Sashe 21
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A daidai gate ta tsaya wurin Officer dake zaune shi kad'ai tace"Sannu da gadin gate Officer" ya d'ago ya kalleta yana daria,don maganar tata ta bashi dariya yace "Yauwa kema sannunki yar fillo" tace "kai kad'ai a zaune ina d'ayan Officern yake? Rausayar da kai yayi yace ya tafi yin wani uzuri ne" ta ta6e baki tace "ba wani uzuri wayo yayi maka yanzun haka zance ya tafi wurin Budurwarshi ya barka kai d'aya kana ta aikin tsaro,wllh kada ka yarda ya maida kai sakarai kaima ka rama atoh" jinjina kai yayi yana d'an murmushi jin abunda tace,sam baiji komae ba don yasan ta sam ba datsar k'umba gareta ba duk abunda yazo bakinta fad'i take yace"to yar fillo ya zanyi in rama d'in? turo baki tayi tace "nifa ka daina ceman yar fillo" kyalkyacewa da dariya yayi don dama yasan bata son sunan yace "to ke ba yar fillon bace? tace "to nidai banso ka kira ni da Fatuu na kawae" yace "to shikenan hajia fatuu na bari,sai a fad'i man yadda zan rink'a ramawa nima" tace "yo kaima budurwar zakayi sai ka rink'a tafiya tadi....." katseta yayi yace "to ni ina zan samu budurwa nida kullum ina nan zaune ina tsaron gate" tace "Yo yadda yayi shima ya samu zaka yi" ta juya tana k'okarin shiga gidan yace "to ko ke kizama budurwar tawa kawai ma...",
A fusace ta juyo bayan ta tsaya ta bishi da wani kallo,shi kam sai daria yake,tace" God forbid! ni bazan zama budurwar kowa ba yanzu sai na zama likita,kuma lokacin ni nafi karfin mai gadin gate,tana gama fad'in hakan ta shige sai kuma ta sake lek'owa ta cikin gate din tace "in budurwa ka ke so kaje wurin kawata Haulatu don ita ban ji tana da burin zama koda malamar makaranta ba,kuma nasan zata so ka don sakarya ce" daga haka ta shige tana ta tik'ar daria,shima Officer dariyar yake yana girgiza kai.
A corridor ta tsaya ta cire takalmanta sannan ta d'an lek'a cikin parlon a hankali ta hango hajia dake zaune saman 2-seater ta d'aura takardu saman sofa table tana rubuce rubuce idanuwanta sanye cikin gilashi,cikin d'aga murya Fatuu tace"Assalamu alaikum ga bak'uwa,ga bakuwa daga makkah" hajiya ta d'ago ta kalli entrance tana daria,fatuu ta k'ara maimaita abunda tace,Hajia ta girgiza kai tasan in ba amsa mata tayi ba,haka zatai tayi tace"Maraba da bakuwa mutan makkah shigo" shigowa fatun tayi tana ta kyalkyalar dariya itama hajiyar dariyar take tace "ja'ira",
kusa da ita fatuu taje ta zauna tace"Hajiyar Sanata ina wuni" Hajia tace "lafia lou yar gidan hajiar sanata,kwana biyu baki zo kika gaida hajiyar taki ba, jiya juma'a inata zuba ido banga kinzo yiman barka da juma'a ba" Fatuu ta d'age kai ta kwanta jikin kujerar tace "Ai jiya ban je ko ina ba a d'aki na wuni kamar maijego" ta kai maganar tana ta daria,hajiya dake kallonta tace "hala rigima kika janyo?", "a'a" Fatuu tace tana kunshe daria,
Hajia ta girgiza kai tace"habawa,nida nasan hali,hakanan ba ciwo ba mi zai sa ki wuni a d'aka,har yanzu dai kin k'i daina yin rigima da mutane ko Fatima? dago kanta tayi daga jikin kujerar ta d'an turo baki tace"wllh hajiya mutane ne ke tono na..." hajiya dake kallonta ta katseta"ke kuma ba hakuri ko" dariya kawai fatuu tayi,hajiya tace "gaya man abunda yasa kika wuni a daki" sosae gaban fatuu ya fadi a ranta tace "tabb wllh bazan fadi mata na fasa ma wani glass ba" a fili tace "wata yarinya ce muka yi fad'a na fasa mata hanci da baki" ta kai maganar tana nok'e kai,hajia dake kallonta ta girgiza kai tace "kai jama'a! Yanzu ina amfanin haka fatima,aita gaya maki magana baki ji,ke sam baki da hakuri to kuwa kwanan nan zamu 6ata wllh,6atawa kuma ta har abada kar ma kiyi tunanin zaki ban hakuri in hakura...."da sauri Fatuu ta saukko daga kan kujerar ta duk'a gabanta tace "Don Allah Hajiar Sanata kiyi hakuri wallahi tallahi ita taja ni kinji na rantse,daga nace ta matsa man wuri a Bus din makaranta in zauna bayan an tashi,ta fara gaya man maganganu nai shiru na kyaleta,hakan bai isa ba da muka sauka taci gaba har tana fad'a ma abokanta wai ni daga k'auye aka kawoni..." tayi narai narai da idanu kaman zata yi kuka,
Ajiyar zuciya hajiya ta sauke tana ta kallon fatuu da har kwalla sun cika idanunta, tasan dama hakan sai ya faru don bata son taji tace zasu 6ata,tace"shikenan tashi ki zauna,amman don Allah Fatima ki rika hakuri kinji,yawan fad'an da kike da mutane shiyasa suke tsokanarki ai,ki koyi kauda kai akan abunda bai kai ya kawo ba kinji yar gidan Hajiya" ta k'arasa maganar ta sigar lallashi,
Gyad'a kai Fatuu tayi ta koma kan kujera ta zauna tana murmushin jin dadi,hajiya ta kalli kanta da gyalen ya d'an zame tace "wai har yanzu baki je an kitse kan nan ba? ko rannan ba saida nayi maki magana akan kije ayi maki kitso bane?"
Ta marairaice fuska tace "wllh Balarabar ce zafin hannu ne da ita hajia,in tayi man kitso kaman kan zai tuge gaba d'aya,ni shiyasa banson zuwa" hajiya tace"ba wani zafin hannu,nima ai tana man kitson ko,kawai dai baki son kitson ne,don ma Allah ya taimakeki gashin mai kyau ne ai da tuni ya lalace yadda baki kula dashi d'in nan,bari in Balarabar tazo yiman kitson ai nasa tayi maki shi a gabana kuwa",
ta juya ta kalli kwanon da fatuu ta aje saman carpet da ta shigo tace"mina samu da daren nan haka" Fatuu ta d'ago tace "tuwon dawa ne,Gwaggo tace na kawo maki" fuskar hajiya d'auke da murmushi tace"Aikam nagode wllh,dama kwana biyu banci tuwon dawa ba,gashi Dije badai iya tuwo ba....." Fatuu tace"nikam dai ai ta kusa ta kashe ni da shi" Hajiya tayi daria tace "A ina ki ka ta6a ganin tuwo ya kashe mutum fatima?" Shiru tayi tana ta turo baki,hajia dake ta daria tace"to kinga tashi kidau kwanon miyan nan kije kitchen kisamu bowl mai kyau ki juyo man miyan sai ki daukko man plate in saka tuwon inci abuna yanzu yabi jiki kafin in kwanta,sai ki wanke kwanon ki zubo abinci na nan a kicin d'in kije kici tunda ni dai bazanso tuwon ya kashe ki ba" ta k'arasa maganar tana ta tik'ar daria,
Mik'ewa fatuu tayi ta dau kwanon miyan da ledan tuwon ta nufi kitchen,Hajia tace"ki fara zubo man ruwa a roba in wanke hannuwa",
juyo miyan tayi ta warware tuwon a plate ta kawo ma hajia,har ta juya zata koma kicin don zubo abincin ta waiwayo tace"Hajia ina Aunty Saude ne? Hajiya da har ta fara cin tuwon tace "tana a backyard taje ba su d'awisu abinci" fatuu tace "aikuwa bari inje bayan,dama kwana biyu ban gaisa da mutumina Aku ba...." hajia ta katse ta "A'a kar kije bayan nan,kije ki d'ibo abincin kizo ki tafi kinga dare yayi,na tabbata kika je wurin Aku kuma ai sai an biyo sawunki,ki bari gobe in Allah ya kaimu,ana tasowa islamiyyar safe sai kizo kusha fira dashi,yanzu je ki zubo abincin ki ciko kwanon" Fatuu ta gyad'a kai taje ta zubo abincin wanda dafa dukan couscous ne yaji uban kifi sai k'amshi ke tashi,ta dawo parlon ta aje kwanon akan carpet ta nufi kujerar dake kusa da telephone ta zauna lokacin Hajia har ta kusa cinye tuwon,Fatuu tasa hannu ta dau kan telephone din ta kara a kunnanta ta d'aura kafa d'aya kan daya tana murmura idanu,tace"Hajia" hajiya da ta tura tuwo a baki tace "Uwun" tace "wllh in nazama likita sai na sayi irin wannan telephone d'in kuma har a Office dina na wurin aiki zansa" hajia tace "to Allah ubangiji ya bada ikon zama likitan,amman a Office dinma gwamnati zata sa maki ba sai kinsha wahalan siya ba.....",
Saude ce ta shigo cikin parlon ta kofar baya hannuwanta rik'e da wata roba mai d'an fadi,tana hango fatuu ta aje roban a bakin kofar kicin ta nufo cikin parlon da fara'arta tace "Ah Fatuu yar gidan hajia yaushe ki ka shigo" Fatuu tace "tun d'an dazun,ai naso inzo bayan hajiya ta hana" ta d'an saci kallon hajia tana turo baki,ita dai Saude Murmushi kawae take,
Hajia ta girgiza kai ta kalli saude tace "to wai wurin Aku fa zata da daren nan" Saude ta jinjina kai tace"lallai kam gara ki bari sai gobe don in ki ka je yanzu har sai an biyo ki nasan" Hajia ta gyad'a kai alamar atoh, tace"Saude kije bedroom a bedside din hagu da kin jawo drawer d'in farko akwae kudi ki daukko yan ashirin guda biyar ki kawo man" Saude ta amsa da "to" ta juya don cika umarnin hajiyan.
Hannunta ruk'e da kudin ta dawo dan russunawa tayi ta mika ma ta,hajia tace tsaya ina zuwa,ta juya kan fatuu da ta yi mitsi mitsi da idanu ta d'age baki tana kallo tace "to taso ki tafi kinga har tara saura,yau dai banda wani abun ci,amman gashi kije ki siya ko biscuit ne" Fatuu ta mik'e tana fadin"to ki bashshi mana" Hajia tace "a'a,ai yaba kyauta tukwuici,na yaba da tuwon naji dadin shi kwarae,kice mata nagode Allah yabar zumunci,ya kara zakin hannu" takai maganar tana murmushi, Saude ta mik'a mata kudin,ta duk'a ta dau kwanon tace "Sai da safe Hajia" ta juya kan Saude tace "zanzo gobe da safe in antaso islamiyya Aunty Saude",
Saude da fara'a tace "to Allah ya kaimu" daga haka ta rungume kwanon a 6arin hannunta na dama ta nufi hanyar fita.......
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
*Mallakin*
⬇️
*ZAINAB LALUH*🌹
*(Oummu imam)*
_GARGADI!_
_Wannan littafin ni na kirkire shi,komae kaji yayi daidai ko shige da rayuwar ka/ki ko wani/wata to arashi ne ba da nufi bane kuma ina mai bada hakuri,Don haka kasantuwar littafin nawa ne,ban yarda wani/wata su canza mun littafi ba ko daukar wani bangare daga cikinsa ba tare da izini na ba,Haka ban amince ba,ban yarda ba,ban lamunce ba a yada man shi ba a wata kafa ba misali,YouTube da makamantansu,ba tare da an tuntube ni ba,ni mai littafin don neman izini,Don haka a kiyaye! kuma idan ka ko kin san ba wani muhimmin abu bane Don Allah kar ayi man magana don bazan kula mutum ba,Don haka mu mutunta kanmu_🤝
*Free Page1️⃣9️⃣&2️⃣0️⃣*
A fusace ta juyo bayan ta tsaya ta bishi da wani kallo,shi kam sai daria yake,tace" God forbid! ni bazan zama budurwar kowa ba yanzu sai na zama likita,kuma lokacin ni nafi karfin mai gadin gate,tana gama fad'in hakan ta shige sai kuma ta sake lek'owa ta cikin gate din tace "in budurwa ka ke so kaje wurin kawata Haulatu don ita ban ji tana da burin zama koda malamar makaranta ba,kuma nasan zata so ka don sakarya ce" daga haka ta shige tana ta tik'ar daria,shima Officer dariyar yake yana girgiza kai.
A corridor ta tsaya ta cire takalmanta sannan ta d'an lek'a cikin parlon a hankali ta hango hajia dake zaune saman 2-seater ta d'aura takardu saman sofa table tana rubuce rubuce idanuwanta sanye cikin gilashi,cikin d'aga murya Fatuu tace"Assalamu alaikum ga bak'uwa,ga bakuwa daga makkah" hajiya ta d'ago ta kalli entrance tana daria,fatuu ta k'ara maimaita abunda tace,Hajia ta girgiza kai tasan in ba amsa mata tayi ba,haka zatai tayi tace"Maraba da bakuwa mutan makkah shigo" shigowa fatun tayi tana ta kyalkyalar dariya itama hajiyar dariyar take tace "ja'ira",
kusa da ita fatuu taje ta zauna tace"Hajiyar Sanata ina wuni" Hajia tace "lafia lou yar gidan hajiar sanata,kwana biyu baki zo kika gaida hajiyar taki ba, jiya juma'a inata zuba ido banga kinzo yiman barka da juma'a ba" Fatuu ta d'age kai ta kwanta jikin kujerar tace "Ai jiya ban je ko ina ba a d'aki na wuni kamar maijego" ta kai maganar tana ta daria,hajiya dake kallonta tace "hala rigima kika janyo?", "a'a" Fatuu tace tana kunshe daria,
Hajia ta girgiza kai tace"habawa,nida nasan hali,hakanan ba ciwo ba mi zai sa ki wuni a d'aka,har yanzu dai kin k'i daina yin rigima da mutane ko Fatima? dago kanta tayi daga jikin kujerar ta d'an turo baki tace"wllh hajiya mutane ne ke tono na..." hajiya dake kallonta ta katseta"ke kuma ba hakuri ko" dariya kawai fatuu tayi,hajiya tace "gaya man abunda yasa kika wuni a daki" sosae gaban fatuu ya fadi a ranta tace "tabb wllh bazan fadi mata na fasa ma wani glass ba" a fili tace "wata yarinya ce muka yi fad'a na fasa mata hanci da baki" ta kai maganar tana nok'e kai,hajia dake kallonta ta girgiza kai tace "kai jama'a! Yanzu ina amfanin haka fatima,aita gaya maki magana baki ji,ke sam baki da hakuri to kuwa kwanan nan zamu 6ata wllh,6atawa kuma ta har abada kar ma kiyi tunanin zaki ban hakuri in hakura...."da sauri Fatuu ta saukko daga kan kujerar ta duk'a gabanta tace "Don Allah Hajiar Sanata kiyi hakuri wallahi tallahi ita taja ni kinji na rantse,daga nace ta matsa man wuri a Bus din makaranta in zauna bayan an tashi,ta fara gaya man maganganu nai shiru na kyaleta,hakan bai isa ba da muka sauka taci gaba har tana fad'a ma abokanta wai ni daga k'auye aka kawoni..." tayi narai narai da idanu kaman zata yi kuka,
Ajiyar zuciya hajiya ta sauke tana ta kallon fatuu da har kwalla sun cika idanunta, tasan dama hakan sai ya faru don bata son taji tace zasu 6ata,tace"shikenan tashi ki zauna,amman don Allah Fatima ki rika hakuri kinji,yawan fad'an da kike da mutane shiyasa suke tsokanarki ai,ki koyi kauda kai akan abunda bai kai ya kawo ba kinji yar gidan Hajiya" ta k'arasa maganar ta sigar lallashi,
Gyad'a kai Fatuu tayi ta koma kan kujera ta zauna tana murmushin jin dadi,hajiya ta kalli kanta da gyalen ya d'an zame tace "wai har yanzu baki je an kitse kan nan ba? ko rannan ba saida nayi maki magana akan kije ayi maki kitso bane?"
Ta marairaice fuska tace "wllh Balarabar ce zafin hannu ne da ita hajia,in tayi man kitso kaman kan zai tuge gaba d'aya,ni shiyasa banson zuwa" hajiya tace"ba wani zafin hannu,nima ai tana man kitson ko,kawai dai baki son kitson ne,don ma Allah ya taimakeki gashin mai kyau ne ai da tuni ya lalace yadda baki kula dashi d'in nan,bari in Balarabar tazo yiman kitson ai nasa tayi maki shi a gabana kuwa",
ta juya ta kalli kwanon da fatuu ta aje saman carpet da ta shigo tace"mina samu da daren nan haka" Fatuu ta d'ago tace "tuwon dawa ne,Gwaggo tace na kawo maki" fuskar hajiya d'auke da murmushi tace"Aikam nagode wllh,dama kwana biyu banci tuwon dawa ba,gashi Dije badai iya tuwo ba....." Fatuu tace"nikam dai ai ta kusa ta kashe ni da shi" Hajiya tayi daria tace "A ina ki ka ta6a ganin tuwo ya kashe mutum fatima?" Shiru tayi tana ta turo baki,hajia dake ta daria tace"to kinga tashi kidau kwanon miyan nan kije kitchen kisamu bowl mai kyau ki juyo man miyan sai ki daukko man plate in saka tuwon inci abuna yanzu yabi jiki kafin in kwanta,sai ki wanke kwanon ki zubo abinci na nan a kicin d'in kije kici tunda ni dai bazanso tuwon ya kashe ki ba" ta k'arasa maganar tana ta tik'ar daria,
Mik'ewa fatuu tayi ta dau kwanon miyan da ledan tuwon ta nufi kitchen,Hajia tace"ki fara zubo man ruwa a roba in wanke hannuwa",
juyo miyan tayi ta warware tuwon a plate ta kawo ma hajia,har ta juya zata koma kicin don zubo abincin ta waiwayo tace"Hajia ina Aunty Saude ne? Hajiya da har ta fara cin tuwon tace "tana a backyard taje ba su d'awisu abinci" fatuu tace "aikuwa bari inje bayan,dama kwana biyu ban gaisa da mutumina Aku ba...." hajia ta katse ta "A'a kar kije bayan nan,kije ki d'ibo abincin kizo ki tafi kinga dare yayi,na tabbata kika je wurin Aku kuma ai sai an biyo sawunki,ki bari gobe in Allah ya kaimu,ana tasowa islamiyyar safe sai kizo kusha fira dashi,yanzu je ki zubo abincin ki ciko kwanon" Fatuu ta gyad'a kai taje ta zubo abincin wanda dafa dukan couscous ne yaji uban kifi sai k'amshi ke tashi,ta dawo parlon ta aje kwanon akan carpet ta nufi kujerar dake kusa da telephone ta zauna lokacin Hajia har ta kusa cinye tuwon,Fatuu tasa hannu ta dau kan telephone din ta kara a kunnanta ta d'aura kafa d'aya kan daya tana murmura idanu,tace"Hajia" hajiya da ta tura tuwo a baki tace "Uwun" tace "wllh in nazama likita sai na sayi irin wannan telephone d'in kuma har a Office dina na wurin aiki zansa" hajia tace "to Allah ubangiji ya bada ikon zama likitan,amman a Office dinma gwamnati zata sa maki ba sai kinsha wahalan siya ba.....",
Saude ce ta shigo cikin parlon ta kofar baya hannuwanta rik'e da wata roba mai d'an fadi,tana hango fatuu ta aje roban a bakin kofar kicin ta nufo cikin parlon da fara'arta tace "Ah Fatuu yar gidan hajia yaushe ki ka shigo" Fatuu tace "tun d'an dazun,ai naso inzo bayan hajiya ta hana" ta d'an saci kallon hajia tana turo baki,ita dai Saude Murmushi kawae take,
Hajia ta girgiza kai ta kalli saude tace "to wai wurin Aku fa zata da daren nan" Saude ta jinjina kai tace"lallai kam gara ki bari sai gobe don in ki ka je yanzu har sai an biyo ki nasan" Hajia ta gyad'a kai alamar atoh, tace"Saude kije bedroom a bedside din hagu da kin jawo drawer d'in farko akwae kudi ki daukko yan ashirin guda biyar ki kawo man" Saude ta amsa da "to" ta juya don cika umarnin hajiyan.
Hannunta ruk'e da kudin ta dawo dan russunawa tayi ta mika ma ta,hajia tace tsaya ina zuwa,ta juya kan fatuu da ta yi mitsi mitsi da idanu ta d'age baki tana kallo tace "to taso ki tafi kinga har tara saura,yau dai banda wani abun ci,amman gashi kije ki siya ko biscuit ne" Fatuu ta mik'e tana fadin"to ki bashshi mana" Hajia tace "a'a,ai yaba kyauta tukwuici,na yaba da tuwon naji dadin shi kwarae,kice mata nagode Allah yabar zumunci,ya kara zakin hannu" takai maganar tana murmushi, Saude ta mik'a mata kudin,ta duk'a ta dau kwanon tace "Sai da safe Hajia" ta juya kan Saude tace "zanzo gobe da safe in antaso islamiyya Aunty Saude",
Saude da fara'a tace "to Allah ya kaimu" daga haka ta rungume kwanon a 6arin hannunta na dama ta nufi hanyar fita.......
*💖A SANADIN MAKWABTAKA💖*
*Mallakin*
⬇️
*ZAINAB LALUH*🌹
*(Oummu imam)*
_GARGADI!_
_Wannan littafin ni na kirkire shi,komae kaji yayi daidai ko shige da rayuwar ka/ki ko wani/wata to arashi ne ba da nufi bane kuma ina mai bada hakuri,Don haka kasantuwar littafin nawa ne,ban yarda wani/wata su canza mun littafi ba ko daukar wani bangare daga cikinsa ba tare da izini na ba,Haka ban amince ba,ban yarda ba,ban lamunce ba a yada man shi ba a wata kafa ba misali,YouTube da makamantansu,ba tare da an tuntube ni ba,ni mai littafin don neman izini,Don haka a kiyaye! kuma idan ka ko kin san ba wani muhimmin abu bane Don Allah kar ayi man magana don bazan kula mutum ba,Don haka mu mutunta kanmu_🤝
*Free Page1️⃣9️⃣&2️⃣0️⃣*