Sashe 19
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haisam na fitowa daga part d'in Hajiya ya nufi Part d'insa yana amsa wayan da aka kira shi,a daidai stairs din balcony ya gama wayan,tura kofa yayi ya shiga cikin parlon ya zauna kan kujera hadi da daukar Remote yayi powering tv On,ya d'an kishingida yaci gaba da kallon American film d'in da yake kallo a MBCMAX, bayan wani d'an lokaci ya dau wayarsa ya duba time,sake d'aukan remote yayi yai Offing tv sannan ya mik'e ya nufi bedroom.
Sanye cikin Sportswear ya fito,red t-shirt da wandonta black daga gefen hagu na rigan na dauke da tambarin ADIDAS wanda akayi da bakar sak'a haka wandon ma adai dai gefen da akayi rubutun rigan shima akayi da jar sak'a daga k'asa yad'an matse,ba k'aramin kyau yayi cikin shigan kayan ba,kuma da ganin laushin kayan tabbas zasu yi kudi,saida ya tsaya yasa takalma a corridor kafin ya iso cikin parlon ya dau wayansa ya fice zuwa masallaci wanda liman ke ta kwalla kiran sallah,
Tare da su Uncle Mani ya fito bayan angama sallan la'asar d'in ya nufi cikin parking space don fiddo da Bike d'insa bayan yayi ma T.k da ya fito daga masallaci bayan sun fito umarnin ya daukko masa jakarsa kaman jiya,
Uncle Mani ya nufi part d'in Hajia don yi mata sallama su kuma su Alhaji Sa'idu suka tsaya gefen motar da suka zo da ita suna jiran ya dawo gaba daya hankalinsu na kan Haisam daya fiddo bike d'in cikin harabar ya haye yana kokarin sa helmet,adai dai lokacin da t.k ya kusa k'arasowa da jakar,
Hajiya da Kawu Mani suka fito suka nufo parking space din,Kawu Mani dake ta kallon Haisam tunda suka fito ya fara magana"Yanzu Hajjaju shima Haisam na hawa irin mashin d'in nan? Hajia ta ta6e baki tace " Unn" adaidai lokacin da suka k'araso wurin su Alhaji Sa'idu ya kunna mashin d'in gaba daya suka toshe kunnuwansu da hannayensu da sauri,haisam ya d'an juyo ya d'aga ma Uncle Mani hannu alamar yana masa sallama bai jira ya maido masa ba yaja mashin din da gudu ya tunkari gate d'in da tuni an wangale masa shi.
Uncle Mani ya sauke ajiyar zuciya bayan Haisam ya fice yace"I don't know what's wrong with our Youths,abu mai had'ari shi suke mayarwa abun adon su,and what really baffle me with them shine duk irin mummunan had'arin da mashin d'innan ke haddasawa hakan bai serving dinsu misali su daina hawan...Alhaji Sa'idu ya kar6e"Sam basu bi dashi yadda yadace ne,haka zaka ga suna ta falla uban gudu kai kace zasu kiyama..."Mutumin na karshe ya katse shi da cewa"Ai wasu kam kiyaman suke tafiya wllh sam basu la'akari da irin titinan mu ba kaman na waje bane,su yi ta tuk'in ganganci,gashi naji ance mashin d'in tsada ne dashi sosae..."Hajiya dake tsaye hannuwanta goye a bayanta ta amsa "tsada kam! Miliyan biyar ya zuba kafin ya mallaki wannan nasan..."gaba daya suka zaro ido a tare suka maimaita kudin da hajiyan ta fad'a,ita kam kai ta jinjina masu Uncle Mani yace "to Allah ya kyauta,Allah ya k'ara tsarewa,gaba d'aya suka amsa da Amin" daga haka ya kalli hajia da d'an murmushi yace "to hajjaju mu zamu wuce sai wani lokaci kuma in Allah yasa rayuwarmu ta kai" hajia tayi murmushi tace"To Allah yasa rayuwar tamu ta kai" ta fiddo hannayenta dake goye a bayanta ta mik'a ma Alhaji Sa'idu kud'i dake cikin hannunta na dama da fara'a tace"gashi ayi ma iyali tsaraba nagode da ziyara,Allah yabar zumunci" hannu biyu yasa ya kar6a harda d'an russunawa suna ta godiya shida dayan,Uncle Mani yace"To ni hajjaju ba'a sallame ni ba" dariya tayi tace banda kai ai sune bak'i na, kai na gida ne" shima dariyar yake ya bud'e mota yace"ba wani abu nasan tawa sallamar babba ce tafi karfin hannu k'ilan,zan turo Account details" daga haka ya shige Abokan tafiyarma suka shiga suna ta kara godiar rafar 50k da hajia ta basu cike da farinciki hannu ta d'aga masu bayan sun fita daga cikin parking space din tace"Agaida Iyali",daga haka ta juya ta koma ciki.
Tunda ta shige gida take kunshe a daki,bayan tayi sallar Azahar bacci yayi awon gaba da ita,ko Uniform d'in bata cire ba,bugun kofar da ake tayi ne ya farkar da ita a tsorace ta fito daga d'akin tana tafiya cikin sand'a har Lokacin kuma ana ta buga kofar da k'arfi,tsayawa tayi cikin zauren tana tunanin waye ke buga kofan haka? kodai mai Motar ne ya kawo k'ara,ji tayi gabanta yayi mugun fad'uwa nan take tsoro ya kama ta tace a ranta "to ya akai yasan gidanmu bayan lokacin da na jefi motan ba kowa wurin..." wani bugu aka yima k'ofar wanda daji mai buga kofan ya k'ule yasa ta tunkari kofar da sauri ta d'an leka idonta d'aya ta ramin makulli nan take ta gane waye da sauri takai hannu sama ta cire sakatan sannan ta d'an ja baya,aikam da karfi aka bugo kofan don da bata matsa ba daba k'aramin buguwa zatai ba,rai a6ace yake kallonta Kawu Amadu ne hannunshi daya rungume da kwali d'ayan kuma katuwar leda ce,Fatuu dake ta faman zare ido tace "sannu da zuwa Kawu Amadu...."da sauri ya katseta da fad'in "sannu da zuwan uwarwa,don iskanci daman kina cikin gidan kika barni inata bugun k'ofa tsawon lokaci,to waima uban me kike a cikin gidan daba zaki zo ki budan ba? d'an turo baki tayi tace "ba komai,bacci ne ya d'auke ni fa" a harzuk'e yace"to miye na kulle kofa don zaki yi bacci" da sauri tace "ina gudun kar a shigo ayi sata ne ina baccin...." "k'arya kike" yace yana k'are mata kallo kafin yaci gaba "fad'a kika jawo ko? Da sauri ta girgiza kai alamar a'a,kwafa yayi yace "ai na dawo gidan inma rigima ki ka jawo zan gani,kuma uban miye na zama da Uniform har yanxu a jiki da alama ma ko wanka baki yi ba,bare kiyi sallah" ya k'arasa maganar yana kokarin aje kayan hannunsa a bakin kofa,d'agowa yayi ya daka mata tsawa"wuce kije ki wanka kafin na buge ki a wurin" juyawa tayi ta nufi cikin gida tana d'an k'unk'uni har ta nufi d'aki taji yace"bakiji mi nace kiyi bane? Da sauri tace "naji.." yace"to wuce ki dau bokiti ki d'ibi ruwa" ta wuce ta xuba ruwan ta shige band'aki,shima yana shiga wankan yayi a d'an band'akin cikin d'akin nasa ya shirya ya kwashi kayan da ya siyo ya nufi shago don jera su.
Sai can bayan Issha gwaggo ta dawo,fatuu dai na k'unk'ume a d'aki cike da zullumin kar akawo k'ararta, koda ta fito tayi ma gwaggon sannu da zuwa dakin ta koma ita kam gwaggo a gajiye take hakan yasa ko ta kan Fatuu bata bi ba balle har ta fahimci wani abu,sai can dare gwaggo tayi bacci sannan ta fito taci abinci tayi sallah ta koma ta kwanta tare da yankewa ranta cewa baza'a kawo k'arar tata ba tunda har aka kai wannan lokacin.
Washe gari asabar da safe Fatuu ce da Haulat zaune cikin ajin su na islamiyya,Haulat ta kalli Fatuu da murmushi tace"sannu hajiyar fad'a" wata yar dariyar iskanci fatuu tayi tace "waya ce maki nayi fada" d'an ta6e baki Haulat tayi tace "har gida akazo aka fad'a mana irin fadan da kuka yi, wai har kin fasa ma Murja baki da hanci" murmura idanu Fatuu tayi tace"Yessss,gobe ma ta k'ara gaya man banzan maganganu harta kirani da yar kauye" girgiza kai haulat tayi tace"ni wllh don kince Gwaggo bata nan amman a lokacin da sai na kai k'arar ki tunda ke dai baki da hakuri" harararta Fatuu tayi tace "aida da ta dawo kinzo kin kawo k'arartawa sarkin masu hakurin duniya" haulat tace "tunda ya rigada ya wuce miye na inzo,Amman ai naji ance wani mutum ne yayi maganinki da ki ka k'i barin fadan ya wanka maki mari" ta kai maganar tana tik'ar daria,wata yar iskar dariya Fatuu ta sake yi tace"hehehe ashe yai maganina,muka dai yi maganin juna don shima yayi asara ehe" haulat ta dakata da dariyar da take tace "what do you mean da ku kai maganin juna?wace irin asara kuma? Fatuu ta gyad'a kai da turancin ta na yar sakandire tace "what u hear" Still haulat tayi tana ta kallonta can tace "don Allah Fatuu fad'a man abunda kika yi masa" fatun na shirin yin magana Malaminsu ya shigo hakan yasata yin shiru daga nan kuma basu sake samun daman yin magana ba don yana fita wani ma ya shigo a haka har aka tashi,akan hanyar su ta komawa gida Haulat tace "d'azun na tambaye ki mi kika yiwa Mutumin baki gaya man ba" banza fatuu tayi mata,haulat ta sake cewa "kinji,mi kika yi masa ne" ba tare data kalleta ba tace"ke dalla bafa komai,wasa nike,ba abunda nayi masa kawai don kar kiyi tunanin yayi nasara akaina ne" haulat tace "kawai dai bazaki fadan bane Amman ko nayi rantsuwa ba zanyi kaffara ba tunda kika ce yayi asara da akwai abunda kika yi masa...." cikin tsiwa tace "ehh d'in nayi, tunda ba ki yarda ba abunda nayi masa ba" shiru haulat tayi amman ba don ta yardan ba,can tace "to ki kar6i jakar ki ko,kince in taho maki da ita kuma kin barni inata kayanta" juyowa Fatuu tayi ta figi jakar ba ko nagode tayi gaba abunta sai wurga kafa take da alama dai ta saba da yin tafiya haka,girgiza kai haulat tayi tace daga abun arziki,tabi bayanta har suka zo bakin lungun da suke rabuwa,haulat ta d'an daga murya tace "sai munhade Anjima hajia Fatuu ikon Allah" Fatuu ta juyo tayi mata kallon up and down ta k'ara gaba,Haulat dai dariya tayi a fili tace"Allah ya shirye ki" daga haka ta nufi hanyar gidansu, adai dai kofar shiga gida fatuu ta waiga tana kallon hanyar da haulat ta bi a fili tace "don ina sakarya Allah ya rufa man asiri in tona ma kaina,don na tabbata na fad'i mata sai ta fad'a ma gwaggo ko kuma tayi ta ma mutane nasihar banza ita ga mai hakuri yen-yen-yen" ta d'age baki daga haka ta shige gida.
Sanye cikin Sportswear ya fito,red t-shirt da wandonta black daga gefen hagu na rigan na dauke da tambarin ADIDAS wanda akayi da bakar sak'a haka wandon ma adai dai gefen da akayi rubutun rigan shima akayi da jar sak'a daga k'asa yad'an matse,ba k'aramin kyau yayi cikin shigan kayan ba,kuma da ganin laushin kayan tabbas zasu yi kudi,saida ya tsaya yasa takalma a corridor kafin ya iso cikin parlon ya dau wayansa ya fice zuwa masallaci wanda liman ke ta kwalla kiran sallah,
Tare da su Uncle Mani ya fito bayan angama sallan la'asar d'in ya nufi cikin parking space don fiddo da Bike d'insa bayan yayi ma T.k da ya fito daga masallaci bayan sun fito umarnin ya daukko masa jakarsa kaman jiya,
Uncle Mani ya nufi part d'in Hajia don yi mata sallama su kuma su Alhaji Sa'idu suka tsaya gefen motar da suka zo da ita suna jiran ya dawo gaba daya hankalinsu na kan Haisam daya fiddo bike d'in cikin harabar ya haye yana kokarin sa helmet,adai dai lokacin da t.k ya kusa k'arasowa da jakar,
Hajiya da Kawu Mani suka fito suka nufo parking space din,Kawu Mani dake ta kallon Haisam tunda suka fito ya fara magana"Yanzu Hajjaju shima Haisam na hawa irin mashin d'in nan? Hajia ta ta6e baki tace " Unn" adaidai lokacin da suka k'araso wurin su Alhaji Sa'idu ya kunna mashin d'in gaba daya suka toshe kunnuwansu da hannayensu da sauri,haisam ya d'an juyo ya d'aga ma Uncle Mani hannu alamar yana masa sallama bai jira ya maido masa ba yaja mashin din da gudu ya tunkari gate d'in da tuni an wangale masa shi.
Uncle Mani ya sauke ajiyar zuciya bayan Haisam ya fice yace"I don't know what's wrong with our Youths,abu mai had'ari shi suke mayarwa abun adon su,and what really baffle me with them shine duk irin mummunan had'arin da mashin d'innan ke haddasawa hakan bai serving dinsu misali su daina hawan...Alhaji Sa'idu ya kar6e"Sam basu bi dashi yadda yadace ne,haka zaka ga suna ta falla uban gudu kai kace zasu kiyama..."Mutumin na karshe ya katse shi da cewa"Ai wasu kam kiyaman suke tafiya wllh sam basu la'akari da irin titinan mu ba kaman na waje bane,su yi ta tuk'in ganganci,gashi naji ance mashin d'in tsada ne dashi sosae..."Hajiya dake tsaye hannuwanta goye a bayanta ta amsa "tsada kam! Miliyan biyar ya zuba kafin ya mallaki wannan nasan..."gaba daya suka zaro ido a tare suka maimaita kudin da hajiyan ta fad'a,ita kam kai ta jinjina masu Uncle Mani yace "to Allah ya kyauta,Allah ya k'ara tsarewa,gaba d'aya suka amsa da Amin" daga haka ya kalli hajia da d'an murmushi yace "to hajjaju mu zamu wuce sai wani lokaci kuma in Allah yasa rayuwarmu ta kai" hajia tayi murmushi tace"To Allah yasa rayuwar tamu ta kai" ta fiddo hannayenta dake goye a bayanta ta mik'a ma Alhaji Sa'idu kud'i dake cikin hannunta na dama da fara'a tace"gashi ayi ma iyali tsaraba nagode da ziyara,Allah yabar zumunci" hannu biyu yasa ya kar6a harda d'an russunawa suna ta godiya shida dayan,Uncle Mani yace"To ni hajjaju ba'a sallame ni ba" dariya tayi tace banda kai ai sune bak'i na, kai na gida ne" shima dariyar yake ya bud'e mota yace"ba wani abu nasan tawa sallamar babba ce tafi karfin hannu k'ilan,zan turo Account details" daga haka ya shige Abokan tafiyarma suka shiga suna ta kara godiar rafar 50k da hajia ta basu cike da farinciki hannu ta d'aga masu bayan sun fita daga cikin parking space din tace"Agaida Iyali",daga haka ta juya ta koma ciki.
Tunda ta shige gida take kunshe a daki,bayan tayi sallar Azahar bacci yayi awon gaba da ita,ko Uniform d'in bata cire ba,bugun kofar da ake tayi ne ya farkar da ita a tsorace ta fito daga d'akin tana tafiya cikin sand'a har Lokacin kuma ana ta buga kofar da k'arfi,tsayawa tayi cikin zauren tana tunanin waye ke buga kofan haka? kodai mai Motar ne ya kawo k'ara,ji tayi gabanta yayi mugun fad'uwa nan take tsoro ya kama ta tace a ranta "to ya akai yasan gidanmu bayan lokacin da na jefi motan ba kowa wurin..." wani bugu aka yima k'ofar wanda daji mai buga kofan ya k'ule yasa ta tunkari kofar da sauri ta d'an leka idonta d'aya ta ramin makulli nan take ta gane waye da sauri takai hannu sama ta cire sakatan sannan ta d'an ja baya,aikam da karfi aka bugo kofan don da bata matsa ba daba k'aramin buguwa zatai ba,rai a6ace yake kallonta Kawu Amadu ne hannunshi daya rungume da kwali d'ayan kuma katuwar leda ce,Fatuu dake ta faman zare ido tace "sannu da zuwa Kawu Amadu...."da sauri ya katseta da fad'in "sannu da zuwan uwarwa,don iskanci daman kina cikin gidan kika barni inata bugun k'ofa tsawon lokaci,to waima uban me kike a cikin gidan daba zaki zo ki budan ba? d'an turo baki tayi tace "ba komai,bacci ne ya d'auke ni fa" a harzuk'e yace"to miye na kulle kofa don zaki yi bacci" da sauri tace "ina gudun kar a shigo ayi sata ne ina baccin...." "k'arya kike" yace yana k'are mata kallo kafin yaci gaba "fad'a kika jawo ko? Da sauri ta girgiza kai alamar a'a,kwafa yayi yace "ai na dawo gidan inma rigima ki ka jawo zan gani,kuma uban miye na zama da Uniform har yanxu a jiki da alama ma ko wanka baki yi ba,bare kiyi sallah" ya k'arasa maganar yana kokarin aje kayan hannunsa a bakin kofa,d'agowa yayi ya daka mata tsawa"wuce kije ki wanka kafin na buge ki a wurin" juyawa tayi ta nufi cikin gida tana d'an k'unk'uni har ta nufi d'aki taji yace"bakiji mi nace kiyi bane? Da sauri tace "naji.." yace"to wuce ki dau bokiti ki d'ibi ruwa" ta wuce ta xuba ruwan ta shige band'aki,shima yana shiga wankan yayi a d'an band'akin cikin d'akin nasa ya shirya ya kwashi kayan da ya siyo ya nufi shago don jera su.
Sai can bayan Issha gwaggo ta dawo,fatuu dai na k'unk'ume a d'aki cike da zullumin kar akawo k'ararta, koda ta fito tayi ma gwaggon sannu da zuwa dakin ta koma ita kam gwaggo a gajiye take hakan yasa ko ta kan Fatuu bata bi ba balle har ta fahimci wani abu,sai can dare gwaggo tayi bacci sannan ta fito taci abinci tayi sallah ta koma ta kwanta tare da yankewa ranta cewa baza'a kawo k'arar tata ba tunda har aka kai wannan lokacin.
Washe gari asabar da safe Fatuu ce da Haulat zaune cikin ajin su na islamiyya,Haulat ta kalli Fatuu da murmushi tace"sannu hajiyar fad'a" wata yar dariyar iskanci fatuu tayi tace "waya ce maki nayi fada" d'an ta6e baki Haulat tayi tace "har gida akazo aka fad'a mana irin fadan da kuka yi, wai har kin fasa ma Murja baki da hanci" murmura idanu Fatuu tayi tace"Yessss,gobe ma ta k'ara gaya man banzan maganganu harta kirani da yar kauye" girgiza kai haulat tayi tace"ni wllh don kince Gwaggo bata nan amman a lokacin da sai na kai k'arar ki tunda ke dai baki da hakuri" harararta Fatuu tayi tace "aida da ta dawo kinzo kin kawo k'arartawa sarkin masu hakurin duniya" haulat tace "tunda ya rigada ya wuce miye na inzo,Amman ai naji ance wani mutum ne yayi maganinki da ki ka k'i barin fadan ya wanka maki mari" ta kai maganar tana tik'ar daria,wata yar iskar dariya Fatuu ta sake yi tace"hehehe ashe yai maganina,muka dai yi maganin juna don shima yayi asara ehe" haulat ta dakata da dariyar da take tace "what do you mean da ku kai maganin juna?wace irin asara kuma? Fatuu ta gyad'a kai da turancin ta na yar sakandire tace "what u hear" Still haulat tayi tana ta kallonta can tace "don Allah Fatuu fad'a man abunda kika yi masa" fatun na shirin yin magana Malaminsu ya shigo hakan yasata yin shiru daga nan kuma basu sake samun daman yin magana ba don yana fita wani ma ya shigo a haka har aka tashi,akan hanyar su ta komawa gida Haulat tace "d'azun na tambaye ki mi kika yiwa Mutumin baki gaya man ba" banza fatuu tayi mata,haulat ta sake cewa "kinji,mi kika yi masa ne" ba tare data kalleta ba tace"ke dalla bafa komai,wasa nike,ba abunda nayi masa kawai don kar kiyi tunanin yayi nasara akaina ne" haulat tace "kawai dai bazaki fadan bane Amman ko nayi rantsuwa ba zanyi kaffara ba tunda kika ce yayi asara da akwai abunda kika yi masa...." cikin tsiwa tace "ehh d'in nayi, tunda ba ki yarda ba abunda nayi masa ba" shiru haulat tayi amman ba don ta yardan ba,can tace "to ki kar6i jakar ki ko,kince in taho maki da ita kuma kin barni inata kayanta" juyowa Fatuu tayi ta figi jakar ba ko nagode tayi gaba abunta sai wurga kafa take da alama dai ta saba da yin tafiya haka,girgiza kai haulat tayi tace daga abun arziki,tabi bayanta har suka zo bakin lungun da suke rabuwa,haulat ta d'an daga murya tace "sai munhade Anjima hajia Fatuu ikon Allah" Fatuu ta juyo tayi mata kallon up and down ta k'ara gaba,Haulat dai dariya tayi a fili tace"Allah ya shirye ki" daga haka ta nufi hanyar gidansu, adai dai kofar shiga gida fatuu ta waiga tana kallon hanyar da haulat ta bi a fili tace "don ina sakarya Allah ya rufa man asiri in tona ma kaina,don na tabbata na fad'i mata sai ta fad'a ma gwaggo ko kuma tayi ta ma mutane nasihar banza ita ga mai hakuri yen-yen-yen" ta d'age baki daga haka ta shige gida.