Sashe 62
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin da ta shiga cike da Murna ta fad'a saman gadonta,da duk damuwa ta hana tayi murnar,sai faman Murmushi take saki,zazzage kayan tayi saman gadon tana sake dubawa,sai faman sambatu take tana yaba kirkin haisam,saukkowa tayi ta fara kokarin gwada rigunan,ba k'aramin kyau suka yi mata ba,sun hau da fatarta sosae gashi duk sunyi mata daidai sai kace ya gwada mata ne kafin ya za6ar mata,guda d'aya ce bak'ar ta d'an so yi mata yawa itama ba sosae ba,data sa takalmi mai tudu zatayi mata daidai kuma ita ta yanke shawarar bari sai sallah don ta had'u sosae har wani d'aukan ido take,duk wadda tasa sai taje ta nuna ma gwaggo,cike da farinciki gwaggon ke yabawa don ba karamin dad'in kayan taji ba,kowa na jin dadi in yaga anyi ma nasa,ba kamar fatuu yar lelenta,
**** **** ****
Ranar Lahadi Misalin k'arfe ukku na rana haisam ya shigo cikin parlon Hajiya bakinshi dauke da sallama,hajiya dake zaune saman 3-seater ta d'an kishingid'a idanunta sanye cikin gilashi ta amsa mashi, juyawa tayi tana kallonshi har ya k'araso,agefenta ya zauna yana mata murmushi,itama murmushin take mayar masa,
"Yau ba aikin latse latsenne naga ka fito"d'an kwantar da kanshi yayi"yea,ai gobe zanje Office",
"Haka fa tunda kasamu sauki,Allah ya tsare gaba",can k'asan makwoshinshi ya amsa "Amin",
shuru sukayi na d'an lokaci,to break the silence hajiya tace"ko akawo ma wani abu ka dan ta6a?",
d'age mata gira yayi"not too long naci fa abinci",
"Eh ai dama ba abincin nike nufi ba d'an abu mara nauyi haka da zaka d'an tauna",lumshe mata ido yayi nan take ta gane abunda yake nufi,Saude ta kwala ma kira ta bata umarnin kawo abun da zasu dan tauna,bada jimawa ba ta kawo masu meatballs cikin plate da fork hajiya ta amsa,tana k'okarin kinkimo sofa table hajiya ta dakatar da ita tace taje kawae,a tsakiyansu ta aje plate d'in tace mashi gashi nan ya ci,kai ya d'aga mata kafin yasa fork ya dau d'aya ya d'an gutsira yana chewing a hankali yana kallon Tv,itama hajiyar d'auka ta fara tana ci suna d'an yin fira,can ta kai hannu cikin sumar kanshi ta nutsa shi ciki"wai wannan sumar ba'a aske ta ne tayi tsawo da yawa,koda yake dole ai tayi tsawon tunda kud'i ake kashe mata,don ma a nad'e take wannan da ba k'aramin tsawo kitso zai yi ba in akayi maka",
Wani kallo yayi mata da d'an murmushi"ko zaki man kitson ne",
"In kana so ai sai in maka, kasan k'aramin aikina ne,sai dae ba lalle ma kitson ya tsaya akan wannan sumar ba ta cika santsi",ta k'arasa maganar har lokacin hannunta na acikin sumar tana d'an sosa mashi kan,shi dae murmushi kawae yake don abunda take mashin dama ta saba tun yana k'arami haka zata sa hannu cikin sumarshi tana sosa mashi,ba kamar in ranshi ya 6aci ko yayi fushi a haka take rarrashinshi,
cire hannun tayi tace"ya kamata a rik'a rage maka ita, kaima kasha iska",
Sigh yayi"ai ana rage shi,shiyasa kike ganinshi haka da yafi hakan sosae",
jinjina kai tayi suka ci gaba da cin abunda ke gabansu sai dae ita shi yake bata a baki idonta akan tv,
"Motan ki da kika ce zaki bada waye zaki ba?",
maido idonta tayi kanshi"wani abu?,
girgiza mata kai yayi"i just want know in akwae wanda zaki ba",
"Eh,kawunku Mani nike son ba,don kwanaki da suka zo naga tashi ta fara tsufa dama tun wadda Senator ya basu ce,ko za kai wani abu da ita ne?"idasa cinye abunda ke bakinsa yayi kafin yace"No,ki bashi kawae,i thought baki fidda wanda zaki ba bane,da zan ba Abbas ne,amman zansa akawo mashi wani,
"to ka bashin kawae,ai shima d'an gidane wani lokaci aba Manin" lumshe ido yayi yana d'an girgiza kai alamar a'a,shiru tayi tana kallonshi,tasan tunda ta ambaci wanda zata ba,zai yi wuya yayi amfani da ita,
"To ba ni nace ka bashi ba"
"Ki ba wanda kikai niyya rabonshi ne,za'a kawo ma Abbas d'in period",daga haka ya aje fork d'in asaman plate alamar ya k'oshi ya maida kanshi saitin tv,itama hajiyar kallon taci gaba da yi,
"to mi zai hana ka kira Nameer,nasan baza'a rasa motan da basu amfani da ita acan Abujan ba tunda wasu aje suke kawae kaga sai ka tambayeshi in akwae lafiyayya sai aba Abbas d'in kawae",kai ya d'aga mata
alamar toh batare da ya kalleta ba,ta kuma cewa"ko ni in kirashi kawae don nasan ma ba lalle ka kirashin ba",
"Ba sai kin kira ba,zanyi abunda ya kamata",d'an ta6e baki tayi suka ci gaba da yin kallon,
"Wai nikam Fateema ko Lafiya,jiya fa banga tazo gidan nan ba,yau ma gashi har yamma,ko tazo wurinka?"hajiya tayi maganar idonta akan haisam,girgiza mata kai yayi"tun Friday da nayi dropping nata ban k'ara ganinta ba",
"To Allah yasa dae lpy,don in lafiya lafiya baka k'i ganinta agidan nan ba,ba kamar ma weekend",shi dae shiru yayi baice mata komai ba,
can tace"kai bari dai in kira Dijen muji lafiya",juyawa tayi ta d'aukko wayarta akan hannun kujera ta fara k'okarin kiran Gwaggo,tana fara ringing ta d'auka,bayan sun gaisa take tambayarta lafiya bata ga Mutuniyarta ba cikin weekend d'innan,anan gwaggon ke sanar da ita cewa bata lafiya ne tun ranar Juma'a da zazza6i ta kwana,jiya jikin ya d'an yi tsanani don har sai da aka mata allura amman zuwa yau ta samu sauki sosae,salati hajiya tayi tace ai bata sani ba,tace agaida mata ita sai ta shigo dubata in Allah ya yarda,Gwaggon nace mata ai ba sai tazo ba tunda da sauk'i sosae a haka suka yi Sallama,cire wayar tayi daga kunnanta idonta akan haisam da tunda ta saki salati ya juyo yana kallonta,tace"kaji ashe wai bata lpy tun ranar juma'a da zazza6i ta kwana jiya jikin yayi tsanani har saida aka mata allura,amman dai tace da sauki",
"Allah ya bata lafiya",yace still idanunsa akanta,
hajiya taci gaba"aikam zuwa dubiya ya kama ni,ance wai ka gaida mai gaidaka,sam Fateema bata da kyaliya,kar kaso kaga yadda take tashin hankalinta in ban jin dadi,wani ciwo da nayi kwanaki tasani gaba tayi tana kuka wai bata so in Mutu"takai maganar tana dariya,shima d'an Murmushi yayi bai dai ce mata komae ba,
"Ko zaka je ka dubata ne,kaga ma sai ku gaisa da Gwaggonta don ta sanka sosai,kaima nasan zaka santa,matar akwai kirki wllh",shiru ya d'an yi,hajiya ta bishi da ido can ya furta"Ok",
"Yauwa,ka gano ya jikin nata,ko zuwa da daddare ne sai in lek'a",jinjina mata kai yayi daga haka ya mik'e,hajiya tace"in can d'in zaka ko Saude ta zuba abinci ka tafin mata dashi?" Wani kallo ya jefa ma hajiyan kaman harara"ni zaki aika da abinci",
dariya tayi"wai ai naga kaima da baka lpy ta kawo maka abun dubiya ko",
"Ba can zani ba yanzu sai after asr,in zaki bada abu akai mata ki bada"daga haka ya nufi hanyar fita hajiya nata dariya dama tsokana ce kawae tasan bazai ta6a daukar warmer din abinci ba da sunan zuwa dubiya,
Yana isa part d'inshi ya fad'a toilet don yin wanka,after some minutes ya fito jikinsa sanye da Bathrobe ya nufi Closet dinshi,within few minutes ya shirya cikin Red polo shirt da farin Jeans itama rigar daga cikin collar dinta fari ne sai faman sakin daddad'an kamshi yake,a corridor ya tsaya yasa fararen takalma,Masha Allah shigar Red and White nasan ba sai na fad'i kyan da yayi cikin kayan ba,a parlor ya d'au wayarsa da ya aje lokacin da ya shigo daga haka ya nufi Masallaci da aka gama kiran sallan la'asar.
Yana fitowa daga masallacin bayan an gama sallan ya nufi gidansu Fatuu,a bakin shagon Amadu ya tsaya shima bai dad'e da ya dawo daga sallar ba,yana ganin haisam d'in ya shiga washe baki yana gaidashi,hannu ya mik'a masa suka gaisa,cikin cool voice d'inshi yace mashi ya shiga ya sanar yazo duba Zarah ne,da sauri ya amsa mashi da toh kafin ya nufi cikin gidan,bai jima ba ya fito yace mashi ya shigo,atare suka shiga Amadu na gaba shi kuma yana binsa a nutse yake yin tafiyar har suka shiga ciki,suna shiga gwaggo dake abakin kopar d'akinta ta tarbeshi da fara'a"Maraba da d'ana Haisam",fuska a sake ya amsa mata nan take kuma ya ga ya santa da Hajiya,gashi ma har ta kirashi da d'anta,cikin d'akin tace mashi ya shigo wanda ke d'auke da gado six by six da wardrobe d'inshi mai gida biyu da d'an k'aramin Dressing Mirror sai kujera two seater da kuma one seater, d'akin sai k'amshin incense stick da aka kunna ke tashi,a bakin kopar d'akin ya cire takalmansa ya shiga da yar sallama,fuskar gwaggo da fara'a ta nuna masa kujera don ya zauna,bayan ya zauna ita kuma ta koma bakin gadon ta zauna,cikin muryarsa mai sanyi ya fara gaisar da ita ta amsa,shiru ya d'an yi can kuma ya d'ago don tunda ya shigo kanshi na a k'asa,
"Ya mai jiki",
"Ah maijiki da sauk'i sosae,oni Hajiya sai da ta taso ka ai nace mata ta samu sauki da bata wahalar da kai ba wllh", shi dai shiru yayi idonshi na kan floor d'in dakin,ita kam gwaggo idonta na akanshi bata ta6a tunanin zai zo gidan ba don iyakarta dashi su gaisa ne in yazo gidan hajiya,
can tace"Mun ga d'awainiyar abun Arziki,inata son inzo in yi godiya wllh jikin nata ne ya hana,don jiya gaba d'aya bansamu na fita bama saboda jikin nata,yau nike niyyar in shigo da daddare sai kuma ga ka,da nasan zaka zo ai da tunda safe na shigo"fuskarta d'auke da fara'a take yin maganar,
d'an guntun Murmushi yayi ba tare da ya kalleta ba yace"ba wani abu ai",
Godiya ta shiga yi mashi sosae tana shi mashi Albarka,tun yana amsawa kasa kasa har dae yayi shiru yana ci gaba da amsawa acikin ransa,tana cikin yin godiyar Amadu ya shigo dauke da plate ya d'auro ruwa pure water da yan k'ananun robobin lemu guda biyu don irinsu kawae yake saidawa saboda yan makaranta don ba freezer gareshi ba a shagon,a gaban haisam ya aje ya k'ara gaidashi kafin ya fita,shiru sukayi na d'an wani lokaci don Mutumin ba gwanin yin fira bane ba kaman kuma a inda yake bak'o,
**** **** ****
Ranar Lahadi Misalin k'arfe ukku na rana haisam ya shigo cikin parlon Hajiya bakinshi dauke da sallama,hajiya dake zaune saman 3-seater ta d'an kishingid'a idanunta sanye cikin gilashi ta amsa mashi, juyawa tayi tana kallonshi har ya k'araso,agefenta ya zauna yana mata murmushi,itama murmushin take mayar masa,
"Yau ba aikin latse latsenne naga ka fito"d'an kwantar da kanshi yayi"yea,ai gobe zanje Office",
"Haka fa tunda kasamu sauki,Allah ya tsare gaba",can k'asan makwoshinshi ya amsa "Amin",
shuru sukayi na d'an lokaci,to break the silence hajiya tace"ko akawo ma wani abu ka dan ta6a?",
d'age mata gira yayi"not too long naci fa abinci",
"Eh ai dama ba abincin nike nufi ba d'an abu mara nauyi haka da zaka d'an tauna",lumshe mata ido yayi nan take ta gane abunda yake nufi,Saude ta kwala ma kira ta bata umarnin kawo abun da zasu dan tauna,bada jimawa ba ta kawo masu meatballs cikin plate da fork hajiya ta amsa,tana k'okarin kinkimo sofa table hajiya ta dakatar da ita tace taje kawae,a tsakiyansu ta aje plate d'in tace mashi gashi nan ya ci,kai ya d'aga mata kafin yasa fork ya dau d'aya ya d'an gutsira yana chewing a hankali yana kallon Tv,itama hajiyar d'auka ta fara tana ci suna d'an yin fira,can ta kai hannu cikin sumar kanshi ta nutsa shi ciki"wai wannan sumar ba'a aske ta ne tayi tsawo da yawa,koda yake dole ai tayi tsawon tunda kud'i ake kashe mata,don ma a nad'e take wannan da ba k'aramin tsawo kitso zai yi ba in akayi maka",
Wani kallo yayi mata da d'an murmushi"ko zaki man kitson ne",
"In kana so ai sai in maka, kasan k'aramin aikina ne,sai dae ba lalle ma kitson ya tsaya akan wannan sumar ba ta cika santsi",ta k'arasa maganar har lokacin hannunta na acikin sumar tana d'an sosa mashi kan,shi dae murmushi kawae yake don abunda take mashin dama ta saba tun yana k'arami haka zata sa hannu cikin sumarshi tana sosa mashi,ba kamar in ranshi ya 6aci ko yayi fushi a haka take rarrashinshi,
cire hannun tayi tace"ya kamata a rik'a rage maka ita, kaima kasha iska",
Sigh yayi"ai ana rage shi,shiyasa kike ganinshi haka da yafi hakan sosae",
jinjina kai tayi suka ci gaba da cin abunda ke gabansu sai dae ita shi yake bata a baki idonta akan tv,
"Motan ki da kika ce zaki bada waye zaki ba?",
maido idonta tayi kanshi"wani abu?,
girgiza mata kai yayi"i just want know in akwae wanda zaki ba",
"Eh,kawunku Mani nike son ba,don kwanaki da suka zo naga tashi ta fara tsufa dama tun wadda Senator ya basu ce,ko za kai wani abu da ita ne?"idasa cinye abunda ke bakinsa yayi kafin yace"No,ki bashi kawae,i thought baki fidda wanda zaki ba bane,da zan ba Abbas ne,amman zansa akawo mashi wani,
"to ka bashin kawae,ai shima d'an gidane wani lokaci aba Manin" lumshe ido yayi yana d'an girgiza kai alamar a'a,shiru tayi tana kallonshi,tasan tunda ta ambaci wanda zata ba,zai yi wuya yayi amfani da ita,
"To ba ni nace ka bashi ba"
"Ki ba wanda kikai niyya rabonshi ne,za'a kawo ma Abbas d'in period",daga haka ya aje fork d'in asaman plate alamar ya k'oshi ya maida kanshi saitin tv,itama hajiyar kallon taci gaba da yi,
"to mi zai hana ka kira Nameer,nasan baza'a rasa motan da basu amfani da ita acan Abujan ba tunda wasu aje suke kawae kaga sai ka tambayeshi in akwae lafiyayya sai aba Abbas d'in kawae",kai ya d'aga mata
alamar toh batare da ya kalleta ba,ta kuma cewa"ko ni in kirashi kawae don nasan ma ba lalle ka kirashin ba",
"Ba sai kin kira ba,zanyi abunda ya kamata",d'an ta6e baki tayi suka ci gaba da yin kallon,
"Wai nikam Fateema ko Lafiya,jiya fa banga tazo gidan nan ba,yau ma gashi har yamma,ko tazo wurinka?"hajiya tayi maganar idonta akan haisam,girgiza mata kai yayi"tun Friday da nayi dropping nata ban k'ara ganinta ba",
"To Allah yasa dae lpy,don in lafiya lafiya baka k'i ganinta agidan nan ba,ba kamar ma weekend",shi dae shiru yayi baice mata komai ba,
can tace"kai bari dai in kira Dijen muji lafiya",juyawa tayi ta d'aukko wayarta akan hannun kujera ta fara k'okarin kiran Gwaggo,tana fara ringing ta d'auka,bayan sun gaisa take tambayarta lafiya bata ga Mutuniyarta ba cikin weekend d'innan,anan gwaggon ke sanar da ita cewa bata lafiya ne tun ranar Juma'a da zazza6i ta kwana,jiya jikin ya d'an yi tsanani don har sai da aka mata allura amman zuwa yau ta samu sauki sosae,salati hajiya tayi tace ai bata sani ba,tace agaida mata ita sai ta shigo dubata in Allah ya yarda,Gwaggon nace mata ai ba sai tazo ba tunda da sauk'i sosae a haka suka yi Sallama,cire wayar tayi daga kunnanta idonta akan haisam da tunda ta saki salati ya juyo yana kallonta,tace"kaji ashe wai bata lpy tun ranar juma'a da zazza6i ta kwana jiya jikin yayi tsanani har saida aka mata allura,amman dai tace da sauki",
"Allah ya bata lafiya",yace still idanunsa akanta,
hajiya taci gaba"aikam zuwa dubiya ya kama ni,ance wai ka gaida mai gaidaka,sam Fateema bata da kyaliya,kar kaso kaga yadda take tashin hankalinta in ban jin dadi,wani ciwo da nayi kwanaki tasani gaba tayi tana kuka wai bata so in Mutu"takai maganar tana dariya,shima d'an Murmushi yayi bai dai ce mata komae ba,
"Ko zaka je ka dubata ne,kaga ma sai ku gaisa da Gwaggonta don ta sanka sosai,kaima nasan zaka santa,matar akwai kirki wllh",shiru ya d'an yi,hajiya ta bishi da ido can ya furta"Ok",
"Yauwa,ka gano ya jikin nata,ko zuwa da daddare ne sai in lek'a",jinjina mata kai yayi daga haka ya mik'e,hajiya tace"in can d'in zaka ko Saude ta zuba abinci ka tafin mata dashi?" Wani kallo ya jefa ma hajiyan kaman harara"ni zaki aika da abinci",
dariya tayi"wai ai naga kaima da baka lpy ta kawo maka abun dubiya ko",
"Ba can zani ba yanzu sai after asr,in zaki bada abu akai mata ki bada"daga haka ya nufi hanyar fita hajiya nata dariya dama tsokana ce kawae tasan bazai ta6a daukar warmer din abinci ba da sunan zuwa dubiya,
Yana isa part d'inshi ya fad'a toilet don yin wanka,after some minutes ya fito jikinsa sanye da Bathrobe ya nufi Closet dinshi,within few minutes ya shirya cikin Red polo shirt da farin Jeans itama rigar daga cikin collar dinta fari ne sai faman sakin daddad'an kamshi yake,a corridor ya tsaya yasa fararen takalma,Masha Allah shigar Red and White nasan ba sai na fad'i kyan da yayi cikin kayan ba,a parlor ya d'au wayarsa da ya aje lokacin da ya shigo daga haka ya nufi Masallaci da aka gama kiran sallan la'asar.
Yana fitowa daga masallacin bayan an gama sallan ya nufi gidansu Fatuu,a bakin shagon Amadu ya tsaya shima bai dad'e da ya dawo daga sallar ba,yana ganin haisam d'in ya shiga washe baki yana gaidashi,hannu ya mik'a masa suka gaisa,cikin cool voice d'inshi yace mashi ya shiga ya sanar yazo duba Zarah ne,da sauri ya amsa mashi da toh kafin ya nufi cikin gidan,bai jima ba ya fito yace mashi ya shigo,atare suka shiga Amadu na gaba shi kuma yana binsa a nutse yake yin tafiyar har suka shiga ciki,suna shiga gwaggo dake abakin kopar d'akinta ta tarbeshi da fara'a"Maraba da d'ana Haisam",fuska a sake ya amsa mata nan take kuma ya ga ya santa da Hajiya,gashi ma har ta kirashi da d'anta,cikin d'akin tace mashi ya shigo wanda ke d'auke da gado six by six da wardrobe d'inshi mai gida biyu da d'an k'aramin Dressing Mirror sai kujera two seater da kuma one seater, d'akin sai k'amshin incense stick da aka kunna ke tashi,a bakin kopar d'akin ya cire takalmansa ya shiga da yar sallama,fuskar gwaggo da fara'a ta nuna masa kujera don ya zauna,bayan ya zauna ita kuma ta koma bakin gadon ta zauna,cikin muryarsa mai sanyi ya fara gaisar da ita ta amsa,shiru ya d'an yi can kuma ya d'ago don tunda ya shigo kanshi na a k'asa,
"Ya mai jiki",
"Ah maijiki da sauk'i sosae,oni Hajiya sai da ta taso ka ai nace mata ta samu sauki da bata wahalar da kai ba wllh", shi dai shiru yayi idonshi na kan floor d'in dakin,ita kam gwaggo idonta na akanshi bata ta6a tunanin zai zo gidan ba don iyakarta dashi su gaisa ne in yazo gidan hajiya,
can tace"Mun ga d'awainiyar abun Arziki,inata son inzo in yi godiya wllh jikin nata ne ya hana,don jiya gaba d'aya bansamu na fita bama saboda jikin nata,yau nike niyyar in shigo da daddare sai kuma ga ka,da nasan zaka zo ai da tunda safe na shigo"fuskarta d'auke da fara'a take yin maganar,
d'an guntun Murmushi yayi ba tare da ya kalleta ba yace"ba wani abu ai",
Godiya ta shiga yi mashi sosae tana shi mashi Albarka,tun yana amsawa kasa kasa har dae yayi shiru yana ci gaba da amsawa acikin ransa,tana cikin yin godiyar Amadu ya shigo dauke da plate ya d'auro ruwa pure water da yan k'ananun robobin lemu guda biyu don irinsu kawae yake saidawa saboda yan makaranta don ba freezer gareshi ba a shagon,a gaban haisam ya aje ya k'ara gaidashi kafin ya fita,shiru sukayi na d'an wani lokaci don Mutumin ba gwanin yin fira bane ba kaman kuma a inda yake bak'o,