Sashe 40
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nannauyar ajiyar zuciya gwaggo ta sauke cike da takaici tace"kai jama'a duniya dai ta idasa lalacewa yanzu ace kaman Ashiru yasan ya hakkewa mace,yanzu dai indai kana da yaya mata agabanka baka da kwanciyar hankali wllh masifar fyaden nan tayi yawa kullum gargadi ake nasiha ake amman a banza abun sai kara gaba yake na jiki ma sai ya cutar maka da y'a,Allah kai mana maganin wannan masifa ka shiryi al'ummar Annabi..." ladidi ta amsa"S.a.w,ke dai bari Dije Amin ya Allah,ni wllh malam tanimun ma ke bani tausayi shi kuma ta nan Allah ya jarabe shi gashi malami" gwaggo tace"wllh ai abun a tausaya masa ne jarabawar ya'ya ai babbar jarabawa ce mutum baida yadda zaiyi dole ya rungumeta har Allah ya yaye inda rabo,Allah ka shirya mana zuria shirin addinin musulunci",
"Amin" ladidi ta amsa tana kokarin mikewa tace"na tsaida ki zaki tafi aiki ga lokaci nata tafiya" mik'ewa itama Gwaggon tayi tana fadin"to daman dai wani lokacin dole ai uzuri yasa ka makara kaman yadda wani lokacin kaima ba'a zuwa a amshe ka da wuri saboda wani dalilin haka dai ake ta fama" yar dariya ladidi tayi"hakane kam rayuwan gaba daya sai da uzuri,ku kunma ji dadi kunata aikin ku wllh kai bawa kullum sai fama da wuta kake" gwaggo tace"to ya za'ai kowa da hanyar da Allah ya tsaga masa cin abincinsa,Allah dai ya kara rufa mana asiri duniya da lahira" ladidi ta amsa da Amin yayin da suka nufi hanyar zaure a tare,
Da sauri fatuu ta koma gefen d'an gadonta ta zauna daga inda ta la6e tana sauraron hirarsu gwaggo,hannu tasa ta ruke ha6arta a fili tace"kai,wai yaya handsome har yasa an kama su gaye kenan" kwafa tayi ta sake cewa"ai maganinsu kenan mugaye kawai,kilan ma su za'a kai gidan yarin ba ni ba,wayyo har naji tausayin Gaye wllh shi baiso ba amman abokanansa sun ja masa" idasa fadawa tayi saman gadon ta kwanta tana kallon sama ta ci gaba"yakamata inje in gaida Yaya handsome tunda saboda ni yaji ciwo,ko yama akai yasan naje kangon nan,kilan yagan sanda na juya nabi lungun ne,ashe dai haka yake da mugun kirki ni wllh farkon dana fara ganinshi nayi tunanin baida mutunci ba kaman daya falla mun marin nan" kyalkyacewa tayi da dariyar farinciki kafin tace"ai da har naji tsoron ko yana can bai iya tafiya ne shiyasa ban ganshi da safe ba,ashe har wurin yan Sanda yaje ya kai kara,ohooo shiyasa yace kar na fadi ma kowa abunda ya faru nagano dalilin...,Oh da ansan nice da sai aita nuna ni wasu ma su ki yarda ba ai man fyaden ba,gwara ma da ba wanda yasan ni ce"ta k'arasa maganar tana ta faman watsa hannuwa kaman da wani take maganan,
"Fatuu" gwaggo da ta dawo daga rakiyar da tayi ma ladidi ta kwala mata kira,da sauri ta saukko daga gadon ta nufi kopa tana amsa kiran,d'aga labulan tayi ganin gwaggon a bakin kopan yasa ta tsaya tace"gani" kallon kanta gwaggon tayi wanda ke bude ba dankwali ta d'an girgiza kai tace"wai ke don Allah fatuu sai yaushe ne zaki hankali,kisan abunda ya dace ne iye?yanzu wannan kan naki tun yaushe yake a tsefe ne,kudi fa kawai zaki dauka kije a kitse maki amman abun duniya ya gagara so kike sai na kama hannunki naje na kaiki ne?" turo baki fatuu tayi"Allah gwaggo bazaki gane ba fa,wllh balaraban nan mugun zafin hannu gare ta,kitson da tayi man na karshe fa har dan guntun fitsari sai da nayi fa" ta6e baki gwaggo tayi tace"wannan kuma ai kin saba in dai sakin fitsari ne,kullum mutum bazai yi abu lokacin da yake jin sa ba sai ya matse shi ba dole ya zubo ba,ke dai kika sani,gashin ma naki bai da zuciya ne yadda baki gyara shin nan kamata yayi ace zuwa yanzu duk ya zube ya bar ki da kwaikwaidon kai",
Langa6ar da kai tayi tana turo baki"kai gwaggo harda mugun fata,to ke ki mun ko kalaba ko kuma ki man na fulani da kike man" gwaggo tace"Uhmm sai ki ta jira na ai har in samu lokaci,nasan hakan ba matsala bane a wurinki,kinga ni zan wuce wurin aiki nama rigada na makara,ga abinci nan a kicin in Amadu ya dawo ki dau nasa ki kai masa,sannan kema in kin ci kiyi wanka sai ki share tsakan gidan da kuma kicin din don duk ya 6aci ban samu na gyara ba" daga haka ta juya can kuma sai ta sake juyowa tace"fatuu na roke ki don Allah ki zauna agida kar kije ko ina da lokacin islamiyya yayi ki tafi ana tasowa kuma ki dawo gida kinji?,
d'an sosa kai tayi"to,amman zan dan je gidan hajia in nagama abunda kika sani kafin lokacin islamiyyar yayi" wani kallo gwaggon tayi mata kafin tace"wai mi kike yi ne a gidan hajiyar ba jiya kinje ba kuma ma da dare,to mi kuma zaki je yi yanzu?anya fatuu ba wata rigimar kike shirin jawo man ba kike fakewa da zuwa gidan hajia?" da sauri ta girgiza kai tace"Allah ni ba wani rigimar da zan jawo maki,yaushe rabon ma da kiji an kawo karata,kawai banson in zauna ni daya shiru tunda kinga shi kawu Amadu da ya dawo ya dan huta shago zaije ya bude" ta6e baki gwaggon tayi"ai jin shirun ba'a kawo k'arar taki ba kwana biyu yasa ni nike zullumi don in kikai kwance kwancen nan to ba k'araman rigima za'a jawo man ba",
kyalkyacewa da daria fatuu tayi tace"to ki kwantar da hankalinki kakus ba wani rigiman da zan jawo na bari na shiryu ba ruwana yanzu" gwaggo tace"da nafi kowa farin ciki,sai dai nasan a iya baki ne don nasaba jin hakan" daga haka ta juya ta nufi hanyar fita fatuu ta d'an daga murya"inje ko? batare da gwaggo ta juyo ba tace"ai sai kita zuwa ko na hana ma nasan sai kinje" fatuu da ke ta dariya da karfi tace"si to a warti kakus" hannu gwaggon ta d'ago mata lokacin kuma ta idasa ficewa daga gidan,fatuu na ganin ta fice ta koma d'aki da sauri don daukko gyalenta dan gado ta tafi gidan hajiyar Sanata.
*💖ASANADIN MAKWABTAKA💖*
_A heart touching love story._
_*BY ZAINAB LALUH📲*_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
*32⃣*
Fitowa tayi da sauri tana yafa gyalen saman uniform din jikinta,a daidai zaure suka had'e da kawu Amadu ya dawo daga Makaranta shima,wani kallo yayi mata yace"yawo ko?" Da sauri ta girgiza mashi kai"a'a gidan hajiya zani kuma na tambayi gwaggo ma yanzun nan ta fita" gyada kai yayi yace"eh na hadu da ita,mashin d'in da ya kawo ni ma ta hau,yanzun je ki kawo man abinci na sai kita tafiya" to tace ta juya don daukko masa abincin,
Yana zaune agefen yar katifarsa yana cire safar kafarsa ta shigo,aje masa yar kular abincin da cokali asamanta tayi a gabansa tace"gashi nan" tana k'okarin juyawa yace"ruwa fa?"wani kallo tayi masa tana turo baki "kai kawu wai ruwan ma baka iya zuwa kasha in ka gama don kawai ka wahalar dani" harararta yayi cikin d'aure fuska yace"Imi fijirma(ina wasa dake)!zaki kawo man ruwan ko sai na tattaka ki anan,kin iya jin wahalan asa ki yin abu amman baki jin wahalan yawo"tana ta faman turo baki ta koma ta d'ebo masa ruwan ta kawo masa,yar harara ya watsa mata kafin yasa cokali ya fara cin abincin,juyawa tayi zata fita ta hango kwali d'auke da su biscuits dasu sweet aje a jikin bango, d'an juyowa tayi ta saci kallonsa taga hankalinsa na kan abincin da sauri tasa hannu ta rarumo sweet jin karar ta6a kwalin yasa shi dagowa da sauri yace'Fatuu...."da gudu ta fice daga gidan.
________________
Haisam zaune a parlornsa hannunsa ruke da wayarsa yana karatun Al'qurani a hankali ta cikin app d'in Vmuslim,tun bayan da suka dawo shi da Officer direct part din hajiya ya nufa don yin breakfast yasha magungunan da aka bashi,anan ne taga raunin daya ji a kafan,ba k'aramin tashi hankalinta yayi ba taita faman tambayan shi yadda ya samu rauni bacin jiya lafiya lou suka rabu,bai 6oye mata ba ya fad'i mata kwalba ce ya taka amman a part d'in sa yace mata bai fad'i mata ainihin yadda akai ya samu raunin ba,aikam ba k'aramin jimami ta shiga ba mamaki ya cikata na yadda akai akasamu kwalba apart dinsa har ya taka don tasan ko lemun kwalba basu amfani dashi haka dai taita faman jajanta al'amarin,da kanta ta had'o masa breakfast har yunkurin bashi a baki tayi ya hanata yana ta faman dariya,tsare shi tayi sai da ta tabbatar yaci sosae sannan ta 6allo masa magungunan yasha,ci gaba su kai da hira har ya tambayeta miyasa bata je aiki ba,ta sanar mashi cewa tana aikin wani project ne sai ta gama gaba daya sannan zata je,bayan wani lokaci ne hajiyan tayi bak'i hakan yasa haisam din baro part din hajiar,har cewa tayi yaje dakinta ya kwanta yace mata baijin bacci zai koma part d'insa.
A hankali fatuu ta kama handle din kopan ta tura ta d'an leka ciki,hango shi tayi zaune yaba kopan baya ta yadda duka kafafunsa na asaman kujeran ya mik'ar dasu,k'ira'ar karatun da yake na tashi a hankali,
Shiga tayi da yar sallama a bakinta gabanta na d'an faduwa ta nufi can gefen c-table ta durkushe,bai kalleta ba amman yaji shigowar mutum,cigaba yayi da karatunsa ita kuma tana ta kallonshi tana wasa da yatsun hannunta,sai da yakai karshen surar da yake karantawa ya aje wayan a gefensa,tsawon wasu seconds ya d'auka kafin ya juya ya kalleta fuskar nan ad'aure tamkar bai ta6a dariya ba,lokaci guda fatuu tasha jinin jikinta ta shiga motsa baki gabanta na bugawa da karfi da karfi,tana son ta bud'a baki ta gaishe shi amman sam ta kasa saboda ganin yanayin shi,yadau d'an lokaci yana kallonta
"Dama ke yar iskace" ya jefo ma fatuu tambaya,a gigice ta zaro idanu tana kallonshi jin abunda yace,girgiza kai ta fara yi a tsananin rud'e tace"A..a...a'a wllh ni ba yar iska bace,na rantse da Allah ban ta6a iskanci da kowa ba kaji na rantse maka...." ta6e baki ta fara yi nan da nan hawaye suka fara zubowa daga idanunta,
"Amin" ladidi ta amsa tana kokarin mikewa tace"na tsaida ki zaki tafi aiki ga lokaci nata tafiya" mik'ewa itama Gwaggon tayi tana fadin"to daman dai wani lokacin dole ai uzuri yasa ka makara kaman yadda wani lokacin kaima ba'a zuwa a amshe ka da wuri saboda wani dalilin haka dai ake ta fama" yar dariya ladidi tayi"hakane kam rayuwan gaba daya sai da uzuri,ku kunma ji dadi kunata aikin ku wllh kai bawa kullum sai fama da wuta kake" gwaggo tace"to ya za'ai kowa da hanyar da Allah ya tsaga masa cin abincinsa,Allah dai ya kara rufa mana asiri duniya da lahira" ladidi ta amsa da Amin yayin da suka nufi hanyar zaure a tare,
Da sauri fatuu ta koma gefen d'an gadonta ta zauna daga inda ta la6e tana sauraron hirarsu gwaggo,hannu tasa ta ruke ha6arta a fili tace"kai,wai yaya handsome har yasa an kama su gaye kenan" kwafa tayi ta sake cewa"ai maganinsu kenan mugaye kawai,kilan ma su za'a kai gidan yarin ba ni ba,wayyo har naji tausayin Gaye wllh shi baiso ba amman abokanansa sun ja masa" idasa fadawa tayi saman gadon ta kwanta tana kallon sama ta ci gaba"yakamata inje in gaida Yaya handsome tunda saboda ni yaji ciwo,ko yama akai yasan naje kangon nan,kilan yagan sanda na juya nabi lungun ne,ashe dai haka yake da mugun kirki ni wllh farkon dana fara ganinshi nayi tunanin baida mutunci ba kaman daya falla mun marin nan" kyalkyacewa tayi da dariyar farinciki kafin tace"ai da har naji tsoron ko yana can bai iya tafiya ne shiyasa ban ganshi da safe ba,ashe har wurin yan Sanda yaje ya kai kara,ohooo shiyasa yace kar na fadi ma kowa abunda ya faru nagano dalilin...,Oh da ansan nice da sai aita nuna ni wasu ma su ki yarda ba ai man fyaden ba,gwara ma da ba wanda yasan ni ce"ta k'arasa maganar tana ta faman watsa hannuwa kaman da wani take maganan,
"Fatuu" gwaggo da ta dawo daga rakiyar da tayi ma ladidi ta kwala mata kira,da sauri ta saukko daga gadon ta nufi kopa tana amsa kiran,d'aga labulan tayi ganin gwaggon a bakin kopan yasa ta tsaya tace"gani" kallon kanta gwaggon tayi wanda ke bude ba dankwali ta d'an girgiza kai tace"wai ke don Allah fatuu sai yaushe ne zaki hankali,kisan abunda ya dace ne iye?yanzu wannan kan naki tun yaushe yake a tsefe ne,kudi fa kawai zaki dauka kije a kitse maki amman abun duniya ya gagara so kike sai na kama hannunki naje na kaiki ne?" turo baki fatuu tayi"Allah gwaggo bazaki gane ba fa,wllh balaraban nan mugun zafin hannu gare ta,kitson da tayi man na karshe fa har dan guntun fitsari sai da nayi fa" ta6e baki gwaggo tayi tace"wannan kuma ai kin saba in dai sakin fitsari ne,kullum mutum bazai yi abu lokacin da yake jin sa ba sai ya matse shi ba dole ya zubo ba,ke dai kika sani,gashin ma naki bai da zuciya ne yadda baki gyara shin nan kamata yayi ace zuwa yanzu duk ya zube ya bar ki da kwaikwaidon kai",
Langa6ar da kai tayi tana turo baki"kai gwaggo harda mugun fata,to ke ki mun ko kalaba ko kuma ki man na fulani da kike man" gwaggo tace"Uhmm sai ki ta jira na ai har in samu lokaci,nasan hakan ba matsala bane a wurinki,kinga ni zan wuce wurin aiki nama rigada na makara,ga abinci nan a kicin in Amadu ya dawo ki dau nasa ki kai masa,sannan kema in kin ci kiyi wanka sai ki share tsakan gidan da kuma kicin din don duk ya 6aci ban samu na gyara ba" daga haka ta juya can kuma sai ta sake juyowa tace"fatuu na roke ki don Allah ki zauna agida kar kije ko ina da lokacin islamiyya yayi ki tafi ana tasowa kuma ki dawo gida kinji?,
d'an sosa kai tayi"to,amman zan dan je gidan hajia in nagama abunda kika sani kafin lokacin islamiyyar yayi" wani kallo gwaggon tayi mata kafin tace"wai mi kike yi ne a gidan hajiyar ba jiya kinje ba kuma ma da dare,to mi kuma zaki je yi yanzu?anya fatuu ba wata rigimar kike shirin jawo man ba kike fakewa da zuwa gidan hajia?" da sauri ta girgiza kai tace"Allah ni ba wani rigimar da zan jawo maki,yaushe rabon ma da kiji an kawo karata,kawai banson in zauna ni daya shiru tunda kinga shi kawu Amadu da ya dawo ya dan huta shago zaije ya bude" ta6e baki gwaggon tayi"ai jin shirun ba'a kawo k'arar taki ba kwana biyu yasa ni nike zullumi don in kikai kwance kwancen nan to ba k'araman rigima za'a jawo man ba",
kyalkyacewa da daria fatuu tayi tace"to ki kwantar da hankalinki kakus ba wani rigiman da zan jawo na bari na shiryu ba ruwana yanzu" gwaggo tace"da nafi kowa farin ciki,sai dai nasan a iya baki ne don nasaba jin hakan" daga haka ta juya ta nufi hanyar fita fatuu ta d'an daga murya"inje ko? batare da gwaggo ta juyo ba tace"ai sai kita zuwa ko na hana ma nasan sai kinje" fatuu da ke ta dariya da karfi tace"si to a warti kakus" hannu gwaggon ta d'ago mata lokacin kuma ta idasa ficewa daga gidan,fatuu na ganin ta fice ta koma d'aki da sauri don daukko gyalenta dan gado ta tafi gidan hajiyar Sanata.
*💖ASANADIN MAKWABTAKA💖*
_A heart touching love story._
_*BY ZAINAB LALUH📲*_
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
*32⃣*
Fitowa tayi da sauri tana yafa gyalen saman uniform din jikinta,a daidai zaure suka had'e da kawu Amadu ya dawo daga Makaranta shima,wani kallo yayi mata yace"yawo ko?" Da sauri ta girgiza mashi kai"a'a gidan hajiya zani kuma na tambayi gwaggo ma yanzun nan ta fita" gyada kai yayi yace"eh na hadu da ita,mashin d'in da ya kawo ni ma ta hau,yanzun je ki kawo man abinci na sai kita tafiya" to tace ta juya don daukko masa abincin,
Yana zaune agefen yar katifarsa yana cire safar kafarsa ta shigo,aje masa yar kular abincin da cokali asamanta tayi a gabansa tace"gashi nan" tana k'okarin juyawa yace"ruwa fa?"wani kallo tayi masa tana turo baki "kai kawu wai ruwan ma baka iya zuwa kasha in ka gama don kawai ka wahalar dani" harararta yayi cikin d'aure fuska yace"Imi fijirma(ina wasa dake)!zaki kawo man ruwan ko sai na tattaka ki anan,kin iya jin wahalan asa ki yin abu amman baki jin wahalan yawo"tana ta faman turo baki ta koma ta d'ebo masa ruwan ta kawo masa,yar harara ya watsa mata kafin yasa cokali ya fara cin abincin,juyawa tayi zata fita ta hango kwali d'auke da su biscuits dasu sweet aje a jikin bango, d'an juyowa tayi ta saci kallonsa taga hankalinsa na kan abincin da sauri tasa hannu ta rarumo sweet jin karar ta6a kwalin yasa shi dagowa da sauri yace'Fatuu...."da gudu ta fice daga gidan.
________________
Haisam zaune a parlornsa hannunsa ruke da wayarsa yana karatun Al'qurani a hankali ta cikin app d'in Vmuslim,tun bayan da suka dawo shi da Officer direct part din hajiya ya nufa don yin breakfast yasha magungunan da aka bashi,anan ne taga raunin daya ji a kafan,ba k'aramin tashi hankalinta yayi ba taita faman tambayan shi yadda ya samu rauni bacin jiya lafiya lou suka rabu,bai 6oye mata ba ya fad'i mata kwalba ce ya taka amman a part d'in sa yace mata bai fad'i mata ainihin yadda akai ya samu raunin ba,aikam ba k'aramin jimami ta shiga ba mamaki ya cikata na yadda akai akasamu kwalba apart dinsa har ya taka don tasan ko lemun kwalba basu amfani dashi haka dai taita faman jajanta al'amarin,da kanta ta had'o masa breakfast har yunkurin bashi a baki tayi ya hanata yana ta faman dariya,tsare shi tayi sai da ta tabbatar yaci sosae sannan ta 6allo masa magungunan yasha,ci gaba su kai da hira har ya tambayeta miyasa bata je aiki ba,ta sanar mashi cewa tana aikin wani project ne sai ta gama gaba daya sannan zata je,bayan wani lokaci ne hajiyan tayi bak'i hakan yasa haisam din baro part din hajiar,har cewa tayi yaje dakinta ya kwanta yace mata baijin bacci zai koma part d'insa.
A hankali fatuu ta kama handle din kopan ta tura ta d'an leka ciki,hango shi tayi zaune yaba kopan baya ta yadda duka kafafunsa na asaman kujeran ya mik'ar dasu,k'ira'ar karatun da yake na tashi a hankali,
Shiga tayi da yar sallama a bakinta gabanta na d'an faduwa ta nufi can gefen c-table ta durkushe,bai kalleta ba amman yaji shigowar mutum,cigaba yayi da karatunsa ita kuma tana ta kallonshi tana wasa da yatsun hannunta,sai da yakai karshen surar da yake karantawa ya aje wayan a gefensa,tsawon wasu seconds ya d'auka kafin ya juya ya kalleta fuskar nan ad'aure tamkar bai ta6a dariya ba,lokaci guda fatuu tasha jinin jikinta ta shiga motsa baki gabanta na bugawa da karfi da karfi,tana son ta bud'a baki ta gaishe shi amman sam ta kasa saboda ganin yanayin shi,yadau d'an lokaci yana kallonta
"Dama ke yar iskace" ya jefo ma fatuu tambaya,a gigice ta zaro idanu tana kallonshi jin abunda yace,girgiza kai ta fara yi a tsananin rud'e tace"A..a...a'a wllh ni ba yar iska bace,na rantse da Allah ban ta6a iskanci da kowa ba kaji na rantse maka...." ta6e baki ta fara yi nan da nan hawaye suka fara zubowa daga idanunta,