← Book details Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 122 OF 137

Sashe 122

Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 10 min read

.......Babban d'aki ne mai d'auke da abubuwan sarauta irin na gargajiya, lokacin data shiga zaune ta iskeshi akan kujerar da yake zama tare da wani babban Mutum yayi shiga ta alfarma yana zaune akan kujera daga gefen ardon da gani kuma wayayyan d'an boko ne kuma kana kallonshi zaka gane shima bafullatani ne, ard'on tsoho ne sosae don duk gashin fuskarsa hurhura ne ba bak'in gashi ko kwaya d'aya haka ma kanshi duk da a rufe yake gashi d'an tsamurmuri dashi wato baida jiki kwata kwata hakan kuma nada alak'a da tsufan da yayi sosae amman k'yam yake yana gani kuma yana ji amman dae tafiya saida sanda yake yi, da zasu shiga mino ce tayi sallama duk suka amsa harda mutumin ta duka k'asa kan shimfida ta gaishe dasu duk suka amsa ita kuwa Fatuu gaban ard'on ta nufa tayi mashi tsaye tana bin fuskarshi da kallo shima idonshi na akanta ya d'an k'ank'ance su da alama so yake ya gane wacece ita, haka shima wanccan mutumin da mino kallonsu suke, tambaya yayi wacece ita maimakon ta bashi amsa sai ce mashi tayi "wai har yanzun kana nan baka mutu ba?" da fullanci tayi Maganar jin hakan yasa nan take ya ganeta don kaf zuriyar gidan ba wanda zai iya mashi hakan in ba itan ba dama kuma yasan da zuwan nasu, hannu ya kai gefenshi ya janyo wata zungureriyar sanda zai buga mata ta ja baya da sauri tana dariya yace mata har yanzu shed'anun da ke kanta na nan kenan, tura mashi baki tayi yace ta girma amman har yanzu bata iya gaisuwa ba bata ga mutum ba in shi bazata gaidashi ba, juyawa tayi ta kalli Mutumin ta gaidashi ya amsa mata yana Murmushi sannan ta juya ta gaida ardon bai amsa mata ba sai ya nuna mata gabanshi yace ta zauna tace ai bugunta zaiyi yace bazai bugeta ba ai ita bak'uwa ce yanzu, zama tayi tana fuskantarshi yace to ta gaidashi yanzu bayan ta gaisheshi ne yace ta dawo ko tace a'a,
"Ai kuwa bazan bari ki koma ba aure zanyi maki kin yi girma da yawa" ya fad'a da fullanci cikin dusashshiyar murya ta tsufa, tura mashi baki tayi tace "na rantse ba mai mani aure sai nagama karatu na zama likita har na fara aiki sannan zanyi aure kuma ni zan za6i mijin ba wani ba" jinjina kai yay kafin yace zata gani in zai barta ta koman,wani kallo tayi mashi tace "in ka hana ba sai in gudu ba ai nasan hanya" shiru yay yana ta binta da ido da d'an Murmushi tace "an kawo maka tsarabar dana kawo, koda yake kai bazaka iya cin biscuit ko chocolate da wannan bakin naka ba daba hakora kaman na......" bata k'arasa ba ya k'ara d'ago sandar taja baya daga zaunen tana Fad'in ita fa yanzu budurwar birni ce tafi karfin a bugeta yace ta matso taga in bai bugetan ba, su dai su mino sai Murmushi suke, jin tace sai tagama karatu ta fara aiki ko zata yi aure yasa Mutumin ce mata "What's ur name?" kallon Mutumin da yayi mata tambayar tayi sai kuma ta bashi amsa itama da turancin cigaba da yi mata tambayoyi yay game da alakarta da ardon da inda take da kuma yanayin karatunta duk da turanci ta rink'a bashi amsa itama, sosae ya yaba da yadda take turancin ba wani gargada ko tangard'a har ya tambayeta a Katsinar private skul take yi ne tace mashi a government skul ce nan take ya fahimci tana da kokari sosae mino dai na gefe tana kallonsu suna turancin gwanin burgewa don tasan yaren da suke saboda tana zuwa makaranta itama saidae ba wani turanci take ji ba inba dan guntu ba kaman tambayar sunan mutum haka shima ardon yasan yaren nasara ne suke yi bayan sun gama ta juya ta kalli ardo da ya zuba mata ido tace "kai fa baka san mi muke cewa ba ko?" d'an Murmushi yay kafin yace "kin zama nasara bama wanda zai aure ki sai nasaran" da sauri tace "ai nima ban iya auren d'an garin nan don duk basu da ilimi basu iya komae ba sai noma da kiwo samarin birni kuwa irina suke so don haka in na tashi aure sai ma na za6a" ta k'arasa tana murmura mashi baki shidae Mutumin sai Murmushi yake can ardon yace ta tashi su shiga ciki yana tattaunawa da bak'o tace to kafin suka mik'e tare da mino suka nufi hanyar fita, Bayan sun fito waje ta nufa don taga in kawu Amadu na nan ya kira mata Ya Handsome, koda ta duba inda Kamalu ke saida rake bataga kowa ba baima fito da raken ba acan gefe ta hango Mota Jeep dake ajiye ta kalli mino tace Motar mutumin ce tace mata eh tace wanene shi Minon tace "Chairman ne Alhaji lawal shine mai katon gidan gonar bakin gari da ardo ke kulawa" d'an ta6e baki tayi kafin ta juya suka koma ciki ta nufi d'akinsu nan ma basu nan ba don taso ba suka koma cikin gidan ganin sun nufi hanyar 6angarensu yasa mino cewa "Adda Fatuu bazaki gaishe da yaya ba?" tura baki ta d'anyi sai kuma ta tuna da Maganar da suka yi da Haisam hakan yasa ta juya tace suje, lokacin da suka je sashen yayan wadda take uwargidan Ard'o tana zaune gefen gadon karfe babbar mata ce jajur da ita tana da tsaga a bakinta kuma tana da jiki ba laifi ta manyanta sosae daga gefe da gefenta mata ne zaune harda kishiyarta guda da kuma matan ya'yanta guda ukku su biyar kenan dama haka suke wuni wurinta suna mata fadanci aita gulmace gulmace, mino ce tayi sallama suka shiga ba tare da sun amsa ba duk suka d'ago suna kallonsu saidae gaba d'aya idanunsu na akan Fatuu ne itama ta lura da kallon da suke matan hakan yasa ta wani sha kunu don tasan bana arziki bane, k'asa mino ta tsugunna tana gaishe da yayar kaman an mata dole ta amsa kafin ta kalli Fatuu da tayi mata tsaye k'erere aka tace ita bata iya gaisuwa bane tayi Maganar tana k'are mata kallo tun daga sama har kasa dama tunda suka zo aka kawo mata gulmar yadda Fatun ta koma wai kaman yar shekara ashirin, gaida ita tayi kaman yadda ta bukata amman sai tak'i amsa mata wai a haka zata gaishe da ita ba ladabi abunda ake koya mata a binnin kenan rashin da'a, sai kace dama da Fatun na garin ladabin take mata, idonta cikin nata tace "to ai ba abun zama" fuska a d'aure tace su sauran a ina taga sun zauna tace "a k'asa ni kuma ban saba zama kasa ba ai" shiru tayi tana kallonta yayin da sauran suka hau jinjina kai alamar al'ajabi, d'an Murmushi da bakai zuci ba Yayan tayi tace ta manta itafa yanzu yar birni ce ta kalli mino ta nuna mata buzun salla tace ta d'aukko mata, shimfida mata tayi tace adda ki zauna cike da kyankyami tana d'an yamutsa fuska ta hau ta zauna suna dae ta bin ta da ido, ganin ta zauna bata gaishetan ba yasa Babar Altine data ta6a karyama kafar kaza cewa "to sai ki gaishetan ko!" wani kallo Fatun tayi mata dama itama sam basu shiri kafin ta kalli Yayan ta gaidata kasa kasa, d'an ta6e baki tayi ta amsa tace ya birnin ta bata amsa da lafiya lou daga haka kuma suka d'an yi shiru Fatun na kallon gefe yayin da Yayar ke k'are mata kallo can tace "amman kin dawo ne ko" ba tare data kalleta ba tace "a'a ai karatu nike" jinjina kai tayi sai kuma tace "amman yakamata yanzu ace kinyi aure har kin haihu ma" wani kallo ta juyo tayi mata mai kaman harara a d'an harzuke tace "ni ba wani aure da zanyi sai na gama karatu na fara aiki" gaba d'aya kowa kallonta yake da mamakin yadda take ma Yayar Magana, d'an Murmushi tayi bata ce mata komae ba ta kalli d'aya daga cikin matan dake zaune tace "Bimbi in kin gama dama furan ki zuba ma bak'uwar birni" Fatuu na jin hakan tace ta koshi don tasan ba har zuci tayi maganar ba, mik'ewa tayi tace ma Mino ta taso su tafi tayi masu sallama suka tafi, tana fita matan suka hau jinjina kai suna fad'in an idasa lalata yarinya kawae wata tace yo dama an kai yarinya birni ai dole ta lalace Allah ma yasa bata san maza ba don yadda take Magana tsaitsayen nan sai dae ace Allah ya kyauta kawae wata tace ai tabbas ma wannan tasan maza daga ganin jikinta, ita dae Yayan nata saurarensu Allah kadae yasan abunda take kullawa acikin ranta don gani take fatun ta wulak'anta tane duk da ba yanzu ta fara yi mata hakan ba amman tafi jin ciwo don tana ganin yanzu ai ta mallaki hankali. Duk yadda taso tayi Video call da Haisam ranar abun ya faskara don yinin ranar Amadu bai nan sun fita tare da kamalu basu suka dawo ba sai bayan Magrib saidae tayi waya dashi kawae, washe gari ya kama Monday kwanansu biyu da zuwa a ranar gwaggo taso komawa saboda aiki amman suka rok'eta ta d'an k'ara ko kwana biyu ne cikin masu rok'on nata harda Fatuu kaman zata yi mata kuka hakan yasa ta hakura sai ranar laraba zata tafi, ranar da yamma tana sanye cikin Jallabiya ta d'aura kallabi akanta ta nufi kopar gida tana zuwa ta iske Amadu zaune saman benci gaban teburin raken Kamalu, gaidasu tayi tace don Allah ya kira mata Ya Handsome video call yace dama yasan ba gaisuwar Allah da Annabi bace to bai kira, rokonshi ta fara yi harda tsugunnawa k'asa Kamalu dae nata dariya don yar tsamarsu burgeshi take, saida ya gama ja mata rai sannan ya kirashi ya bata ta sanar mashi zasu yi Video call din bayan ya d'auka ta gaidashi ta sanar mashi ya amsa da owk, mik'a ma Amadu wayar tayi tana ta faman washe baki ya fara kokarin kiran nashi sai dae da yayi connecting sai kuma yayi disconnecting da kyar ya samu yayi ya mik'a mata, ta fara murnar ganin haisam d'in kenan kiran ya datse rai 6ace ta sanar ma Amadun yace to sai tayi hakuri ba network mai kyau, rokonshi ta fara yi ya daka mata tsawa yace to shine zaisa shi yayi, Kamalu yace in suna son network sai sunje bakin gari acan ake samu ta fara rok'on Amadun ya bata wayar taje can tayi, wani kallo yayi mata yace "matsalata dake baki da cikakken hankali nine zan baki wayata kije bakin gari salon a kwace man waya ko" Kamalu na dariya yace " a'a mu garinmu ba'a kwacen waya wama yasan yadda zai yi amfani da ita balle ya kwace ai sai d'aid'aikun Mutanan da yawanci ma ba a garin suke zaune ba" jin haka ta hau yi mashi magiya da k'yar ya bata yana jaddada mata tabi mai waya a hankali ta amsa da to cike da zumudi ta juya da gudu ta nufi bakin garin Amadun ya d'aga murya yana karfa ta fasa mashi waya, yar tafiya ce tayi ta isa wurin cikin sa'a tana kiran nashi yayi lafiya lou lokacin haisam d'in na kishingide kan gado tana ganinshi ta washe baki ta kira sunanshi, amsa mata yayi yace tana lafiya tace lafiya lou, "Ya Handsome ka koma Katsina ne?" girgiza mata kai yay tace "har yanzu kana Lagos d'in kenan" yace "Yeah ban gama abunda nazo yi ba sai tomorrow zan tafi,
"to yanzu kana ina na ganka kwance ko Hotel?" girgiza mata kai yay "Nah" ta k'ara cewa to yana ina yace yana gidan Mommynshi ta Lagos tace mai auren Bature ya d'aga mata kai alamar eh wai harda cewa ina yake ta ganshi yace bai Nigeria, fira suka ci gaba da yi harda ce mashi wllh tayi missing d'inshi shima yayi nata yayi mata Murmushi kawae, can tace "Yauwa Ya Handsome don Allah jibi gwaggo zata taho kace ta taho dani pls" da d'an Murmushi ya girgiza kai yace "why, ba already kun gama magana ba" turo baki tayi sai kuma tace "to kai ka biyo ka d'aukeni" yace mata ai ba'a Mota zai dawo ba tace a jirgi yace eh,
Chapter 122 · 0% Book details