallahi bai isa ya hanani zuwa....,"

Kafin ta ƙarasa Innti ta saka bayan hannunta ta make mata baki, nan take leɓenta na ƙasa ya fashe, da wani irin yanayi na sarewa da macewar zuciya daga abin da take so Ana ta ce "Innti duka?

"Me ya sa bakya so na ne Innti......" Ta kasa ƙarasawa

"Saboda mijinki kike wannan?"

Jajur haka idanun Innti ya yi gashi sun ƙanƙance tare da shigewa ciki tana wani irin haki da dafe ƙirji ta ce "Saboda duk abin da zuciya ta raya miki ne Nanaah, wallahi akan idanuna ko bayansa, ina duniya ko bana duniya kika bijirewa Daada, ki kai rashin biyayya a gare shi ban yafe ba, ban yafe muku ba duka. Mahaifinku ne yana da iko da hakan, duk abin da ya zartar akan ki ya zartu babu haufi. Mene don ya saka Iftihal a caca? Haka tunaninsa da lissafinsa ya bashi, hakan yake ganin shine dai-dai. Idan ƙaddararta ce hakan babu yadda za mu yi sai dai mu yi mata addu'a Ubangiji ya bata haƙuri da juriya ya sanya mata salama ko?" Cike da takaici da baƙincikin da ya yi mata yawa a zuciya take faɗin hakan

"A'a.... A'a Innti" Iftihal ta ce tana ƙanƙame jikinta da rusa wani irin firgitaccen kuka ta ce "Ba ruwan ƙaddara, idan ma akwai ta, Daada ne ya zaɓa mini wannan muguwar ƙaddarar da kan shi. Don Allah kar ki bari ya tafi dani, Innti ke uwa ce kin san ɗaci da raɗaɗin hakan, kin san zafin dake cikinsa. Wallahi idan Daada ya tilasta zuciyata zata iya bugawa. Innalillahi wa'inna ilaihirraji'un! Na shiga uku, ki taimaka mini Sahibata"

Ana ma fashewa da kuka ta yi taje ta rungume Iftihal ta sumbaci goshinta da kuncinta ta riƙo hannayenta ta sumbata. "I promise you in dai ina raye babu inda za ki, idan dole sai kin je zani a madadinki, za'a maye gurbina dake, ki zauna da Innti ko ƙaddarar ce ni na shirya mata, ni na amshi ƙaddarar" kuka suke yi sosai sun ƙanƙame juna. Innti sulale wa ta yi a wajan, ta kasa fitar da hawaye balle kuka ta yi hooking ma gabaɗaya bata sam meke yi mata daɗi ba, bata hayyacinta balle ta lura da suman da Yaa Jadid yake yi.
Chapter 38 · 0% Book details