← Book details Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 137 OF 137

Sashe 137

Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Suna baro wurin ta fara gyangyad'i ganin hakan yasa yace ta sauke seat din ta kwanta sosae tace to, wuraren karfe biyar da wani abu suka shigo Katsina har saida suka iso bakin layin gidansu ta farka ganin inda suke yasa ta juya da alamun mamaki tace "wai ashe har mun dawo" kai ya daga mata idonshi akan hanyar layin ita kuma tana a kwance bata tada seat d'in ba,tunkan su k'arasa ya hango wata babbar bak'ar jeep fake a gefen gidan Hajiya tana facing d'insu da alama wanda ke ciki tafiya zaiyi daga jikin kopar motar ta wurin driver watace tsaye ta duk'ar da kanta da alama tana Magana ne da wanda ke acikin Motar, k'ura ido yay yana k'are mata kallo kafin da tsananin mamaki kan fuskarshi ya furta "What a Suprise!!!" jin abunda yace yasa Fatuu kallonshi ganin inda ya k'ura ma ido yasa ta juya ta kalli glass d'in gaban Motar itama ta kalli abunda yake gani, daidai gaban jeep d'in wadda Lexus GX460 ce ya parker tashi Motar lokacin kuma ta jikin kopar ta juyo, Tubarakallahu ahsanul khaliqin shine abunda na furta, kallo d'aya zakai mata ka yanke ba bahaushiya bace, doguwa ce ba kamar da yake takalman kafarta masu tsinine sosae tana sanye da straight gown ta babbar atampa glitter rigar ta bayyanar da dirinta sai dae sam bata da jiki ga d'amamman cikinta kai kace bata cin abinci, a bangaren kyawun fuska kuwa abun ba'a Magana don fara ce sosae tana da dogon hanci da d'an madaidaicin baki wanda lips dinsu ke jajur duk da da gani ta k'ara da janbaki, tayi d'aurin kallabi zara buhari yayin da yalwatacciyar sumarta brown ke d'aure da ribbom ta saketa saman gadon bayanta wuyanta na sanye da yar ziririyar sarka wadda da gani zinari ce haka ma d'an kunnan dake kunnanta barima ce ta zinari hannunta na hagu na sanye da golden agogo sam bata da mayafi ajikinta, tana juyowa ya bud'e Motar da sauri ya fita, nufarta yay tana ta faman sakar mashi kayataccen Murmushi koda ya isa gabanta kawae sai ta bud'e hannu ta rungumeshi can yasa hannu ya d'ago da ita suka had'a goshinsu suna ma juna dariya................End Of Book One,

Shin wacece wannan? Mi kuma ke tsakaninta da Haisam? Da gaske Haisam na son Fatuu kuma zai aureta? Amsoshin wadannan tambayoyin na acikin A Sanadin Makwabtaka kashi na biyu.

ALHAMDULILLAH, Anan na kawo karshen A Sanadin Makwabtaka kashi na farko wanda kamar gabatarwa ne ga ainihin Labarin dake a cikin kashi na biyu, ina rokon Allah yadda ya bani ikon kammala kashi na farko ya bani ikon kammala kashi na biyu cikin koshin lafiya, ya kuma bani ikon rubuta abunda zai amfaneni ya amfani Al'ummar Musulmi gaba d'aya Amin.

Ga mai bukatar cigaba da karanta kashi na biyu wato Book 2 zai biya kudin karatu Naira 300 kacal ta wannan Account din👇

1509618776
Zainab Bature
Access Bank

Za'a turo da shedar biya ta daya daga cikin wadannan Lambobin wayan ko kuma tuntu6a don neman karin bayani, 09013804524 ko 08169856268.

Thanks and i luv u as u patronize🤝🥰
Chapter 137 · 0% Book details