Sashe 69
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wani abu ake a Jos d'in?" Hajiya ce ta katseshi da wannan tambayar,
"Eh akwai wani Yayana acan babban malamin tsangaya ne,ana tura mashi kangararrun yara ba kamar masu irin halin Ashirun wato masu yin shaye shaye da kuma sata kuma akan dace su shiryu,da farko lokacin da ya jefa rayuwarshi cikin wannan halin nayi tunanin zan iya gyarashi amman ina,ganin abun nashi yana yin gaba ne yasa nayi ma yayan nawa magana akanshi yace in kaishi can,wllh banfi sati guda da kaishi ba sai gashi ya gudo,bayan wani lokaci na sake d'aukarshi na maidashi amman sai ya sake guduwa kuma abunda ya tada man hankali shine da ya gudun ba nan gida ya dawo ba gaba yayi bamu san inda ya nufa ba,hankalinmu ya matukar tashi don ba irin neman da bamu yi mashi ba amman shiru ba labarinshi,haka muka hakura kuma muka dukufa da yin Addu'ar Allah ya bayyana shi kwatsam, wata rana sai gashi kamar an jefo shi,nayi Matuk'ar farincikin dawowarsa duk da canjin dana gani atattare dashi,wai ashe lagos ya tafi bayan ya gudun,to tun dagananne na hak'ura da turashi jos d'in duk da halin nashi saima abunda yayi gaba bayan yaje lagos d'in", sauke ajiyar zuciya suka yi gaba dayansu,
"Yanzu mi kake bukata a wurina ne?" Haisam ne ya yi Maganar,shiru yayi ya d'an sadda kanshi k'asa kafin ya d'ago yace"idan zai yuwu ina neman alfarmar ayi mashi duk hukuncin da ya dace amman don Allah kar akaishi kotu don daga can ne za'a iya tura su gidan yari,na dad'e ina mashi Addu'ar shiriya watakil lokacinne yayi don tabbas naga nadama a idanuwanshi kuma sanin basu kaiga aikata laifin bane yasa nayi karfin halin zuwa nema mashi wannan Alfarmar,wallahi tallahi kaji arantse da ace yau sun aikata laifin koda shi Ashirun bai yin ba bazan ta6a nema masa sassauci ba duk kuwa yadda raina zai sosu zan bada goyon baya d'ari bisa d'ari akan ayanke masa hukunci",
Jin ya dakata yasa Haisam fara Magana"at first munso ayi masu afuwa ne tunda basu kaiga aikatawa ba so bayan munje can da Yarinyar ne kuma ta kawo wani issue wanda yasa dole aka fasa yi masu afuwan da akai niyya bansan ko kasamu labarin hakan ba",da d'an rud'u Malam tanimu ya girgiza mashi kai"bansan wani abu ba bayan abunda ake tuhumarsu dashi,dayake tunda aka kamasu ni banje ba sai yau,yan uwansa dae na zuwa Mahaifiyarsa ma taje",jinjina kai Haisam yayi nan take ya fad'i masa dalilin da yasa aka fasa yi masu afuwar,cike da tashin hankali ya saka salati yana tafa hannuwa,a razane, a kuma firgice yace"Wllh sam bansan hakan abun yake ba da ban fara ma zuwa nema masa afuwa ba,ashe rashin hankalin Ashiru har yakai haka,yanzu ace saboda kayan maye zai goyi bayan wannan aika aikar da suka so yi ba don Allah ya takaita Al'amarin ba",lokaci guda idanunsa suka cuccuko tab da kwalla,girgiza kai hajiya tayi cike da takaici ta fara magana"nima dai na Matuk'ar girgiza wllh da jin hakan,sam Ashiru bai yi man wayo ba,yadda bai goyi baya ba tun farko kamata yayi jin wannan Mummunar niyyar tasu yasashi bujire masu ta hanyar tona masu asiri amman ina,saboda tsabar rashin hankali ya za6i ya jefa kanshi cikin matsala ta hanyar goya masu baya duk da yasan mummunan kudirinsu ",
"Ai Hajiya ni yanzu ma wllh na cire hannuna daga lamarinshi daman rashin sani ne,duk hukuncin da ya dace ai mashi ai mashi kawae shi ya ja ma kanshi" yana kai Maganar kwallan daya taru suka zubo mashi sharrr ya sunkuyar da kan k'asa,
Sigh Haisam yayi gently yace"We should thank Allah da bai basu nasarar aikatawa ba gaba daya,lamarin zai fi zuwa da sauki,in sha Allah zanyi ma wanda case din ke ahannunsu Magana za'a duba ayi abunda zai yuwu",
Hajiya ce ta shiga bashi baki tana cewa kar yasa damuwa aranshi yaci gaba da yi mashi Addu'a kawae don ita kadai ce magani inda rabon shiryuwa wataran komae zai zamo tarihi.
Mik'ewa Haisam yayi ya kalli Hajiya"is that all?"ya tambayeta,kallon Malam tanimu dake ta matsar kwalla tayi tace"Malam ko akwae wani abu?"da sauri ya girgiza mata kai"Babu komae hajiya Nagode kwarae,Allah ya k'ara girma",jin hakan yasa Haisam yi mashi sallama ya nufi hanyar fita daga falon don duk a takure yake bazai ta6a samun natsuwa ba har sai yaji saukar ruwa ajikinsa,d'an k'ara tattaunawa sukai kan halin da yara matasa ke jefa rayuwarsu daga bisani Malam Tanimun yayi mata sallama ya tafi.
____________
Washegari da Safe misalin k'arfe 7:30 Fatuu ta fito kopar gida jikinta sanye da kayan makaranta,tsaye tayi gefen kiosk d'in Amadu tana d'an tunanin ko Ya Handsome ya wuce,zuciyarta ce ta raya mata wani abu hakan yasa ta mik'i hanyar zuwa gidan Hajiya,tana karya kwanar Gate aka zuge gate d'in,tsaye tayi tana kallon Motar da ta fito wadda suka je Police Station da itace,adaidai inda take tsaye Motar ta tsaya glass d'in ya fara sauka ahankali tana had'a idanu da Haisam ta sakar mashi Murmushi,shima murmushin ya maida mata yana sanye cikin Suit Ash and black colour,alamar ta shigo yayi mata da kai hakan yasa takai hannu da sauri ta bud'e Motar ta shiga,rufe glass d'in yayi bayan ta rufe kopar,daga haka yaja Motar suka fara tafiya,
"Gud Morning Ya Handsome",fuskarshi asake yace" Morning,how a'r u",
"I'm fine" ta bashi amsa,jinjina kai yayi ba tare da ya k'ara cewa kamae ba,
"Ya Handsome ashe kasan Principal d'inmu?" kai ya d'aga mata alamar eh,
"Ashe shiyasa kasan Makarantar da nike"nan ma kai ya d'aga mata,ganin sun wuce kwanar gidansu Haulat yasata sakin salati "kai innalillahi...."kallonta yayi yace"What?",
"Wllh jiya mantawa nayi ban biya ma kawata Haulatu ba hakan yasata ta makara aka tareta,ranta ya 6aci har tana ceman wai tunda an kawo ni a Mota sanyin Ac ya ratsa ni ai dole in manta da ita",
d'an bud'a idanu yayi yace"baki kyauta ba" turo baki tayi cike da shagwa6a"to ai mantawa nayi ko,kowa ba yana yin mantuwa ba",d'an ta6e lips d'insa yayi sai kuma yace"to yau sai ki biya matan ko",
"To ai saidae ka aje ni sai inje in biya mata mu hau Bus" kallonta ya d'anyi "Why,ko wannan ba Mota bane?",
langa6ar da kai tayi idonta akanshi"to ai kai naga baka son ana zauna maka a bayan mota to kuma in tazo ita a ina zata zauna?"d'age mata gira yayi yace"mukai dake ba'a zauna man a bayan Mota?"
zaro ido tayi cike da mamaki"to amman jiya dana zauna ba k'in tafiya kayi ba kace sai na zauna a inda ya dace ka nuna man gaba",
"Yea,ai ni ba Driver dinki bane da zaki zauna a baya kuma gaban ba kowa" bud'a baki tayi alamar mamaki"wai dama saboda hakan ne kace in dawo gaba?'kai ya d'aga mata kafin yace"ina ne gidansu Friend d'in naki?",
"To ai mun fa wuce kwanar tana baya" gyad'a kai yayi ya fara k'okarin juya motar,kallonta yayi bayan ya juya"shi center d'in nasu yana fita titi ne?"
"Eh,amman fa bansan ko Wannan k'atuwar motar zata wuce ba don lungun nasu d'an tsukuku ne,yauwa ga lungun nan" takai Maganar tana nuna masa lungun da yatsanta,kallon lungun yayi nan take ya fahimci motan zata iya wucewa hakan yasashi kutsawa ciki,suna zuwa daidai gidansu Haulat tace "wait, wait ga gidan nan",tayi Maganar tana nuna gidan,ganin tana k'okarin fita yace"ki bari ayi mata horn mana ta fito",da sauri ta kalleshi ido waje"Haulatun za'ai ma horn,ita da ba mota garesu ba taya zata gane ita ake kira bari dae inje in kirata" yadda tayi Maganar sai kace ita Motar garesu,tana shiga cikin zauren gidan suka kusan cin karo da ita ta taho tana sanya hijabin Makaranta,tana ganin fatuu tace"ai na zata yauma a Motar aka daukeki kin manta dani..."da sauri Fatuu tasa hannu ta rufe mata baki,
"Dalla kiyi shiru da Ya Handsome d'in fa muka zo" da mamaki Haulat ta d'an bud'a idanunta"bangane ba?",
"Shi d'an gidan hajiyan nike nufi gashi nan kopar gidanku shi yace in kirawo ki zai kaimu Makarantar" zaro ido Haulat tayi ta kasa magana,ita kam Fatuu hannu takai tana gyara mata wuyan hijab d'inta da ya jirkice ta goge mata maikon kosai data gama ci agefen bakin,
"Ki taho mutafi kada yayi ta jiranmu,amman fa kada kiyi mashi hauka ko kauyanci da kin shiga motan ki gaidashi sai kija bakinki kiyi shuru don shi baison Surutu" daga haka tayi gaba Haulat da tayi sototo tana saurarenta tabi bayanta,har zata fita ta juyo da sauri"ki saka wannan jakar ledan taki cikin hijab ki 6oyeta har muje class don kauyanci ne ki shiga wannan had'addar Motar da Jakar leda",kai kawai ta gyad'a mata tayi yadda tace daga haka suka fita,nuna mata kopar baya Fatuu tayi tace"ki bud'e ta ki shiga,in baki iya ba in bud'e maki kuma in kin shiga ki kulle da karfi don kar taki rufuwa" d'an Murmushi kawai Haulat tayi takai hannu taja Door handle d'in sai gashi kopar ta bud'e fatuu na ganin ta shiga itama ta bud'e gaban ta shige,
"Ya Handsome gata nan na kirata" kai ya d'aga mata yana k'okarin jan motan Haulat data kame kanta agefe guda tace"ina kwana",kai kawae ya jinjina mata daga haka suka tafi,tunda suka hau hanya Fatuu keta faman zuba kaman burkakkar radio,cike da mamaki haulat ke kallonta ita data gama mata hud'ubar taja bakinta tayi shiru baison surutu amman ita ji yadda ta cika su da surutun,ita dai saidai ta d'an girgiza kai kawae kai kace bata acikin Motar ma.
"Eh akwai wani Yayana acan babban malamin tsangaya ne,ana tura mashi kangararrun yara ba kamar masu irin halin Ashirun wato masu yin shaye shaye da kuma sata kuma akan dace su shiryu,da farko lokacin da ya jefa rayuwarshi cikin wannan halin nayi tunanin zan iya gyarashi amman ina,ganin abun nashi yana yin gaba ne yasa nayi ma yayan nawa magana akanshi yace in kaishi can,wllh banfi sati guda da kaishi ba sai gashi ya gudo,bayan wani lokaci na sake d'aukarshi na maidashi amman sai ya sake guduwa kuma abunda ya tada man hankali shine da ya gudun ba nan gida ya dawo ba gaba yayi bamu san inda ya nufa ba,hankalinmu ya matukar tashi don ba irin neman da bamu yi mashi ba amman shiru ba labarinshi,haka muka hakura kuma muka dukufa da yin Addu'ar Allah ya bayyana shi kwatsam, wata rana sai gashi kamar an jefo shi,nayi Matuk'ar farincikin dawowarsa duk da canjin dana gani atattare dashi,wai ashe lagos ya tafi bayan ya gudun,to tun dagananne na hak'ura da turashi jos d'in duk da halin nashi saima abunda yayi gaba bayan yaje lagos d'in", sauke ajiyar zuciya suka yi gaba dayansu,
"Yanzu mi kake bukata a wurina ne?" Haisam ne ya yi Maganar,shiru yayi ya d'an sadda kanshi k'asa kafin ya d'ago yace"idan zai yuwu ina neman alfarmar ayi mashi duk hukuncin da ya dace amman don Allah kar akaishi kotu don daga can ne za'a iya tura su gidan yari,na dad'e ina mashi Addu'ar shiriya watakil lokacinne yayi don tabbas naga nadama a idanuwanshi kuma sanin basu kaiga aikata laifin bane yasa nayi karfin halin zuwa nema mashi wannan Alfarmar,wallahi tallahi kaji arantse da ace yau sun aikata laifin koda shi Ashirun bai yin ba bazan ta6a nema masa sassauci ba duk kuwa yadda raina zai sosu zan bada goyon baya d'ari bisa d'ari akan ayanke masa hukunci",
Jin ya dakata yasa Haisam fara Magana"at first munso ayi masu afuwa ne tunda basu kaiga aikatawa ba so bayan munje can da Yarinyar ne kuma ta kawo wani issue wanda yasa dole aka fasa yi masu afuwan da akai niyya bansan ko kasamu labarin hakan ba",da d'an rud'u Malam tanimu ya girgiza mashi kai"bansan wani abu ba bayan abunda ake tuhumarsu dashi,dayake tunda aka kamasu ni banje ba sai yau,yan uwansa dae na zuwa Mahaifiyarsa ma taje",jinjina kai Haisam yayi nan take ya fad'i masa dalilin da yasa aka fasa yi masu afuwar,cike da tashin hankali ya saka salati yana tafa hannuwa,a razane, a kuma firgice yace"Wllh sam bansan hakan abun yake ba da ban fara ma zuwa nema masa afuwa ba,ashe rashin hankalin Ashiru har yakai haka,yanzu ace saboda kayan maye zai goyi bayan wannan aika aikar da suka so yi ba don Allah ya takaita Al'amarin ba",lokaci guda idanunsa suka cuccuko tab da kwalla,girgiza kai hajiya tayi cike da takaici ta fara magana"nima dai na Matuk'ar girgiza wllh da jin hakan,sam Ashiru bai yi man wayo ba,yadda bai goyi baya ba tun farko kamata yayi jin wannan Mummunar niyyar tasu yasashi bujire masu ta hanyar tona masu asiri amman ina,saboda tsabar rashin hankali ya za6i ya jefa kanshi cikin matsala ta hanyar goya masu baya duk da yasan mummunan kudirinsu ",
"Ai Hajiya ni yanzu ma wllh na cire hannuna daga lamarinshi daman rashin sani ne,duk hukuncin da ya dace ai mashi ai mashi kawae shi ya ja ma kanshi" yana kai Maganar kwallan daya taru suka zubo mashi sharrr ya sunkuyar da kan k'asa,
Sigh Haisam yayi gently yace"We should thank Allah da bai basu nasarar aikatawa ba gaba daya,lamarin zai fi zuwa da sauki,in sha Allah zanyi ma wanda case din ke ahannunsu Magana za'a duba ayi abunda zai yuwu",
Hajiya ce ta shiga bashi baki tana cewa kar yasa damuwa aranshi yaci gaba da yi mashi Addu'a kawae don ita kadai ce magani inda rabon shiryuwa wataran komae zai zamo tarihi.
Mik'ewa Haisam yayi ya kalli Hajiya"is that all?"ya tambayeta,kallon Malam tanimu dake ta matsar kwalla tayi tace"Malam ko akwae wani abu?"da sauri ya girgiza mata kai"Babu komae hajiya Nagode kwarae,Allah ya k'ara girma",jin hakan yasa Haisam yi mashi sallama ya nufi hanyar fita daga falon don duk a takure yake bazai ta6a samun natsuwa ba har sai yaji saukar ruwa ajikinsa,d'an k'ara tattaunawa sukai kan halin da yara matasa ke jefa rayuwarsu daga bisani Malam Tanimun yayi mata sallama ya tafi.
____________
Washegari da Safe misalin k'arfe 7:30 Fatuu ta fito kopar gida jikinta sanye da kayan makaranta,tsaye tayi gefen kiosk d'in Amadu tana d'an tunanin ko Ya Handsome ya wuce,zuciyarta ce ta raya mata wani abu hakan yasa ta mik'i hanyar zuwa gidan Hajiya,tana karya kwanar Gate aka zuge gate d'in,tsaye tayi tana kallon Motar da ta fito wadda suka je Police Station da itace,adaidai inda take tsaye Motar ta tsaya glass d'in ya fara sauka ahankali tana had'a idanu da Haisam ta sakar mashi Murmushi,shima murmushin ya maida mata yana sanye cikin Suit Ash and black colour,alamar ta shigo yayi mata da kai hakan yasa takai hannu da sauri ta bud'e Motar ta shiga,rufe glass d'in yayi bayan ta rufe kopar,daga haka yaja Motar suka fara tafiya,
"Gud Morning Ya Handsome",fuskarshi asake yace" Morning,how a'r u",
"I'm fine" ta bashi amsa,jinjina kai yayi ba tare da ya k'ara cewa kamae ba,
"Ya Handsome ashe kasan Principal d'inmu?" kai ya d'aga mata alamar eh,
"Ashe shiyasa kasan Makarantar da nike"nan ma kai ya d'aga mata,ganin sun wuce kwanar gidansu Haulat yasata sakin salati "kai innalillahi...."kallonta yayi yace"What?",
"Wllh jiya mantawa nayi ban biya ma kawata Haulatu ba hakan yasata ta makara aka tareta,ranta ya 6aci har tana ceman wai tunda an kawo ni a Mota sanyin Ac ya ratsa ni ai dole in manta da ita",
d'an bud'a idanu yayi yace"baki kyauta ba" turo baki tayi cike da shagwa6a"to ai mantawa nayi ko,kowa ba yana yin mantuwa ba",d'an ta6e lips d'insa yayi sai kuma yace"to yau sai ki biya matan ko",
"To ai saidae ka aje ni sai inje in biya mata mu hau Bus" kallonta ya d'anyi "Why,ko wannan ba Mota bane?",
langa6ar da kai tayi idonta akanshi"to ai kai naga baka son ana zauna maka a bayan mota to kuma in tazo ita a ina zata zauna?"d'age mata gira yayi yace"mukai dake ba'a zauna man a bayan Mota?"
zaro ido tayi cike da mamaki"to amman jiya dana zauna ba k'in tafiya kayi ba kace sai na zauna a inda ya dace ka nuna man gaba",
"Yea,ai ni ba Driver dinki bane da zaki zauna a baya kuma gaban ba kowa" bud'a baki tayi alamar mamaki"wai dama saboda hakan ne kace in dawo gaba?'kai ya d'aga mata kafin yace"ina ne gidansu Friend d'in naki?",
"To ai mun fa wuce kwanar tana baya" gyad'a kai yayi ya fara k'okarin juya motar,kallonta yayi bayan ya juya"shi center d'in nasu yana fita titi ne?"
"Eh,amman fa bansan ko Wannan k'atuwar motar zata wuce ba don lungun nasu d'an tsukuku ne,yauwa ga lungun nan" takai Maganar tana nuna masa lungun da yatsanta,kallon lungun yayi nan take ya fahimci motan zata iya wucewa hakan yasashi kutsawa ciki,suna zuwa daidai gidansu Haulat tace "wait, wait ga gidan nan",tayi Maganar tana nuna gidan,ganin tana k'okarin fita yace"ki bari ayi mata horn mana ta fito",da sauri ta kalleshi ido waje"Haulatun za'ai ma horn,ita da ba mota garesu ba taya zata gane ita ake kira bari dae inje in kirata" yadda tayi Maganar sai kace ita Motar garesu,tana shiga cikin zauren gidan suka kusan cin karo da ita ta taho tana sanya hijabin Makaranta,tana ganin fatuu tace"ai na zata yauma a Motar aka daukeki kin manta dani..."da sauri Fatuu tasa hannu ta rufe mata baki,
"Dalla kiyi shiru da Ya Handsome d'in fa muka zo" da mamaki Haulat ta d'an bud'a idanunta"bangane ba?",
"Shi d'an gidan hajiyan nike nufi gashi nan kopar gidanku shi yace in kirawo ki zai kaimu Makarantar" zaro ido Haulat tayi ta kasa magana,ita kam Fatuu hannu takai tana gyara mata wuyan hijab d'inta da ya jirkice ta goge mata maikon kosai data gama ci agefen bakin,
"Ki taho mutafi kada yayi ta jiranmu,amman fa kada kiyi mashi hauka ko kauyanci da kin shiga motan ki gaidashi sai kija bakinki kiyi shuru don shi baison Surutu" daga haka tayi gaba Haulat da tayi sototo tana saurarenta tabi bayanta,har zata fita ta juyo da sauri"ki saka wannan jakar ledan taki cikin hijab ki 6oyeta har muje class don kauyanci ne ki shiga wannan had'addar Motar da Jakar leda",kai kawai ta gyad'a mata tayi yadda tace daga haka suka fita,nuna mata kopar baya Fatuu tayi tace"ki bud'e ta ki shiga,in baki iya ba in bud'e maki kuma in kin shiga ki kulle da karfi don kar taki rufuwa" d'an Murmushi kawai Haulat tayi takai hannu taja Door handle d'in sai gashi kopar ta bud'e fatuu na ganin ta shiga itama ta bud'e gaban ta shige,
"Ya Handsome gata nan na kirata" kai ya d'aga mata yana k'okarin jan motan Haulat data kame kanta agefe guda tace"ina kwana",kai kawae ya jinjina mata daga haka suka tafi,tunda suka hau hanya Fatuu keta faman zuba kaman burkakkar radio,cike da mamaki haulat ke kallonta ita data gama mata hud'ubar taja bakinta tayi shiru baison surutu amman ita ji yadda ta cika su da surutun,ita dai saidai ta d'an girgiza kai kawae kai kace bata acikin Motar ma.