Sashe 27
Batuul Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Bayan su Batuul sun gama cin abinci, wajen k'arfe uku Aunty ta ce su shirya suje gidan Ammah, ita yau baza ta samu zuwa ba, in sunje gaisheta, sai sun ha膹u a dinner, dan gudun magana Batuul ko attempting saka abaya ma batayi ba, wani peplum blouse da skirt na atamfa ta saka, ta samu k'aramin pearl pendant 膹inta da stud masu kyau suma ta saka, ta 膹auki k'aramin mayafi ta yana a kanta, Addua take a gama bikin nan ko zata huta da yawon nn ita kam, Baa Liman suka sa ya kaisu, k'arfe hu膹u suka isa gidan, gidan a cike yake da mutane kowa nata hidima, gaishesu suka rik'a yu har suka isa 膹akin Ammah, basu sameta ba a 膹akin ba, 膹akin Farida sukaje , da sauri Farida ta janyo k'ofar dan kamar ba 膹akinta ba, side 膹in Abui ta jawo hannun Batuul sukayi tana cewa Batuul "ni in zanyi aure baza a zauna a gida ba, dubi fa gidan kamar ba shi ba kuma fa masu aiki na ta gyara amma kamar basayi", "dama haka taro yake, sai an kwana biyu zakiga gidan ya koma daidai", suna isa side 膹in Abui Farida ta mur膹a k'ofan ta shiga, Ammah ta tarar ita da Aunty Amna suna zaune a 膹akin bak'i na side 膹in Abui tana yi mata bayanin wani abu, ga robobi nan manya manya a gabansu cike da kaji da snacks, k'arasawa sukayi daga ciki, Farida ce ta fara gaida Ammah da Aunty Amna, sai Batuul, bayan ta amsa gaisuwan ne tacewa Batuul "Bitti sai yau na ganki tunda aka fara bikin nan, lafiya bakya zuwa", kai ta sunkuyar sannan tace mata "Ammah ina zuwa, shekaran jiya ma naje wushe wushe", " toh yayi , madallah, 膹azu tela ma ya kawo kayanku na dinner na sa a 膹inka muku, sai kuyi shiri anjima kuje kunji", toh kawai Batuul tace amma ba wai dan ta saka zuwan a ranta ba, suna zaune su Ammah kuma nata bayanin yadda za a kai kayan nan gidan amarya, mik'ewa Farida tayi ta fita, shigowa tayi ita da wata yarinya 膹auke da plates a hannayensu na abinci, ajiyewa tayi ta zauna yarinyar kuma ta fita, cewa Batuul tayi ta taso suci abinci, mik'ewa Batuul tayi tazo kusa da ita ta zauna, 膹an kwalin dake kanta ta cire ta ajiye daga gefen gadon sannan suka fara cin abinci, sallama akayi a k'ofa, Sadiq ne ya shigo 膹akin , sai da ya gaida Ammah da Aunty Amna sannan ya zauna, Ammah ce ta dubeshi tace "kun dawo Sadiq, ya hanya, anyi lafiya babu matsala dai ko", kai ya girgiza tare da cewa "Alhamdulillah Ammah kunyi k'ok'ari mutane kamar turo su akayi a wajen 膹aurin auren nan, komai ya tafi lafiya", cewa tayi "Alhamdulillah , dama haka nake son ji, Allah ya sanya Alheri, Allah ya basu zaman lafiya" dukkansu suka amsa da Amin, Farida ce tace "Yaa Sadiq shikenan yanxu Yaa Abu zai bar zama a gidanmu, shikenan daga shi sai kai, gidanmu zai zama daga Abui sai Ammah sai ni, zanyi abinda nakeso", dariya ma ta bashi yace mata "zama gadin gidan zakiyi ashe, ai nima sai kin rigani barin gidan nan, waye ma zai barki ki zauna, next year kema by now munje maiduguri har mun dawo", b'ata rai tayi tare da zumb'uro baki tace "Ammah kin ga Yaa Sadiq ko", kamar ba ita ta fara hiran ba, "Sadiq ka dena damun ta tana cin abinci", dariya yayi ya mike yace "Ammah bari inje in dawo", tace "okay sai ka dawo", Batuul ji tayi sun birgeta, inama tana da yaya itama, amma irin Sadiq ba irin Yaa Abu ba dashi bama a ganin dariyanshi, Sadiq na fita yayi hanyan su ya ha膹u da ango, tsaidashi yayi yace "Abui ya shigo gidane naganka a side 膹inshi, ce mishi yayi "No Ammah na ciki, daga wajenta nake, yace "okay let me get to her", k'ofan falon Abui ya bu膹e, yana saka k'afa Batuul dake ciki taji gaba 膹aya ta zama restless, bugun zuciyan ta ya fara, a hankali ta rik'a tauna abincin dake bakinta, k'ofar 膹akin da suke ya tura ya shigo, cak komai ya tsayawa Batuul dan batayi expecting 膹inshi ba at this time, k'anshin turarenshi ya cika ko ina na 膹akin, da sallama ya k'araso 膹akin yana kare ma mutanan ciki kallo snn ya zauna a gefen gado, Gaisheda Ammah dake ta binsa da kallo yayi ta amsa tana masa sannu da xuwa, sannan ya gaida Aunty Amna da ta dage sae tsokananshi take, Farida ce ta gaisheshi ba tare da ta kallesa ba, ba yabo ba fallasa ya amsa mata, sau 膹aya ya kalli inda Batuul take ya 膹auke kanshi, ita dai bata ce mishi komai ba gashi nan dab da ita ya zauna, xame hannunta tayi daga plate 膹in ta cewa Farida ta k'oshi, Abuturrab na kallon Ammah yace "Ammah b茅ri manyin, (Ammah inason abinci) banyi breakfast ba yau throughout bare inci lunch ga yamma tayi", Aunty Amna ce tace "wannan duk 膹okin zama angon ne ya hanaka cin abinci" tana dariya tayi maganar, bai ce mata komai ba sae murmushin da yyi dan ya saba da tsokanar Aunty Amna, shi bai tab'a ha膹uwa da Aunty 膹inshi mai tsokana kamar ita ba, Ammah ce ta dubi inda su Farida ke cin abinci ta lura da Batuul bata cin abincin, tambayanta tayi "bitti ya akayine bakya cin abincin", murmushi Batuul ta k'irk'ira tace "Na k'oshi Ammah", ce mata tayi "Bitti 膹auko wa Abu abincinshi a palo, yana nan na shirya akan tray xa ki gani", a sanyaye ta mik'e tare da cewa toh, inda ta ajiye 膹ankwalinta ta duba zata 膹auka taga akai ya zauna, bata ce mishi komai ba tayi hanyan palo, binta yayi da kallo har ta b'ace sannan ya 膹auke idonshi tare da tabe baki a ranshi yace batason rufe kanta, dan yasha ganin gashinta on several occasion, mik'ewa Ammah da Aunty Amna sukayi suka fita dan sun gama abinda zasuyi, turowa kawai zasuyi a zo a 膹auki kayan, inda Farida take zaune ya duba yaga tana ta faman dambe da k'ashi, 膹auke kanshi yyi daga kallonta tare da jan tsaki, can ya sake dubanta gnin bata ma san yana yi ba sae fama da k'ashin take bayan ga nama me yawa a plate din yasa ya xabga mata harara yace "ke in baza ki ci abinci nan ba tashi ki fita, kin zauna kina ta kokuwa da k'ashi ko ina zaki kai na cikin plate 膹in" zumb'uro baki tayi tareda kinkiman plate 膹in abincinta tayi waje a ranta tana fa膹in "ohh masifaffe, mutum ran aurenshi ma sai yayi masifa ko ina ruwanshi da k'ashin da nake ci oho", ta fice abinta ya bi ta da harara.