Sashe 50
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Tun daga ranar na fara tunanin barin gidan don kuwa kora da halin ta fara yi man,in suna kallo ita da yaranta dana shiga zata kashe kayan kallon tace kallon ya isa,haka zan fito Jiki a sanyaye,duk wannan abun Dr bai sani ba don bata yi man wulakancin agabanshi,watarana ina zaune a d'aki da daddare inata tunanin yadda zan bar gidan ba tare da Dr din ya tuhume ni ba don banson in haddasa masu fitina,can na tuna da wata tsohuwar gona da muka gada ta marigayi kakanku dake can gefen gari wanda alokacin inda gonar take ya d'an fara shigowa cikin gari don akwae yan gine ginen gidaje da aka fara yi a wurin,gari na wayewa na tafi daura wurin kawu shi6ado don kar6o wasu kudadena dake awurinshi anan nake sanar dashi inason zan gina koda d'aki daya ne a wannan gonar in koma,ya tambayeni dalili na kwashe komae na fad'i masa nan take ya goyi bayana yace daman bai kamata in yi masu zaune agidansu ba,shima ya k'ara man kudi na had'a harda na aikina dana d'an tara,ta hanyar wata Abokiyar aikina na samu wadanda suka gina man daki daya da kewaye aka kuma katange gidan,sai da aka gama ginin nasamu Dr kabeer A asibiti na sanar dashi cewa zan koma gidan,anan yake tambayana ko anyi man wani abu ne,nace mashi a'a inason zan daukko yaro nane nasa shi a makaranta to banson na k'ara d'aura mashi nauyi ne gana iyalinshi kuma,ya fahimce ni sosae yayi man fatan alkhairi ya kuma bani kudi masu yawa wanda zan sa Amadun a makaranta,Matar Dr na Zaune a falo ita da yaranta ba zato ba tsammani ta ganni d'auke da jakar kayana nayi mata godiya na sanar da ita zan bar gidanne daga haka nayi mata sallama na fito yaranta nata yi mun bye bye harda yar kwallarsu,wannan shine dalilin dawowata wannan gidan da muke zaune",
"Lokacin dana dawo na d'an shishshiga makwabta don agaisa in kuma gabatar masu da kaina amatsayin sabuwar makwabciyarsu,alokacinne nashiga gidan Hajiyar Sanata wanda ada bai kai yadda yake yanzu girma ba da k'ayatuwa,hannu bibbiyu ta kar6e ni ba kamar da ta ji ni yar daura ce don itama Asalin yar can ce tana ma da dangantaka da Masarautar Dauran,daga nan muka fara zumunci da ita sosae tamkar uwa haka na dauketa don ta haifeni,koda na daukko Amadu nasashi a makaranta kusan duk dawainiyar karatunshi ita keyi,banda damuwar inda zan barshi in zan tafi aiki don da ya dawo bannan zai tafi gidan hajiya daga baya tukur ya zama d'an gidan suka fara abota tare ma suke tafiya makarantar allo da yamma,rashin sa Amadun makaranta da wuri ne yasa tukur d'in ya wuce shi don duk tsararraki ne amman Amadu ya dan girme mashi,kinga shi tukur yanzu yana makarantar gaba da Secondary shikuma Amadu har yanzu a sakandiren yake,A hankali ahankali da Kud'in da nike samu na albashi naci gaba da ginin gidan nan har yanzu ya koma haka,to Hajiya Fatuu yar Jarida,yanzu kinji komae ko?"
Kyalkyacewa da Dariya fatuu tayi tace"Amman wannan matar Dr din shegiya ce,daman kin Aure shin muga yadda zata yi,Oh da yanzu muna gidan Dr shine kakana kuma kinga da cikin sauki zai taimaka man in zama likita,Allah ya isa na matar Dr",Dariya gwaggo tayi tana girgiza kai jin shirmen fatuu"bana hana ki zagi ba,ni sam banga laifinta ba wllh kishi take akan mijinta ba wani abu ba,duk da hakan bai hana ayi mata kishiyoyin ba har ma guda biyu,yana nan yanzu shi Medical Director ne",
Fatuu tace"Allah ya kara,yasa ma ya cike ta hud'un",girgiza kai kawae Gwaggo tayi,
Hannu fatuu ta kai ta shafo kanta da sauri tace"Gwaggo ya naji kamar kina man kitso kuma",
"Eh wai in rage hanya,bana fulani kika ce kina so ba,na gaban ne nike yi maki goben in Allah ya kaimu sai in k'arasa maki",kai fatuu ta daga alamar toh,
Shiru sukae na wani lokaci kafin fatuu tace"Gwaggo kinsan Yaya Handsome?",
"yaya Handson kuma wani abu ne hakan?" gwaggo ta tambaya,kyalkyacewa da dariya tayi"kai gwaggo mutum ne fa,d'and'an Hajiyar Sanata nike nufi fa" ta6e baki gwaggo tayi"Haisam dinne wani handson,kuma waya fad'i maki d'and'an Hajiya ne,ke ko fadi maki akae ita ta haife shi kya yarda,Jikanta ne,Senator d'in da kika ji ana cewa shine d'an hajiyar shikuma Haisam d'an Senator dinne",waro ido fatuu tayi"haba ashe shiyasa kwata kwata basu kama,ni wllh dana ganshi zaune Agidan nayi zaton danta ne ashe anko muka yi dashi shima kakarshi ce ita",
"Itama Hajiya yaranta biyu a Duniya,amman ita ba kamar ni ba tana haihuwar kawae tana samun matsala ta yawan 6ari,wani cikin kuma inta samu har sai ta haihu sai d'an yazo ba rai,to daga baya ma sai aka juya mata mahaifar kawae,Shi Senator d'in shine babban d'an hajiyan daga shi sai Hajiya Maryam tana lagos tana aure Bature ne take aure,Allah cikin ikonsa su duk suna haihuwa sosae shi Senator Ali bansan ainihin yawan yaranshi ba,amman ita hajiya Maryam din tana da yara biyar yanzu,yaranta tubarkallah suma kaman turawan suke don duk farin ubansu suka daukko ga gashi kwayar idanunsu kala daban daban,da suna yawan zuwa amman yanzu sun rage zuwa ita Hajiyar ke zuwa can ta d'an kwana biyu......",
Cike da mamaki fatuu tace"Bature mai jan kunnuwa,Gwaggo ina ta same shi har ta aure shin?",
"Oho bansani ba,amman kya iya zuwa ki tambayi hajiyan"cike da gatse tayi maganar,
"To shi Yaya Handsome d'in Gwaggo waya biyo ne,naga shima kalan yan kasan waje ne",
"Senator Ali mai Kud'in gaske ne,Don a yadda naji yafi duk wani Senator d'an Arewa kudi,yana da kamfanoni iri iri har a kasashen dake makwabtaka damu,yana da gidajen Mai,da kamfanonin saida Motoci,Wanda wasu ya gaje sune daga Mahaifinsa,Mahaifiyar Haisam ba yar nan kasar bace Asalinta yar kasar Ethiopia ce...." katseta fatuu tayi"Wace k'asa ce kuma Ethiopia Gwaggo?",
"Kasar Ethiopia tana a cikin nahiyar Africa,kinsan akwae nahiyoyi bakwae a Duniya,Akwae Nahiyar turawa,Larabawa,Indiyawa....." da sauri Fatuu ta katse mata hanzarinta"Continent ake cewa gwaggo an yi mana shi a Makaranta guda bakwae ke akwai",
"Yauwa to Contilet d'in..." wata Mahaukaciyar Dariya fatuu ta saki"kai Gwaggo wayace maki Contilet yake,kalli bakina kiga yadda nike fad'i,CONTINENT" ta dashe
baki tana nuna ma gwaggon,
d'an guntun tsoki taja"to ban fad'in yadda kike cewan ki kyale ni da yanda na iyan" Fatuu dake ta dariya tace"Aikam wllh in turawa suka ji ki garkameki zasu yi a gidan yarin kasan teku kije kita cin gabza",
"Tunda Sarauniyar Engila na zaga ba" gwaggo ta fad'a fuskarta ad'an daure,
"To ci gaba kice Contilet d'in..." a harzuke gwaggo tace"banci gaban",
"Haba Kakus,kinsan fa wasa nike don Allah kici gaba da bani labarin Yaya Handsome d'in" ta hada hannuwanta tana rokon gwaggon,
"Zanci gaba,amman wllh kika kara katseni na gama"d'aga kai fatuu tayi alamar ta yarda,
"Mahaifiyarshi Fateema Fulanin Ethiopia ce,yayin da Mahaifinta yake Balarabe wato Kakan Haisam din na wurin Uwa,a yadda Hajiya ke ban labari Aiki ne ya kaishi kasar Ethiopian har ya Auri Kakar Haisam d'in wadda yar sarauta ce acan,suka haifi Mahaifiyarshi Fateema wadda yan biyu ne su,Wani taron Yan kasuwa ne yakai Senator Ali kasar Ethiopian anan ya had'u da Mahaifiyar Haisam din,shi da Abokinshi suka Aure su ai na fada maki yan biyu ne su,Fateema da Zainab,ita Zainab d'in yanzu haka Mijinta shine Gwamnan Jahar Nasarawa,ita kuma Fateema tana Abuja Gidan Senator Ali,da farko kafin ya zama Sanata din anan Katsina suke zaune a G.R.A,nan yake da katafaren gida,Hajiya ta ce lokacin da ta dawo Katsina don da a Abuja take lokacin Mijinta na Minister a gidan ta fara zama,to lokacin da shikuma zai koma Abuja yaso ta Zauna a Gidan don tace bazata bisu Abujan ba Amman taki acewarta yayi mata girma,shine aka gina mata wannan wanda kusan rabin Unguwar nan duk filayenshi ne da ya saida ma mutane,Allah yasa ma Hajiya kaunar Haisam tunda aka haifeshi Wanda hakanne yasa ta roki abata shi har yayi Primary da k'aramar Sakandire awurinta acan Abuja kafin ta dawo nan ya karasa Secondary d'in anan daganan kuma ya tafi kasar waje yayi Degree dinsa na farko bayan ya gama bai dawo wurinta ba ya fara aiki a Abuja sai dae yana yawan zuwa daga baya ya sake fita wata kasar yayi Degree na biyu shine da ya gama ya dawo nan,to kinji game da Haisam din",ta k'arasa tana kallon fatuu,
"Ohh,yanzu nagane dalilin dayasa bai ceman Fateema kamar yadda Hajiyan ke kira na shi saidae yace man Zarah,ashe sunan Mamanshi ne" fatuu tayi maganar tana jinjina kai,
"To gwaggo wannan Sojan na d'akin Hajiyan waye shi??"
",
kai gaskiya fatuu na gaji da wadannan tambayoyin haba,wannan dama yar Jarida kawae kika zama,shi d'in Mijin Hajiya ne General Adamu Zakee,Asali d'an nan Katsina ne kuma Soja ne tun Zamanin turawa,bayan ya kai matakin janar yayi retire daga nan aka bashi Ministern tsaro wanda yana ruke da mukamin ne ya rasu Sakamakon had'arin Jirgin Sama da ya rutsa dashi anan kasar....."katseta Fatuu tayi"Allahu Aikuwa nasan lokacin da yayi hadarin wll....."bata k'arasa ba sakamakon bugun bakinta da Gwaggon tayi tace"in buge bakin mai karya kawae,Mutumin da ya rasu kusan Shekaru Goma Sha biyar yanzu shine zaki ce wani kinsan lokacin,ashe har yanzu baki daina wannan muguwar k'aryar ba",
Turo baki Fatuu tayi"wllh ba karya nike ba,nayi zaton sune suka yi wani had'ari da akace Jirgi ya fad'o a Yola" Gwaggo dake harararta ta ture mata kai"d'aga ni in tashi inyi Sallah anata kira,kinga naso ma ki daka man daddawa wllh gashi har an kira Sallah,yi sauri kiyi sallar sai ki d'an kwankwatsa man ita"Wani kallo Fatuu ta bita dashi ta cuno baki"kai Gwaggo,kai gwaggo,wai an gama hiran yan gayu kuma zaki wani ce a daka daddawa,maimakon kice inje in kama kaza daya a keji in yanka",
Ruke ha6a gwaggo tayi"Waye zai wani baki ki yanka masa kaza,ance maki na manta kazan da kika matsa kwanaki in baki ki yanka kika gutsire ma kaine,ba wata kazar da za'a yanka sai Azumi in Allah ya kaimu,Nama dae ai daidai gwargwado ina siyowa,kuma inma tuwo kike tunani zanyi to bashi bane taliyar hausa ce za'a dan 6ararraka"Lokaci guda Fatuu ta washe baki"Yauwa Kakus yanzu naji magana,ni zan dafa to",
"Lokacin dana dawo na d'an shishshiga makwabta don agaisa in kuma gabatar masu da kaina amatsayin sabuwar makwabciyarsu,alokacinne nashiga gidan Hajiyar Sanata wanda ada bai kai yadda yake yanzu girma ba da k'ayatuwa,hannu bibbiyu ta kar6e ni ba kamar da ta ji ni yar daura ce don itama Asalin yar can ce tana ma da dangantaka da Masarautar Dauran,daga nan muka fara zumunci da ita sosae tamkar uwa haka na dauketa don ta haifeni,koda na daukko Amadu nasashi a makaranta kusan duk dawainiyar karatunshi ita keyi,banda damuwar inda zan barshi in zan tafi aiki don da ya dawo bannan zai tafi gidan hajiya daga baya tukur ya zama d'an gidan suka fara abota tare ma suke tafiya makarantar allo da yamma,rashin sa Amadun makaranta da wuri ne yasa tukur d'in ya wuce shi don duk tsararraki ne amman Amadu ya dan girme mashi,kinga shi tukur yanzu yana makarantar gaba da Secondary shikuma Amadu har yanzu a sakandiren yake,A hankali ahankali da Kud'in da nike samu na albashi naci gaba da ginin gidan nan har yanzu ya koma haka,to Hajiya Fatuu yar Jarida,yanzu kinji komae ko?"
Kyalkyacewa da Dariya fatuu tayi tace"Amman wannan matar Dr din shegiya ce,daman kin Aure shin muga yadda zata yi,Oh da yanzu muna gidan Dr shine kakana kuma kinga da cikin sauki zai taimaka man in zama likita,Allah ya isa na matar Dr",Dariya gwaggo tayi tana girgiza kai jin shirmen fatuu"bana hana ki zagi ba,ni sam banga laifinta ba wllh kishi take akan mijinta ba wani abu ba,duk da hakan bai hana ayi mata kishiyoyin ba har ma guda biyu,yana nan yanzu shi Medical Director ne",
Fatuu tace"Allah ya kara,yasa ma ya cike ta hud'un",girgiza kai kawae Gwaggo tayi,
Hannu fatuu ta kai ta shafo kanta da sauri tace"Gwaggo ya naji kamar kina man kitso kuma",
"Eh wai in rage hanya,bana fulani kika ce kina so ba,na gaban ne nike yi maki goben in Allah ya kaimu sai in k'arasa maki",kai fatuu ta daga alamar toh,
Shiru sukae na wani lokaci kafin fatuu tace"Gwaggo kinsan Yaya Handsome?",
"yaya Handson kuma wani abu ne hakan?" gwaggo ta tambaya,kyalkyacewa da dariya tayi"kai gwaggo mutum ne fa,d'and'an Hajiyar Sanata nike nufi fa" ta6e baki gwaggo tayi"Haisam dinne wani handson,kuma waya fad'i maki d'and'an Hajiya ne,ke ko fadi maki akae ita ta haife shi kya yarda,Jikanta ne,Senator d'in da kika ji ana cewa shine d'an hajiyar shikuma Haisam d'an Senator dinne",waro ido fatuu tayi"haba ashe shiyasa kwata kwata basu kama,ni wllh dana ganshi zaune Agidan nayi zaton danta ne ashe anko muka yi dashi shima kakarshi ce ita",
"Itama Hajiya yaranta biyu a Duniya,amman ita ba kamar ni ba tana haihuwar kawae tana samun matsala ta yawan 6ari,wani cikin kuma inta samu har sai ta haihu sai d'an yazo ba rai,to daga baya ma sai aka juya mata mahaifar kawae,Shi Senator d'in shine babban d'an hajiyan daga shi sai Hajiya Maryam tana lagos tana aure Bature ne take aure,Allah cikin ikonsa su duk suna haihuwa sosae shi Senator Ali bansan ainihin yawan yaranshi ba,amman ita hajiya Maryam din tana da yara biyar yanzu,yaranta tubarkallah suma kaman turawan suke don duk farin ubansu suka daukko ga gashi kwayar idanunsu kala daban daban,da suna yawan zuwa amman yanzu sun rage zuwa ita Hajiyar ke zuwa can ta d'an kwana biyu......",
Cike da mamaki fatuu tace"Bature mai jan kunnuwa,Gwaggo ina ta same shi har ta aure shin?",
"Oho bansani ba,amman kya iya zuwa ki tambayi hajiyan"cike da gatse tayi maganar,
"To shi Yaya Handsome d'in Gwaggo waya biyo ne,naga shima kalan yan kasan waje ne",
"Senator Ali mai Kud'in gaske ne,Don a yadda naji yafi duk wani Senator d'an Arewa kudi,yana da kamfanoni iri iri har a kasashen dake makwabtaka damu,yana da gidajen Mai,da kamfanonin saida Motoci,Wanda wasu ya gaje sune daga Mahaifinsa,Mahaifiyar Haisam ba yar nan kasar bace Asalinta yar kasar Ethiopia ce...." katseta fatuu tayi"Wace k'asa ce kuma Ethiopia Gwaggo?",
"Kasar Ethiopia tana a cikin nahiyar Africa,kinsan akwae nahiyoyi bakwae a Duniya,Akwae Nahiyar turawa,Larabawa,Indiyawa....." da sauri Fatuu ta katse mata hanzarinta"Continent ake cewa gwaggo an yi mana shi a Makaranta guda bakwae ke akwai",
"Yauwa to Contilet d'in..." wata Mahaukaciyar Dariya fatuu ta saki"kai Gwaggo wayace maki Contilet yake,kalli bakina kiga yadda nike fad'i,CONTINENT" ta dashe
baki tana nuna ma gwaggon,
d'an guntun tsoki taja"to ban fad'in yadda kike cewan ki kyale ni da yanda na iyan" Fatuu dake ta dariya tace"Aikam wllh in turawa suka ji ki garkameki zasu yi a gidan yarin kasan teku kije kita cin gabza",
"Tunda Sarauniyar Engila na zaga ba" gwaggo ta fad'a fuskarta ad'an daure,
"To ci gaba kice Contilet d'in..." a harzuke gwaggo tace"banci gaban",
"Haba Kakus,kinsan fa wasa nike don Allah kici gaba da bani labarin Yaya Handsome d'in" ta hada hannuwanta tana rokon gwaggon,
"Zanci gaba,amman wllh kika kara katseni na gama"d'aga kai fatuu tayi alamar ta yarda,
"Mahaifiyarshi Fateema Fulanin Ethiopia ce,yayin da Mahaifinta yake Balarabe wato Kakan Haisam din na wurin Uwa,a yadda Hajiya ke ban labari Aiki ne ya kaishi kasar Ethiopian har ya Auri Kakar Haisam d'in wadda yar sarauta ce acan,suka haifi Mahaifiyarshi Fateema wadda yan biyu ne su,Wani taron Yan kasuwa ne yakai Senator Ali kasar Ethiopian anan ya had'u da Mahaifiyar Haisam din,shi da Abokinshi suka Aure su ai na fada maki yan biyu ne su,Fateema da Zainab,ita Zainab d'in yanzu haka Mijinta shine Gwamnan Jahar Nasarawa,ita kuma Fateema tana Abuja Gidan Senator Ali,da farko kafin ya zama Sanata din anan Katsina suke zaune a G.R.A,nan yake da katafaren gida,Hajiya ta ce lokacin da ta dawo Katsina don da a Abuja take lokacin Mijinta na Minister a gidan ta fara zama,to lokacin da shikuma zai koma Abuja yaso ta Zauna a Gidan don tace bazata bisu Abujan ba Amman taki acewarta yayi mata girma,shine aka gina mata wannan wanda kusan rabin Unguwar nan duk filayenshi ne da ya saida ma mutane,Allah yasa ma Hajiya kaunar Haisam tunda aka haifeshi Wanda hakanne yasa ta roki abata shi har yayi Primary da k'aramar Sakandire awurinta acan Abuja kafin ta dawo nan ya karasa Secondary d'in anan daganan kuma ya tafi kasar waje yayi Degree dinsa na farko bayan ya gama bai dawo wurinta ba ya fara aiki a Abuja sai dae yana yawan zuwa daga baya ya sake fita wata kasar yayi Degree na biyu shine da ya gama ya dawo nan,to kinji game da Haisam din",ta k'arasa tana kallon fatuu,
"Ohh,yanzu nagane dalilin dayasa bai ceman Fateema kamar yadda Hajiyan ke kira na shi saidae yace man Zarah,ashe sunan Mamanshi ne" fatuu tayi maganar tana jinjina kai,
"To gwaggo wannan Sojan na d'akin Hajiyan waye shi??"
",
kai gaskiya fatuu na gaji da wadannan tambayoyin haba,wannan dama yar Jarida kawae kika zama,shi d'in Mijin Hajiya ne General Adamu Zakee,Asali d'an nan Katsina ne kuma Soja ne tun Zamanin turawa,bayan ya kai matakin janar yayi retire daga nan aka bashi Ministern tsaro wanda yana ruke da mukamin ne ya rasu Sakamakon had'arin Jirgin Sama da ya rutsa dashi anan kasar....."katseta Fatuu tayi"Allahu Aikuwa nasan lokacin da yayi hadarin wll....."bata k'arasa ba sakamakon bugun bakinta da Gwaggon tayi tace"in buge bakin mai karya kawae,Mutumin da ya rasu kusan Shekaru Goma Sha biyar yanzu shine zaki ce wani kinsan lokacin,ashe har yanzu baki daina wannan muguwar k'aryar ba",
Turo baki Fatuu tayi"wllh ba karya nike ba,nayi zaton sune suka yi wani had'ari da akace Jirgi ya fad'o a Yola" Gwaggo dake harararta ta ture mata kai"d'aga ni in tashi inyi Sallah anata kira,kinga naso ma ki daka man daddawa wllh gashi har an kira Sallah,yi sauri kiyi sallar sai ki d'an kwankwatsa man ita"Wani kallo Fatuu ta bita dashi ta cuno baki"kai Gwaggo,kai gwaggo,wai an gama hiran yan gayu kuma zaki wani ce a daka daddawa,maimakon kice inje in kama kaza daya a keji in yanka",
Ruke ha6a gwaggo tayi"Waye zai wani baki ki yanka masa kaza,ance maki na manta kazan da kika matsa kwanaki in baki ki yanka kika gutsire ma kaine,ba wata kazar da za'a yanka sai Azumi in Allah ya kaimu,Nama dae ai daidai gwargwado ina siyowa,kuma inma tuwo kike tunani zanyi to bashi bane taliyar hausa ce za'a dan 6ararraka"Lokaci guda Fatuu ta washe baki"Yauwa Kakus yanzu naji magana,ni zan dafa to",