← Book details Baccin So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 65 OF 87

Sashe 65

Baccin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

yana duba pulse nasa sai kawai yasake bude jakan magungunan sa dake wajen, wani allura yaciro yakallesa ahankali yace kwanta to kaga allura zan maka temperature zai sauka and you will be able to sleep yayi maganan yana kwantar da Saleem, da kyar da muryan datai karama Saleem yace bazaka tafi ba gyadamai kai Marwan yayi ahankali saiyasa hannu yadauki alluran Saleem yana kallonsa yazuko a syringe saiya ijiye kwalban hannun Saleem ya amsa, a jijiya yamasa alluran saiya ijiye yadauki towel da ruwa yadaura akansa da fuskansa yana matsawa ahankali Saleem ke kallonsa ko kyafta idanu bayayi a kallon Marwan, akwai wani aura da Marwan ke dashi dake sama mutum natsuwa idan Marwan na tare dashi saiyaji ya natsu yadena ganin abubuwan, dinga shafamai towel Marwan yayi yana xaune awajen yanayi yana kallon time alalace saida yabata 30min chur tun bayan kiran da Mami tamai sannan alluran yayi taking effect a jikin Saleem bacci ya kwashesa mai nauyin gaske. Dasauri Marwan ya ijiye towel din yamike yakashe wutan dakin yawuce yafito yarufomai kofa Kusan bayan 10min da kiran Marwan amman shiru baizoba Amirah kaman zata mutu, waya Mami tadauka takira Maryam tasa amata Lipton mai dumi adan matsa lemun tsami a ruwan akawo mata sannan ta ijiye ta da kyar tawuce bayi tadebo ruwan zafi a bowl tasaka towel tafito daidai Ya Maryam nakawo ruwan dumin itama hankalinta yatashi ganin Amirah batada lafiya but ita tadauka normal ciwon marane, Mami tace mata ta tafi suje su kwanta dan gobe duk zasu koma gidajen su, tafiya tayi. Mami taba Amirah Lipton din Tasha kadan sai Mami tashiga gasa mata mara da towel mai zafin tun tana kuka saita fara rage kukan zafin da towel din ke dashi aka dauka amaranta sai kaman yana warware mata abinda takeji da tik tana kuka kadan kadan saita dena tafara hamma tayi hamma kusan sau biyar kafin bacci yayi awon gaba da ita kanta na jikin Mami. Mami tadade tana kallonta sai wani abu ya tsaya mata azuciya, hawaye taji sun sauko mata dasauri takai bayan hannunta ta share, Amirah is extremely innocent Ya Rabbi da bamatasan meke wakana da itaba, da ace yarinya ne datai wayau na yammatan yanzu ta Ina har zasubar mijinsu yagane sha awa sukeji? Koko sununa sunji dadin abinda yamusu sunason yacigaba never. Zuciyan Mami ciwo yake mata cus this is the second time Marwan ke choosing Sale akan matarsa, tasan Marwan na son yarinyar, yarinyar da sonta har yasa yadade a asibiti but what is all this? Deep down she knows this is character Marwan, he cares for everyone and arayuwansa Marwan irin mutanen nanne da they don t know how to say no, basu iya fadin no ba, and wani zubin he feels zai iya dakatar dana gida yayi pleasing na waje like zata iya tana bukatar abu Marwan yabata hakuri yace anjima zai sayo abun only sabida yanzu yana attending to wani na waje he feels family can understand, this is halin Marwan, and yanzu daya auro yarinya that s not that normal, he must adjust and set priorities right cus Amirah needs him and she needs to be his number one before any other thing, Mami tai shiru tana kallonta, yanzu take kara ganin dalilin dayasa mahaifiyar yarinyar bataso ta aurar da diyarta now look at it daga kawota jiya bai dagamata kafafu ba in this her condition ya mammatse yarinyar mutane yamata abinda bata sani ba and jikinta yadauki abun, yazo ya lallubeta yagudu yabarta da ciwon ciki is this not wickedness, duk Mami na maganan zucin nan taji an bude kofan dakin ahankali da yar sallama chan kasa kallo daya yamusu Marwan ya sauke kansa kasa dasauri yana maida kofan yarufe ayanda yaga tana bacci akan cinyan Mami yasan awahale tai baccin yaga cup na ruwan Lipton dabata shanye ba tarage yaga towel cikin bowl na hot water, kasa magana yayi Kansa akasa kunyan Mami yakeji wlh yanda yayi abu adakinta, sosai Mami takallesa sama da kasa sai kawai ta dauka kai tace zaka iya tafiya ka koma kacigaba da abinda kakeyi Dan ijiyan zuciya yasauke yana shafa kansa ahankali yace Mami dan Allah kiy Marwan Mami takirasa kai tsaye, cikin kakkausan murya tace look at me dan dago kansa yayi yakalleta suka hada idanu, strictly Mami tace do you even know what love is Marwan? Dan at first na dauka you love this girl but you don maida kansa kasa Marwan yayi ahankali, kwantar da Amirah Mami tayi taja bargo tarufa mata ta mike tazo gaban Marwan dab dashi ta tsaya bata wani daga murya but yet kasan fada take tace I always sees you as mutum mai hankali hikima but yanzu i think all those attitude weren t you true hali, you knew wacece yarinyar nan kadage uta kakeso cikin hikiman Allah ka aureta, this is just 24hrs da zuwa ta gidanka but all she has been through is pains you are never there for her Mami tayi shiru tace kaga abinda kakeyi yanzu is the same reason dayasa mahaifiyarta ta turo yayanta asibiti dan asanar damu cewa batason ta auren da yarinyar ta, gashinan kaima sabida kaga bawai tanada cikakken kai bane balle tai understanding komi and fight for her right saisa kake treating dinta like a trash kataba jikinta kaji dadi kazubar da ita kaje kana another things right ? Dan runtse idanu Marwan yayi dan wlh wlh babu abu makamancin all abinda Mami ke fadi aransa he loves Amirah morethan his life and he will never take advantage of her condition what happened koda mai lafiya ya aura is the same thing that will happen, baida yanda zaiyi ne, but bazai taba iya gardama da Mami ba, Mami is his mother idan ranta yabac he dares not talk, all abinda zaiyi is yabata hakuri, ahankali yace Mami dan Allah kiyakuri! Shiru Mami tayi tana kallonsa itafa tadauki Amirah diyarta abinda zatayi akan Farida da Faiza is abinda zatayi akan Amirah, strictly tace okay but I have few things to tell you, first thing tomorrow morning inason the same way kadaiuko Saleem ka kawo gidan nan kadaukeza kamaidasa gidan Hajiya marikiyar sa wanda nanne usulin g danda dan Saleem and matarka can never leave in dsame house unless dukanmu anan mun tabbatar dayayi taubatan nasuha sannan yadena son matarka kwata kwata azuciyansa! Ahankali Marwan yadago kansa yakalli Mami, Mami tace oh bazaka iya kaisa dayan gidan ba ko ? Adan hankali Marwan yace Mami ahmmm yadanyi shiru saita kara rage murya sosai yace ni da Amirah mukoma gidanmu please kai tsaye tace sabida ka afkamata and the next minute you will come running to take care of dan uwanka ita kabarta cikin ciwo? Mami tai dan shiru tace at this point I don t trust the love dakake cewa you have for Amirah sabida for the past 24hrs baka kula da yarinyar nan daidai dana one minute ba, I know she s your wife but as a mother I have the right na karbeta naga cutar da ita zakayi, Marwan bazan kara baka yarinyar nan ba saina tabbatar da where you stand, banda haka I will be taking her to hospital zan nema mata lafiya dakaina kai kasha zamanla kula da dan uwanka mai dan uwa Marwan yakalli Mami dasauri zaiyi magana cikin tsananin fushi dan Marwan ya mugun bata mata rai tace wuce kafita dan kallon Mami yayi saiya juya ahankali zuciyansa namai radadi da zafi da ciwo ahankali yakai hannunsa kofan zai bude strictly Mami tace one last thing ka kara shigomin daki koka karama yarinyar nan wani abu dazai jefata halin data shiga yau wallah saina cimaka mutunci sosai Marwan ahankali yabude kofan dakin yafita ran Mami sai tafasa yake nobody will understand yanda Marwan yayi annoying dinta wani takaici daya batako kaman tarufe sa da duka. She said so much bawai she meant everything bane Allah yasani kawai tafadi ne sabida ya tsorata yasan darajan Amirah yasan duk sanda yamata badaidaiba akwai masu hukuntasa inba hakaba zai dinga daukan Amirah not to serious itakuma she wants him yadauki matarsa very serious tazama yar gaban goshinsa irin ita yake gani dinnan, wlh ko gobe jibi taga ya chanza zata basa matarsa kawai she wants to see the change ne. Hanyar dakinsu Matwna yadauka instead of yashiga dakinsa inda Saleem yake saiya shiga dakin Saleem yamaida kofan yarufe ahankali ya sulale yazauna nan gaban kofan idanunsa sunyi jaa zuciyansa batamai dadi ya lumshe idanu yayi shiru yana tuna komi daya faru he knows bai kyauta ba all through d night baibar yarinyar nan tai bacci ba ya wahalar da uta yana zuwa masallaci bai kara dawowa gidan ba sai after one na rana, he put her in pains and he was never there for her, yadawo still he was not there for her not even to come yadubata saida yayi settling Saleem tukunna, da daddare yazo he just lallasheta for few minutes yafara more jikinta and half way ya barta an kirasa cikinta na ciwo he heard yanda matarsa ke kuka but baizoha sai bayan 30min, did he ever think inda ace emergency ne and baizoba inda ta mutu fa? Ya tambayi kansa kirjinsa nawani kalan bugawa ya lumshe idanu again, wlh wlh baiyi ignoring matarsa intentionally ba he just found kansa in a situation that s so hard to explain mesa dalilin dayayi abinda yayi but duka yasan ba da gangan bane Saleem is seriously sick yayi zaiyi?. KUN YARDA DA HUKUNCIN DA MAMI TA YANKE??? DO YOU THINK MAMI IS SELFISH?? SAINAKE GA KAMAN MAMI BATASON SALEEM KO JAMA SO TAKE YADENA KULA DA SALEEM YAKULA DA MATARSA?? MAISA MAMI KESON MARWAN YAFITAR MATA DA SALEEM DAGA GIDA??? KUNA GANIN HAKAN YAYI DAIDAI? EPISODE 7 Da kyar bacci yadeba Marwan sabida damuwa da tunani daya shiga dalilin maganganun Mami. Ana kiran salla asuba yabude idanunsa, bayin dakin yashiga yayi wanka tsaf yafito da towel ajikinsa saiya fito yabude kofa yashiga dakinsa yana kallon Saleem dake bacci sosai, kaya yashiga closet nasa yasaka, t-shirt baka da jean ya feffesa turare yana kamshi sosai saiya fito yawuce wajen gadon yakai hannunsa yataba kan Saleem, baya running temperature at all, ijiyan zuciya yasauke saiya juyo yafito daga dakin
Chapter 65 · 0% Book details