Sashe 20
Hiyaam Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Batty, kai yaro Batty meke damunka?" Ya yi furucin cikin sarƙewar murya domin shi kan shi jikinsa rawa yake yi saboda tsoron yanayin yarinyar daya gama gitta masa zuciya. A hankali ta ɗago kanta tare da buɗe rinannun idanunta, ganin yadda idanun ya yi wani irin jaa ya firfito waje kamar bana mutane ba, ya saka cikin Lami juyawa ta yi saurin saka hannunta ta dafe cikin ta ce
"Ko dai Batty nada iska Dikko?"
"Bana jin haka daga gare ta Lami" Sai ya yi gaba daidai inda Batty ke durƙushe shima ya durƙusa a wajan ya saka hannunsa ya kama hannunta cike da nutsuwa da kulawa ya ce "Mene ya samu ɗiyar nan?"
Baki ta buɗe za ta yi magana sai suka ji kukan mage ya cika ɗakin, wani irin kuka mara daɗin ji wani amon sauti na fita, tuni fitsari ya cika wandon Lami jikinta sai rawar ɗari yake yi. "Yi magana Batty menene?" Wannan karon ma madadin sautin muryar Batty ɗin ya fita sai kukan mage ya sake karaɗe wajan, kafin kuma tif su ji ƙarar saukar abu a gadon bayan Dikko, wani irin hantsilawa Lami ta yi tare da yin allandugure ta kifa, zanin jikinta ya yi gefe guda bata tsaya ɗauka ba ta yi waje fitsari na bin cinyoyinta, a hanya ta haɗu da Sadiatu data fito da sauri tana kiran Dikko ta faɗa masa cewa Allah Ya yi wa yaron Kulu rasuwa, suna haɗuwa da Sadiatu a hanya ta yi gefe zata shige ɗakinta. Sadiatu ta ce
"Lami yaron Kulu ya koma" Kafin Lami ta yi magana sun ji yo ihun Dikko daga cikin bukkar Batty wani tsalle suka yi tare da rungume juna suna salati da ƙarfi, suna rungume da juna Dikko ya fito a guje yana faɗin ya shiga uku zata kashe shi ta cinye masa hannu, tun kafin ya ƙarasa fitowa Lami da Sadiatu sun rugasa ƙarasawa cikin bukkarsa kafin ya ƙarasu sun rufe yana ganin haka ya yi kwana ya nufi ɗakin Kulu wacce take rusa kukan rashin jaririnta.
Yana zuwa ya tarar itama ta rufe ɗakin nata, sai kawai ya fashe da kuka ya kama bukkar Kulu ya haye saman bukkar, yana hawa kamar an ce ya juya suka yi ido huɗu da wata baƙar mage jibgegiyya da ita idanunta jajur sai haki take yi tana zaro harshe waje. Cak numfashin Dikko ya tsaya a ƙirjinsa daga nan bai sake sanin abin da yake faruwa ba.
Dikko na fita daga bukkar Batty sai ta yi saurin miƙewa tsaye idanunta rufe ta fito farfajiyar gidan shiru babu kowa, sannu a hankali ta dinga takawa har ta isa banɗaki ganin babu me ganinta ya saka ta tsugunawa waje guda ta cure jikinta, tana daga durƙushen ta fara wata kalar rawa da girgiza ta kafe yatsun ƙafarta a ƙasa tana kartar ƙasa dasu, a hankali halittar jikinta ya fara sauyawa zuwa suffar mage bata ɗauki lokaci ba, ta koma wata baƙar mage me jajayen idanun ta yi tsalle tare da haure kewayen banɗakin ta yi waje abin ta. Tafiya magen take yi hankali kwance da idanunta na huɗun take cin karo da kurwar jama'a dake yawo a duniya a cikin sakaliyar daren.
Dake yawanci sai dare yayinda gangar jikin mutum ke kwance yana samun nutsuwa a wannan lokacin ne kuma kurwa take tashi ta shiga duniya ta dinga yawo, wannan dalilin ya saka idan ka haɗu da mutum a zahiri sai ka fara tunanin kamar ka san shi, kuma ka rasa inda ka taɓa ganinsa. Hakan ya faru ne dalilin kurwarku data haɗu da daddare a hanya. Wasu kuma na cewa
Ruhi ne yake tashi yabar gangar jiki.
Tunda Batty ta yi arba da Mado ta ji ranta ya biya, domin yana da kitse sosai jininsa da namansa masu kyau ne za su yi daɗi a baki. Wannan dalilin ya saka ta biyo dare ko za ta iya cimma burinta a wannan karon, wannan ne lokaci na farko da take jin ba zata iya haƙura da abin da take ji ba akan Mado ba. Har cikin gidan Moddibo ta kutsa kai cikin sa'a ta samu ɗakin Mado ta haye rufin ɗakin ta shiga rera masa kuka a cikin kunne mara daɗin ji saboda wani amo da yake fita a ciki
"Mado... Mado... Mado..."
Haka magen ta dinga kiran sunansa.
A firgice Mado ya farka jin abin ya yi kamar a mafarki, ya zabura ya miƙe tsaye yana juyawa ya ci karo da Moddibo yana tsaye, Mado ya nufi wajan mahaifinsa yana faɗin
"Baka ji ba?"
Ya girgiza kai. "Baka ji kukan mage ba?"
"Sunana na ji ana kira" Moddibo ya kalli Mado, a wannan lokacin da Mado ya nutsu zai iya hango ƙwayar idanun Batty a cikin idanun Moddibo zai fahimci Batty ce bawai mahaifin nasa ba. Moddibo ya miƙa hannu kamar zai riƙo Mado sai kawai ya kai hannun zuwa wuya Mado ya shaƙe masa wuya, Mado ganin Mahafinsa ne sai bai shiga ramawa ba, ya dinga kokawar ƙwace kan shi amma ya kasa, sai da aka kai Mado ƙasa baya ko motsi kafin Moddibo ya bar ɗakin daidai nan magen ta yi sauri ta fice daga cikin gidan gabaɗaya.
Sama-sama ya ji ana kiran sunansa, gabaɗaya jama'ar gidan sun cika ɗakin Mado saboda ihun daya dinga yi, a hankali ya buɗe idanunsa sai yaga ƙannensa da sauran ƴan'uwansa, salatin da ya ji ana yi ne da tofin da ake yi masa da sautin muryar Moddibo ya saka Mado ƙoƙarin juyawa amma ya kasa saboda kasalar data saukar masa a jiki, ga wuyansa daya kumbura.
Sai ya mayar da idanunsa ya lumshe.
***
Bayan sallar issha'i duk suna zaune a ƙasan bishiyar da Iftihal ta shimfiɗa musu babbar tabarmar da suka saba zama akai wajan cin abinci da hira. Jadid da Jaheed na zaune suna hira sai Iftihal data gama jera musu kwanikan da aka kwasa tuwo da miya a ciki haɗe da babban tire da babban jug, Innti na saman darduba tana azkar. Jadid da yake ta jin sauyin yanayin da yake tabbatar masa ciwonsa zai tashi yaja idanuna ya lumshe a ƙasan zuciyarsa yana addu'ar Ubangiji ya sauƙaƙa masa wannan jarrabawa ya kawo masa da sauƙi. Babban yaya ne ya shigo ciki hannunsa ɗaya cikin aljihu ɗaya kuma riƙe da wayarsa farar Jallabiya ce a jikinsa wacce tabi fatar jikinsa ta kwanta yana da buɗaɗɗan ƙirji tsayi da faɗi a tsaye yake sosai, bai saka hula ba, sai kyakkyawar sumar kan shi data bi fatar wuyansa ta kwanta sai ɗaukan idanu take. Sun san dole zai yi sallama duk da basu ji ba, amma haka suka haɗa baki wajan amsawa. Ya nemi waje ya zauna.
Iftihal ta ƙarasu inda yake ta durƙusa har ƙasa ta ce "Barka da dare Babban yaya, ya aiki?" A nutse ya dubi Iftihal kafin ya ɗan lumshe idanunsa, gargasar idanunsa suka sauka a fatar idanun nasa ya sakarwa Iftihal murmushi. Ta ce "Babban yaya za mu fara exam ta shiga Ss 1 a makaranta gobe"
Ya zuba mata ido, sai ya miƙa hannunsa kaɗan ya riƙe nata ya ɗan matse kasan
Alamar "I wish you all the best" Cikin jin daÉ—i ta ce
"Thank you Babban yaya" Wajanta ta koma ta zauna, Babban yaya kuma idanunsa ya dinga juyawa yana neman inda zai hango Ana amma bata tsakar gidan. "Ƴan'matan Innti ana ta girma wasa-wasa daga secondary school sai University sai kuma aure, ina ka gane mini fuskar tagwaye a ɗakin miji? Musamman ke" ya ƙare maganar yana kallon Iftihal.
Iftihal ta ce "Kai Yaa Jaheed, aure kuma?"
Ya ce "Shi fa, ai kece bakya damun mu da maganar saurayi ko miji. Ita kuma tattabara kullum maganar Allah ya bata kyakkywan miji take yi koda maye ne ba ruwanta"
"Ko kuma Aljani ba" cewar Jadid.
Babban yaya ya watsa ƙwayar idanunsa a fuskar Jadid jin ya ce Alljani sai ya ɗauke kai.
Innti data kammala azkar ta ce "Ƙuruciya dangin hauka, mazan yanzu ya ka ƙare dasu balle ka dinga yi wa kan ka mummunan alkaba'i? In sha Allah mazaje nagari Ubangiji zai muku tukuci dasu, kuma za ku samu mataye na gari da za su zame muku abin alfahari. Bani da addu'a wacce ta shige taku"
"Muna godiya uwar arziƙi irin albarka, Allah Ya yi mana arziƙin da za ki ji daɗi a duniya Babarmu"
Ta ce "Arziƙi na tsoran Allah in sha Allah"
Iftifal ce ta ce "Innti shalele bata fito ba?"
"Ƙyale Ana kin ji Iftihal miskilancin ne ya motsa tun ɗazo take ta ƙunci, kin san an yi tuwo" suka kwashe da dariya abin su.
Æata fuska Iftihal ta yi ta ji itama abincin ya fita a kanta tunda mahaÉ—inta haka zata kwana da yunwa, gashi yau ta fahimci akwai abin da yake damun Innti taÆ™i nuna musu ne. "Innti nima na Æ™oshi, bari na jira ki yi mana tatsuniya kawai kafin na kwanta"
Innti ta zubawa Iftihal idanu kafin ta numfasa zuciya babu daɗi murya a karye ta ce "Ina son ku dinga haƙuri da abin da kuka samu kuke dashi a rayuwa, ni ba kowa ba, ban banda ajjiya ba, ba'a bani ba, bamu da wani gata ɗaya shige na Ubangiji. Ku dinga haƙuri da abin da kuka samu wasu suna nan a daren ko tuwon basu samu ba, mu hakan ni'ima ce a gare mu kin ji?" Iftihal ta jinjina kai ta ce "Kece gatanmu a nan duniya Innti, bamu da haufi akan kulawarki, ba kuma takaicin cin tuwon nake ba, ina samu kaina da rashin sukunin zuciya idan naga mahaɗita tana cikin damuwa ki yi haƙuri"
"MahaÉ—inki halinta dabanne da naki, ta fiki jarumta da taurin zuciya, ki barta da masifar son da take miki da Inntinta ta gargajiya, wannan soyayyar da take mana ita ce jarrabawarta" Murmushi Iftihal ta yi ta ce
"Ban san ya zata yi ba idan na yi nisa da ita" Jaheed ya ce "In sha Allah brothers za ku aura tagwaye, da suka fito ciki guda suma"
"I hope so bro.....
Jadid ya É—an yatsuna fuska ya ce
"Turawan zamani, daman a Government school ana koyar turanci har haka Innti?"
"Ko dai Batty nada iska Dikko?"
"Bana jin haka daga gare ta Lami" Sai ya yi gaba daidai inda Batty ke durƙushe shima ya durƙusa a wajan ya saka hannunsa ya kama hannunta cike da nutsuwa da kulawa ya ce "Mene ya samu ɗiyar nan?"
Baki ta buɗe za ta yi magana sai suka ji kukan mage ya cika ɗakin, wani irin kuka mara daɗin ji wani amon sauti na fita, tuni fitsari ya cika wandon Lami jikinta sai rawar ɗari yake yi. "Yi magana Batty menene?" Wannan karon ma madadin sautin muryar Batty ɗin ya fita sai kukan mage ya sake karaɗe wajan, kafin kuma tif su ji ƙarar saukar abu a gadon bayan Dikko, wani irin hantsilawa Lami ta yi tare da yin allandugure ta kifa, zanin jikinta ya yi gefe guda bata tsaya ɗauka ba ta yi waje fitsari na bin cinyoyinta, a hanya ta haɗu da Sadiatu data fito da sauri tana kiran Dikko ta faɗa masa cewa Allah Ya yi wa yaron Kulu rasuwa, suna haɗuwa da Sadiatu a hanya ta yi gefe zata shige ɗakinta. Sadiatu ta ce
"Lami yaron Kulu ya koma" Kafin Lami ta yi magana sun ji yo ihun Dikko daga cikin bukkar Batty wani tsalle suka yi tare da rungume juna suna salati da ƙarfi, suna rungume da juna Dikko ya fito a guje yana faɗin ya shiga uku zata kashe shi ta cinye masa hannu, tun kafin ya ƙarasa fitowa Lami da Sadiatu sun rugasa ƙarasawa cikin bukkarsa kafin ya ƙarasu sun rufe yana ganin haka ya yi kwana ya nufi ɗakin Kulu wacce take rusa kukan rashin jaririnta.
Yana zuwa ya tarar itama ta rufe ɗakin nata, sai kawai ya fashe da kuka ya kama bukkar Kulu ya haye saman bukkar, yana hawa kamar an ce ya juya suka yi ido huɗu da wata baƙar mage jibgegiyya da ita idanunta jajur sai haki take yi tana zaro harshe waje. Cak numfashin Dikko ya tsaya a ƙirjinsa daga nan bai sake sanin abin da yake faruwa ba.
Dikko na fita daga bukkar Batty sai ta yi saurin miƙewa tsaye idanunta rufe ta fito farfajiyar gidan shiru babu kowa, sannu a hankali ta dinga takawa har ta isa banɗaki ganin babu me ganinta ya saka ta tsugunawa waje guda ta cure jikinta, tana daga durƙushen ta fara wata kalar rawa da girgiza ta kafe yatsun ƙafarta a ƙasa tana kartar ƙasa dasu, a hankali halittar jikinta ya fara sauyawa zuwa suffar mage bata ɗauki lokaci ba, ta koma wata baƙar mage me jajayen idanun ta yi tsalle tare da haure kewayen banɗakin ta yi waje abin ta. Tafiya magen take yi hankali kwance da idanunta na huɗun take cin karo da kurwar jama'a dake yawo a duniya a cikin sakaliyar daren.
Dake yawanci sai dare yayinda gangar jikin mutum ke kwance yana samun nutsuwa a wannan lokacin ne kuma kurwa take tashi ta shiga duniya ta dinga yawo, wannan dalilin ya saka idan ka haɗu da mutum a zahiri sai ka fara tunanin kamar ka san shi, kuma ka rasa inda ka taɓa ganinsa. Hakan ya faru ne dalilin kurwarku data haɗu da daddare a hanya. Wasu kuma na cewa
Ruhi ne yake tashi yabar gangar jiki.
Tunda Batty ta yi arba da Mado ta ji ranta ya biya, domin yana da kitse sosai jininsa da namansa masu kyau ne za su yi daɗi a baki. Wannan dalilin ya saka ta biyo dare ko za ta iya cimma burinta a wannan karon, wannan ne lokaci na farko da take jin ba zata iya haƙura da abin da take ji ba akan Mado ba. Har cikin gidan Moddibo ta kutsa kai cikin sa'a ta samu ɗakin Mado ta haye rufin ɗakin ta shiga rera masa kuka a cikin kunne mara daɗin ji saboda wani amo da yake fita a ciki
"Mado... Mado... Mado..."
Haka magen ta dinga kiran sunansa.
A firgice Mado ya farka jin abin ya yi kamar a mafarki, ya zabura ya miƙe tsaye yana juyawa ya ci karo da Moddibo yana tsaye, Mado ya nufi wajan mahaifinsa yana faɗin
"Baka ji ba?"
Ya girgiza kai. "Baka ji kukan mage ba?"
"Sunana na ji ana kira" Moddibo ya kalli Mado, a wannan lokacin da Mado ya nutsu zai iya hango ƙwayar idanun Batty a cikin idanun Moddibo zai fahimci Batty ce bawai mahaifin nasa ba. Moddibo ya miƙa hannu kamar zai riƙo Mado sai kawai ya kai hannun zuwa wuya Mado ya shaƙe masa wuya, Mado ganin Mahafinsa ne sai bai shiga ramawa ba, ya dinga kokawar ƙwace kan shi amma ya kasa, sai da aka kai Mado ƙasa baya ko motsi kafin Moddibo ya bar ɗakin daidai nan magen ta yi sauri ta fice daga cikin gidan gabaɗaya.
Sama-sama ya ji ana kiran sunansa, gabaɗaya jama'ar gidan sun cika ɗakin Mado saboda ihun daya dinga yi, a hankali ya buɗe idanunsa sai yaga ƙannensa da sauran ƴan'uwansa, salatin da ya ji ana yi ne da tofin da ake yi masa da sautin muryar Moddibo ya saka Mado ƙoƙarin juyawa amma ya kasa saboda kasalar data saukar masa a jiki, ga wuyansa daya kumbura.
Sai ya mayar da idanunsa ya lumshe.
***
Bayan sallar issha'i duk suna zaune a ƙasan bishiyar da Iftihal ta shimfiɗa musu babbar tabarmar da suka saba zama akai wajan cin abinci da hira. Jadid da Jaheed na zaune suna hira sai Iftihal data gama jera musu kwanikan da aka kwasa tuwo da miya a ciki haɗe da babban tire da babban jug, Innti na saman darduba tana azkar. Jadid da yake ta jin sauyin yanayin da yake tabbatar masa ciwonsa zai tashi yaja idanuna ya lumshe a ƙasan zuciyarsa yana addu'ar Ubangiji ya sauƙaƙa masa wannan jarrabawa ya kawo masa da sauƙi. Babban yaya ne ya shigo ciki hannunsa ɗaya cikin aljihu ɗaya kuma riƙe da wayarsa farar Jallabiya ce a jikinsa wacce tabi fatar jikinsa ta kwanta yana da buɗaɗɗan ƙirji tsayi da faɗi a tsaye yake sosai, bai saka hula ba, sai kyakkyawar sumar kan shi data bi fatar wuyansa ta kwanta sai ɗaukan idanu take. Sun san dole zai yi sallama duk da basu ji ba, amma haka suka haɗa baki wajan amsawa. Ya nemi waje ya zauna.
Iftihal ta ƙarasu inda yake ta durƙusa har ƙasa ta ce "Barka da dare Babban yaya, ya aiki?" A nutse ya dubi Iftihal kafin ya ɗan lumshe idanunsa, gargasar idanunsa suka sauka a fatar idanun nasa ya sakarwa Iftihal murmushi. Ta ce "Babban yaya za mu fara exam ta shiga Ss 1 a makaranta gobe"
Ya zuba mata ido, sai ya miƙa hannunsa kaɗan ya riƙe nata ya ɗan matse kasan
Alamar "I wish you all the best" Cikin jin daÉ—i ta ce
"Thank you Babban yaya" Wajanta ta koma ta zauna, Babban yaya kuma idanunsa ya dinga juyawa yana neman inda zai hango Ana amma bata tsakar gidan. "Ƴan'matan Innti ana ta girma wasa-wasa daga secondary school sai University sai kuma aure, ina ka gane mini fuskar tagwaye a ɗakin miji? Musamman ke" ya ƙare maganar yana kallon Iftihal.
Iftihal ta ce "Kai Yaa Jaheed, aure kuma?"
Ya ce "Shi fa, ai kece bakya damun mu da maganar saurayi ko miji. Ita kuma tattabara kullum maganar Allah ya bata kyakkywan miji take yi koda maye ne ba ruwanta"
"Ko kuma Aljani ba" cewar Jadid.
Babban yaya ya watsa ƙwayar idanunsa a fuskar Jadid jin ya ce Alljani sai ya ɗauke kai.
Innti data kammala azkar ta ce "Ƙuruciya dangin hauka, mazan yanzu ya ka ƙare dasu balle ka dinga yi wa kan ka mummunan alkaba'i? In sha Allah mazaje nagari Ubangiji zai muku tukuci dasu, kuma za ku samu mataye na gari da za su zame muku abin alfahari. Bani da addu'a wacce ta shige taku"
"Muna godiya uwar arziƙi irin albarka, Allah Ya yi mana arziƙin da za ki ji daɗi a duniya Babarmu"
Ta ce "Arziƙi na tsoran Allah in sha Allah"
Iftifal ce ta ce "Innti shalele bata fito ba?"
"Ƙyale Ana kin ji Iftihal miskilancin ne ya motsa tun ɗazo take ta ƙunci, kin san an yi tuwo" suka kwashe da dariya abin su.
Æata fuska Iftihal ta yi ta ji itama abincin ya fita a kanta tunda mahaÉ—inta haka zata kwana da yunwa, gashi yau ta fahimci akwai abin da yake damun Innti taÆ™i nuna musu ne. "Innti nima na Æ™oshi, bari na jira ki yi mana tatsuniya kawai kafin na kwanta"
Innti ta zubawa Iftihal idanu kafin ta numfasa zuciya babu daɗi murya a karye ta ce "Ina son ku dinga haƙuri da abin da kuka samu kuke dashi a rayuwa, ni ba kowa ba, ban banda ajjiya ba, ba'a bani ba, bamu da wani gata ɗaya shige na Ubangiji. Ku dinga haƙuri da abin da kuka samu wasu suna nan a daren ko tuwon basu samu ba, mu hakan ni'ima ce a gare mu kin ji?" Iftihal ta jinjina kai ta ce "Kece gatanmu a nan duniya Innti, bamu da haufi akan kulawarki, ba kuma takaicin cin tuwon nake ba, ina samu kaina da rashin sukunin zuciya idan naga mahaɗita tana cikin damuwa ki yi haƙuri"
"MahaÉ—inki halinta dabanne da naki, ta fiki jarumta da taurin zuciya, ki barta da masifar son da take miki da Inntinta ta gargajiya, wannan soyayyar da take mana ita ce jarrabawarta" Murmushi Iftihal ta yi ta ce
"Ban san ya zata yi ba idan na yi nisa da ita" Jaheed ya ce "In sha Allah brothers za ku aura tagwaye, da suka fito ciki guda suma"
"I hope so bro.....
Jadid ya É—an yatsuna fuska ya ce
"Turawan zamani, daman a Government school ana koyar turanci har haka Innti?"