← Book details Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 133 OF 137

Sashe 133

Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da Safe Misalin karfe 7 da rabi Motar Haisam ta fito daga cikin gidan don tafiya aiki kamar ko yaushe, yana hawa hanya wata yarinya ta fara d'aga mashi hannu alamar ya tsaya daga d'ayan bangaren, a hankali ya tsaida Motar bayan ya d'an wuceta kad'an tana ganin ya tsayan ta nufoshi da sauri ta tsaya bakin kopar sai zare ido take don bata hangen wanda ke ciki, Slowly glass d'in kopar ya fara sauka tana yin arba da fuskar Haisam din ta washe mashi baki tana dariya, bin ta da kallo yay ya kasa fahimtar wacece duk da yana ganin kaman ya ta6a ganin face dinta katseshi tay da fad'in "Yalla6ai ina kwana" kai ya daga alamar amsawa taci gaba da cewa "Yalla6ai baka ganeni ba ko?" nan ma kan ya daga mata tace "Jamila ce wadda ka ta6a ba kudi lokacin da ka ganmu muna fad'a da wata har ta fasa man bokiti" sai lokacin ya ganeta taci gaba "ai tun lokacin dana kai ma innata kud'in washegari ta bani awara mai yawa in kawo maka amman dana zo sai masu tsaron gate din suka hana ni shiga har ce masu nayi to su barni inje wurin Hajiyan amman suka hanani na basu awaran su baka nan ma suka ki amsa saidae na maida ma innata, kwanaki can ma na ganka ka shige na biyoka in gaidaka amman suka hanani har wani yace in ban tafi ba zai har6e man kafafuna shiyasa na tafi ban kuma zuwa gidan ba" jinjina mata kai yay da d'an Murmushi ita kuwa sai faman washe baki take kamar wadda akai ma albishir d'in Aljanna,
"Bakya zuwa Skul ne" ya tambaya ganinta rungume da bokiti da alamun tallan take, da sauri tace "da ina zuwa amman yanzu na daina" still idonshi na kanta ya tambayeta miyasa ta daina zuwan cikin karewar murya ta fara mashi bayani "Babana ne ya kwanta jinya kuma ance sai anyi mashi aiki gashi bamu da kud'in, gidan da muke zaune ma an tada mu don Alhaji Sanin ya sayar da gidan amman yana da wani fili a gaban gidan shine yasa akayi mana d'aki guda biyu da kwano irin wanda ake rufin sama to yanzu anan muke kuma shi baban nawa bai iya komae dole sai munyi tallan ake samun kudin da zamu ci abinci a d'an kuma siya mashi magani tunda ba'a samu anyi mashi aikin ba shiyasa innata tace in hakura da makarantar zuwa wani lokaci in inada rabo don tasan ina son karatun" tana k'arasawa kwalla suka zubo mata tayi saurin sa gefen hijab d'inta ta goge don karfin hali kuma taci gaba da yi mashi dariyar, shiru kawae yay yana juya Maganarta acikin ranshi don ba k'aramin ta6a mashi zuciya tay ba, ba kamar da yaji inda suke rayuwa wai a dakin da akayi da zinc taya Mutum zaiyi rayuwa cikin irin wannan abun da ke mugun d'aukar zafi in rana tayi,
"Zanje aiki ne ina makara, Allah ya bashi lafiya" ya fad'a da sanyayyar muryarshi, amsa mashi tayi da Amin kafin da sauri ta d'ago da bokitin tallan data ajiye a kasa tace "Yalla6ai bari in zuba maka kosai" da sauri ya girgiza mata kai tace "Don Allah Yalla6ai ka amsa nasan in na gaya ma innata zata ji dad'i sosae don lokacin data ban awara na kai maka bata ji dadi ba da ba'a samu baka ba" shiru ya d'anyi tace ta zuba mashi ya d'aga mata kai alamar eh kafin yace kad'an zata zuba, aikuwa cike da farinciki ta duk'a ta zubo mashi saida ta cika farar leda ta daura mashi yaji daban ta saka aciki sannan ta d'ago ta mik'a mashi ya mik'o hannu ya amsa da Dan Murmushi ya furta "Nagode" ta jinjina mashi kai still da dariya a fuskarta daga haka glass d'in Motar ya d'aga yajata ita kuwa Jamilar cike da murna ta sunkuci bokitin ta shige lungun gidansu don taje ta fad'awa innarsu, saida ya tsaya ya d'auki Fatuu kamar kullum suka biya suka d'auki haulat kafin suka wuce bayan ya ajesu ya basu kudin break ya had'a masu da k'osan don shi bai cin kosai kawae ya amsa ne don ya fahimci zata ji dadi in yayi hakan, Yana dawowa daga aiki da yamma ko part d'inshi bai wuce ba ya nufi na Hajiya don tunda yaje wurin aikin Maganganun Jamila sun tsaya masa arai, da sallama ya shiga lokacin Hajiya na zaune tana duba wani littafin addini don dama tafi ba karatun littattafan da suka shafi addini karfi fiye da karance karancen jaridu, kusa da ita yaje ya zauna yay mata sannu da gida don asaman 3 seater take zaune, tunda ya zauna take binshi da ido don ta lura kaman akwae abunda ke damunshi ba kamar da ya wuto part d'inta bai tafi nashi yay wanka ya shirya ba kaman yadda ya saba,

"Any problem?" ta tambaya cike da kulawa, shiru ya danyi kafin ya gyara zama ya fara bata labarin Jamila da halin da suke ciki, lokacin daya gama da mamaki tace "Yanzu har akwae masu irin wannan matsalar a unguwar nan amman ban sani ba, ai yakamata ace sunzo neman taimako tunda mutum ba lallai ya sani ba" ta k'arasa da alamun damuwa akan fuskarta,
"Zai iya yuwuwa sunzo basu samu ganinki ba" jinjina kai tayi alamar gasgata zancenshi kafin tace "aikuwa zanyi ma su Officer Magana indae mutum ya nuna yana cikin matsala su rink'a bari yana samun ganin wani inda rabo sai kaga an taimaka" Haisam yace "Better" idonta akanshi tace "to amman kai ya akai kasan yarinyar ma?" gyara zamanshi yay kafin ya bata labarin itace yarinyar daya raba Fad'a da Zarah ranar daya fara ganinta,jinjina kai tayi tace "Allah gwanin hikima, shiyasa akeso duk wanda Allah ya had'a mutum dashi yay kokari yaga abun arziki ya shiga tsakani haka kuma in za'a rabu to ai rabuwar arziki, mutane sukan shigo rayuwarmu da yuwuwar akwae rabonmu a tare dasu ko kuma rabonsu a tare damu" jinjina mata kai yay alamar gasgata Maganarta taci gaba "Allah ubangiji ya bamu ikon taimakama junanmu a koda yaushe" a hankali ya furta "Amin" idonta akanshi tace "Yanzu ya kake ganin za'ai to?" dan watsa hannu guda yay yace "Kiyi duk abunda ya dace game da Lafiyar Dad din nata and asama masu inda zasu zauna sannan ita yarinyar tabar talla ta koma school sai aba Mom din nata enough Capital da zata yi business ko a gida" yana gama Maganar yasa hannu acikin Aljihun suit dinsa ya fito da Wallet dinshi Card ya ciro ya aje ma Hajiyar akan jikinta kafin ya maida Wallet d'in, Hajiya dake binshi da ido tace "kana nufin duk zaka yi wannan?" kai ya d'aga yace "yea a fara abunda ya dace in akwae bukatar cheque let me know", wani kallo tayi mashi kaman harara tace "to baka isa ka wawushe ladan kai kadae ba duk da kai ka kawo aikin ladan nima dole zanyi wani abu aciki" dan Murmushin gefe yayi kawae ya fara kokarin mikewa tace "ka tsaya to ka ci abinci mana sai ka wuce gaba d'aya ko" dakatawa yay yace mata yana son yaje yay wanka ne ya rage kayan jikinshi, hannu ta kai ta fara kokarin cire mashi rigar saman tana Fad'in "anan ma ai zaka iya rage kayan" bayan ta cire ta k'walama Saude kira tace ta kawo mashi abinci.

Washegari da Safe Hajiya da Tk suka je gidansu Jamila sam bai masu wuyar ganewa ba don Haisam ya fad'i mata jikin gidan Alhaji sani karofi filin da suke yake, lokacin da sukaje ba k'aramin tausaya masu tayi ba ganin halin da suke ciki ga Mahaifinnasu na jin jiki ba um ba umum don lalurar kwalwa yake fama da ita cikin nuna jimami Hajiya tace ma innar tasu miyasa bazasu zo su nemi taimako ba sai su barshi kwance a gida haka tace ma Hajiyar wllh sau wurin ukku tana zuwa bata samun ganinta shiyasa kawae sai ta hakuri da tunanin Alhaji sani zai taimaka masu tunda yasan da Maganar jinyar tashi kuma yace zai turo kud'in ai masa aikin don basu k'asar saidae har yanzu shiru amman dae ya turo masu wani abu saidae bazasu isa ayi aikin ba karshe ma abinci suka ci dasu, anan Hajiya ta tambayi inane za'ai masa aikin tace a Kano ne kuma kud'in aikin Miliyan 1 da dubu dari takwas ne Hajiyar tace ba wani abu su fara shirin kaishi aikin saboda tsabar farinciki innarsu Jamilan rushe ma Hajiya tayi da kuka ta kama kafafunta tana ta godiya da Addu'oi har saida kwalla suka taru a idanun Hajiyar ganin kan wasu yan kudi wanda ita a wurinta ba wani abu bane yasata farinciki har haka, (Allah Ubangiji ka bamu ikon sanya farinciki a zukatan junanmu Amin).

Bayan sati biyu
Cikin Nasara anyi mashi aikin Tk ne ya jagoranci tafiya kaishi aikin yanzu yana cigaba da shan Magani a sabon gidansu da Haisam ya siya masu wanda ke acan k'asan unguwar, gidan d'an madaidaici ne yana da d'akuna guda ukku biyu a jere sai daya a farkon shigowa yana da toilet aciki anan mahaifin nasu ke jinya akwae Kitchen mai d'an girma da toilet d'in tsakar gida, bawan Allah har yanzu bai fara yin Magana ba sai dae duk lokacin da aka ambaci su Hajiya sai yay ta zubar da hawaye wanda da gani na farinciki ne, Har gidan Haisam yazo ya dubashi a ranar innar Jamila ta fara ganinshi kuma shine wanda ta ta6a cema Jamila ta gani a gidan Hajiyar lokacin da suka je kar6ar tallafi, sosae tayi mashi godiya da Addu'oi harda kukanta sha6e sha6e shidae kai kawae yake d'aga mata yana fad'in ba wani abu, Jamila sai washe baki take tana farincikin ganinshi a gidannasu saida innar tasu ta tattaro yaran gaba d'aya tasa sukai mashi godiya kafin ya tafi.

Fatuu taci gaba da zuwa Makaranta tana a Science Class wato s.s one Sci A ita da Haulat farko ba class d'aya aka kaisu ba ita haulat Sci C aka kaita da taimakon Discipline master dinsu na Junior da Fatun taje tayi ma Magana yasa aka maido Haulat din Class dinsu.

AFTER 2 YEARS...............
Chapter 133 · 0% Book details