Sashe 11
Asanadin Makwabtaka Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Duk maganganun da take a kunnan gwaggo,fitowa tayi ta tsaya a bakin k'ofa hannunta d'aya dafe jikin bango tana kallon Fatun sai kiciniya take.
"To taya zai sanyu kin kasa natsuwa kisa shi sosae,ji bi yadda kika wani takure kin cusa jaka a hammata,d'agowa tayi tace"to yaya zanyi" fuska a tur6une da alama takalmin ya k'ule ta,
"Ki aje jakar mana a gefe,ki zauna sosai kisa" Aje jakar tayi ta dan zauna a bakin k'ofa kamar yadda gwaggon tace,aikuwa sai gashi takalmin ya sanyu ba wani 6ata lokaci,da sauri fatuu ta d'ago ta kalli gwaggo tana daria tace "Kinga d'an banza ya sanyu kuwa" gwaggo ta dan ta6e baki"Uhm ba wani d'an banza,dama ba ki yadda ya kamata ya sanyun bane,ace komi mutum zai yi bazai sa natsuwa ba,
Mik'ewa fatuu tayi tana kokarin goya yar jakar goyon a bayanta tace"zan tafi" gwaggo tace"To adawo lpy,Allah ya tsare" wani irin kallo fatuu tayi mata tace adawo lafia kuma?
Gwaggo tace"Eh mana ko baki son Addu'ar ne?, "A'a ina so mana amman ai banji bayani ba" tayi maganar tana yi ma gwaggo alamar kud'i da hannuwanta,gwaggo tace"wai don Allah ba ranar da zaki ce yau dai gwaggo kibar kudin ki ne?
Da sauri fatuu tace "iyeee,to kuma dami zan hau mota kuma inyi break,in baki bani ba? Gwaggo tace "to acici baki da magana dama sai ta abinci,a duk satin duniya sai kin cinye mani naira d'ari biyar wani satin ma sai sun fi haka tunda sai ki dawo kice man baki samu bus ba kin ranci kudi kinyi ciko kin hau Napep ko mashin", Fatuu da ke tsaye ta k'agara gwaggo ta sallameta ko ta tafi tace"Don Allah gwaggo kiban,taya karatun zai yiwu da yunwa to ko mota dai ai sai an zuba mata mai take aiki ko" yar daria gwaggo tayi, fatun tace "yau baki zuwa aikin ne? "Zanje,amman sai da rana",
Fatuu tace"kenan zan dawo in iske ki? Gwaggo tace "Anya kuwa kinsan yau juma'a,da wuri zan tafi,wurin k'arfe d'aya haka",
"to ammn dai zaki yi mana abinci ko ba sai na dawo ba inyi"tayi maganar da sigar shagwa6a" gwaggo ta rike baki tace"Ah kajita ko da yaushe-da yaushe nike tafiya in bar mata wani yin abinci,ai sai dai in ina aikin safe ne kuma shima kusan tare muke dawowa,kamar wadda ta iya wani abincin arziki",
Fatuu tace "ai dai ina yi kuma ki ci har kice yayi dad'i" daria gwaggo take tace"Mai karya.....fatu tace"d'an Aljanna,tana daria,"gwaggo kiban don Allah" mik'o mata naira d'ari tayi wadda ke cikin hannun da ta dafa bango dashi,da sauri fatuu ta amsa tace"daman kudin na a hannun ki,amman sai kinja man rai,juyawa tayi ta fara tafia,sannan tace "Kar ki damu kakus,zan biya ki duka kud'aden da kika kashe man in nazama Doctor" har lokacin gwaggo daria take ta girgiza kai tace"nadai fad'a maki ai natsattsu ne ke zama likitoci,in baki natsu ba,ba wata Doctorn da zaki zama" da d'an karfi tace"Insha Allahu zan zama harna rik'a yima ki Allura ma,na tafi" ta karasa fada yayin da ta kusa isa zaure.
Gwaggo tace" To Allah ya tsare adawo lafia ban.......,Fatuu dake cikin zaure ta k'arasa abunda gwaggon zata fadi da karfi"BANDA RIGIMA DON ALLAH FATUU" daga haka ta fice daga gidan,girgiza kai gwaggo tayi tana ta daria tace" Shiryayya,a haka ko nace d'in wani lokacin kafin ta shigo gidan an kawo man k'ararta,Allah dai ya shirya"daga haka ta koma cikin d'aki.
Tafiya fatuu take ta raba hanya biyu,sam ba natsuwa a tafiyar,hanyar shiru dayake safiya ce sai yara jefi jefi yan tafiya makaranta kamar dai ita,sai wani cilla k'afa take kamar zata tashi wai ita nan sauri take,Horn d'in da akai da k'arfi ne a bayanta yasa tayi saurin komawa gefe,sannan ta juyo tana kallon motar da ta taho,Peugeot ce 406,Maroon color,cikin ranta tace"dama mai motar nan ya rage man han....bata k'arasa ba sakamakon mutumin data ga ya wuce fuuu a cikin motar bai ko kalleta ba,da sauri fatuu ta zaro ido had'i da rike ha6arta tace"Kai! Wancan ai mutumin nan ne na jiya mai kama da Aljani,ba dai a layin nan yake ba? ta karasa maganar da sigar tunani harda d'an waigawa baya,tace"Uhm inma nan din yake,shi dai ya sani"
taci gaba da tafiya har tazo wata kwana d'an nesa da gidansu,tana karya kwanar ta tsaya da alamun mamaki a fili tace"lallai ma wannan haulatun,har yanzu bata fito ba,tana nufin in bita har cikin gida kenan" kwafa tayi sannan taci gaba da tafia,ad'an gaba kadan daidai wani gida inda yaro ya fito dauke da d'an bokitin plastic ta tsaya tace ma yaron "Kai haulatu na nan ciki" yaron yace "Eh naganta tazo ta karbi koko a rumfar da Innarsu ke saidawa" ya wuce,ita kuma fatuu ta kad'a kai ta shige cikin gidan wanda gaba daya k'asan gidan kasa ce,sai daga can gaban dakuna ne akai ma k'asan shafen siminti shima duk ya farfashe,a gefe guda wata mata ce cikin wata yar baranda da yara tsaitsaye tana zuba masu koko,matsawa fatuu tayi bakin barandar tace "Innarsu Haulatu ina kwana" da washe baki ta amsa"lafia lau fatee yan makaranta,haulatun na ciki" kad'a kai fatu tayi ciki,tana hawa saman simintin wata yarinya ta lek'o tana daria,wankan tarwad'a ce tana da kyau ba laifi,hannunta d'aya rike da hijabin Uniform dinta dayan kuma kofi ne tana shan koko,tsayawa fatuu tayi tana harararta,fuska daure tace"Ashe ma baki shirya ba don wulakanci kika sa inata sauri" haulatun wadda keta faman daria tace"wallahi markad'e innarmu ta aikan kuma sai na iske layi,amman ai na shirya hijab kawai zansa da Sandals",da yar tsawa fatuu tace "Da Allah to kisa mu tafi,salon sai mun makara wannan banzan displine d'in ya bugi mutane, daman ya tsane ni" ta k'arasa tana murgud'a baki,
Haulatu tace"bafa kyau zagin malami fat...." ta katseta"naji,wayace ya tsane ni"fatuu ta haulatu tace"bafa tsanarki yayi ba,kece kike ja ai yana dukan ki,ni kinga yana duka na?" ta kai maganar tana kurbar koko,"dalla ki fito mutafi ko inyi tafiya ta wallahi,daman ke ai baki ganin laifin kowa sai nawa"da alamar ranta ya 6aci, Haulat tace"Haba kawata daga fad'ar gaskia...."
"to ki rik'e gaskiyar banso" inji fatuu,mik'o ma fatuu kofin kokon haulat tayi tace ida shanye wa",harararta Fatuu tayi da sauri tace "Wa!Ni zan sha wani koko,kokon ma sauran ki,Allah ya kiyaye,ta tofar da miyau gefe" girgiza kai haulat tayi da d'an murmushi ta idasa fitowa,aje kofin tayi a k'asa ta sanya hijab din da Sandals din dake aje bakin kofar d'akin,ta d'auki jakar ta,ta leda irin ta biki tace"Mu tafi" atare suka nufi hanyar fita,haulat ta shiga rumfar da innarta take,ta ajiye kofin data sha koko tace ma Innar "zan tafi" kud'i innar ta miko mata naira sittin tace"A dawo lpy" Allah yasa" haulat tace ta nufi hanyar k'ofar gida,don ita fatuu tuni ta fuce.
A kan hanyarsu ta zuwa bakin titi inda zasu hau Bus fatuu sai faman masifa take ma haulat tana cewa ai in suka rasa Bus itace a matsala don tasan bata da isassun kud'in da zata hau Napep ko mashin,baiwar Allah haulatun ita dai tayi shiru tana sauraranta da alama tana da hakuri,gashi da gani ta girmi fatun ko a yanayin jiki tafi fatuu tsawo a sanyaye tace"Insha Allahu ma zamu samu,in kuma ba'a samun ba sai in dawo ba wani abu,in Allah ya kaimu Monday naje"daga haka ba wanda ya kara cewa wani abu.
Suna isowa bakin hanyar kuwa sai ga Bus din da yar fara'a haulat tace "Alhamdulillah",juyowa fatuu tayi tai mata wani kallo fuska a d'aure.
Haulatu kawar fatuu ce,tun lokacin da tazo garin,lokacin da gwaggo tasa ta a makaranta har gida taje ta had'a su suyi kawance,don tasan halin haulat yarinya ce mai hakuri da natsuwa,ita kadai ce zata iya jure halin fatun a yaran unguwar,gwaggo ta roki haulat da ta d'auki fatuu a matsayin kanwarta ta rik'a nuna mata abubuwa masu kyau,ta kuma rika hanata maras kyau,gwaggo bata 6oye ma haulat komai ba game da halin fatuu, a gabanta kuma tayi ma fatu fad'a sosai akan ta zauna lpy da haulat ta rik'a jin maganarta,intaji sun yi fad'a tasan itace ta ja,kuma sai ta sa6a mata,Innarsu haulat ta tabbatar ma gwaggo cewa haulat bata da matsala karta damu,dama kuma ana ganin mutuncin Gwaggo a unguwar,Ita kuwa haulat tunda taga fatu taji tayi mata,jininta ya had'u da ita,tace ma gwaggo zata kula da ita insha Allahu,A haka kawancen su ya k'ullu,duk da ance wai sai hali yazo d'aya ake abota,to nan dai halin sam bai zo daya ba,dama kuma sai ansamu bambanci abota ke lasting,misali,daya mai wayo daya mara wayo ko daya mara hakuri daya kuma mai hakuri kaman su kenan,Amman duk da hakurin Haulat wani lokacin sai fatu ta k'ule ta har tayi fushi,sai kuma ta dawo taita bata hakuri har sai taga ta hakura,dama ko gwaggonta haka take mata.
"To taya zai sanyu kin kasa natsuwa kisa shi sosae,ji bi yadda kika wani takure kin cusa jaka a hammata,d'agowa tayi tace"to yaya zanyi" fuska a tur6une da alama takalmin ya k'ule ta,
"Ki aje jakar mana a gefe,ki zauna sosai kisa" Aje jakar tayi ta dan zauna a bakin k'ofa kamar yadda gwaggon tace,aikuwa sai gashi takalmin ya sanyu ba wani 6ata lokaci,da sauri fatuu ta d'ago ta kalli gwaggo tana daria tace "Kinga d'an banza ya sanyu kuwa" gwaggo ta dan ta6e baki"Uhm ba wani d'an banza,dama ba ki yadda ya kamata ya sanyun bane,ace komi mutum zai yi bazai sa natsuwa ba,
Mik'ewa fatuu tayi tana kokarin goya yar jakar goyon a bayanta tace"zan tafi" gwaggo tace"To adawo lpy,Allah ya tsare" wani irin kallo fatuu tayi mata tace adawo lafia kuma?
Gwaggo tace"Eh mana ko baki son Addu'ar ne?, "A'a ina so mana amman ai banji bayani ba" tayi maganar tana yi ma gwaggo alamar kud'i da hannuwanta,gwaggo tace"wai don Allah ba ranar da zaki ce yau dai gwaggo kibar kudin ki ne?
Da sauri fatuu tace "iyeee,to kuma dami zan hau mota kuma inyi break,in baki bani ba? Gwaggo tace "to acici baki da magana dama sai ta abinci,a duk satin duniya sai kin cinye mani naira d'ari biyar wani satin ma sai sun fi haka tunda sai ki dawo kice man baki samu bus ba kin ranci kudi kinyi ciko kin hau Napep ko mashin", Fatuu da ke tsaye ta k'agara gwaggo ta sallameta ko ta tafi tace"Don Allah gwaggo kiban,taya karatun zai yiwu da yunwa to ko mota dai ai sai an zuba mata mai take aiki ko" yar daria gwaggo tayi, fatun tace "yau baki zuwa aikin ne? "Zanje,amman sai da rana",
Fatuu tace"kenan zan dawo in iske ki? Gwaggo tace "Anya kuwa kinsan yau juma'a,da wuri zan tafi,wurin k'arfe d'aya haka",
"to ammn dai zaki yi mana abinci ko ba sai na dawo ba inyi"tayi maganar da sigar shagwa6a" gwaggo ta rike baki tace"Ah kajita ko da yaushe-da yaushe nike tafiya in bar mata wani yin abinci,ai sai dai in ina aikin safe ne kuma shima kusan tare muke dawowa,kamar wadda ta iya wani abincin arziki",
Fatuu tace "ai dai ina yi kuma ki ci har kice yayi dad'i" daria gwaggo take tace"Mai karya.....fatu tace"d'an Aljanna,tana daria,"gwaggo kiban don Allah" mik'o mata naira d'ari tayi wadda ke cikin hannun da ta dafa bango dashi,da sauri fatuu ta amsa tace"daman kudin na a hannun ki,amman sai kinja man rai,juyawa tayi ta fara tafia,sannan tace "Kar ki damu kakus,zan biya ki duka kud'aden da kika kashe man in nazama Doctor" har lokacin gwaggo daria take ta girgiza kai tace"nadai fad'a maki ai natsattsu ne ke zama likitoci,in baki natsu ba,ba wata Doctorn da zaki zama" da d'an karfi tace"Insha Allahu zan zama harna rik'a yima ki Allura ma,na tafi" ta karasa fada yayin da ta kusa isa zaure.
Gwaggo tace" To Allah ya tsare adawo lafia ban.......,Fatuu dake cikin zaure ta k'arasa abunda gwaggon zata fadi da karfi"BANDA RIGIMA DON ALLAH FATUU" daga haka ta fice daga gidan,girgiza kai gwaggo tayi tana ta daria tace" Shiryayya,a haka ko nace d'in wani lokacin kafin ta shigo gidan an kawo man k'ararta,Allah dai ya shirya"daga haka ta koma cikin d'aki.
Tafiya fatuu take ta raba hanya biyu,sam ba natsuwa a tafiyar,hanyar shiru dayake safiya ce sai yara jefi jefi yan tafiya makaranta kamar dai ita,sai wani cilla k'afa take kamar zata tashi wai ita nan sauri take,Horn d'in da akai da k'arfi ne a bayanta yasa tayi saurin komawa gefe,sannan ta juyo tana kallon motar da ta taho,Peugeot ce 406,Maroon color,cikin ranta tace"dama mai motar nan ya rage man han....bata k'arasa ba sakamakon mutumin data ga ya wuce fuuu a cikin motar bai ko kalleta ba,da sauri fatuu ta zaro ido had'i da rike ha6arta tace"Kai! Wancan ai mutumin nan ne na jiya mai kama da Aljani,ba dai a layin nan yake ba? ta karasa maganar da sigar tunani harda d'an waigawa baya,tace"Uhm inma nan din yake,shi dai ya sani"
taci gaba da tafiya har tazo wata kwana d'an nesa da gidansu,tana karya kwanar ta tsaya da alamun mamaki a fili tace"lallai ma wannan haulatun,har yanzu bata fito ba,tana nufin in bita har cikin gida kenan" kwafa tayi sannan taci gaba da tafia,ad'an gaba kadan daidai wani gida inda yaro ya fito dauke da d'an bokitin plastic ta tsaya tace ma yaron "Kai haulatu na nan ciki" yaron yace "Eh naganta tazo ta karbi koko a rumfar da Innarsu ke saidawa" ya wuce,ita kuma fatuu ta kad'a kai ta shige cikin gidan wanda gaba daya k'asan gidan kasa ce,sai daga can gaban dakuna ne akai ma k'asan shafen siminti shima duk ya farfashe,a gefe guda wata mata ce cikin wata yar baranda da yara tsaitsaye tana zuba masu koko,matsawa fatuu tayi bakin barandar tace "Innarsu Haulatu ina kwana" da washe baki ta amsa"lafia lau fatee yan makaranta,haulatun na ciki" kad'a kai fatu tayi ciki,tana hawa saman simintin wata yarinya ta lek'o tana daria,wankan tarwad'a ce tana da kyau ba laifi,hannunta d'aya rike da hijabin Uniform dinta dayan kuma kofi ne tana shan koko,tsayawa fatuu tayi tana harararta,fuska daure tace"Ashe ma baki shirya ba don wulakanci kika sa inata sauri" haulatun wadda keta faman daria tace"wallahi markad'e innarmu ta aikan kuma sai na iske layi,amman ai na shirya hijab kawai zansa da Sandals",da yar tsawa fatuu tace "Da Allah to kisa mu tafi,salon sai mun makara wannan banzan displine d'in ya bugi mutane, daman ya tsane ni" ta k'arasa tana murgud'a baki,
Haulatu tace"bafa kyau zagin malami fat...." ta katseta"naji,wayace ya tsane ni"fatuu ta haulatu tace"bafa tsanarki yayi ba,kece kike ja ai yana dukan ki,ni kinga yana duka na?" ta kai maganar tana kurbar koko,"dalla ki fito mutafi ko inyi tafiya ta wallahi,daman ke ai baki ganin laifin kowa sai nawa"da alamar ranta ya 6aci, Haulat tace"Haba kawata daga fad'ar gaskia...."
"to ki rik'e gaskiyar banso" inji fatuu,mik'o ma fatuu kofin kokon haulat tayi tace ida shanye wa",harararta Fatuu tayi da sauri tace "Wa!Ni zan sha wani koko,kokon ma sauran ki,Allah ya kiyaye,ta tofar da miyau gefe" girgiza kai haulat tayi da d'an murmushi ta idasa fitowa,aje kofin tayi a k'asa ta sanya hijab din da Sandals din dake aje bakin kofar d'akin,ta d'auki jakar ta,ta leda irin ta biki tace"Mu tafi" atare suka nufi hanyar fita,haulat ta shiga rumfar da innarta take,ta ajiye kofin data sha koko tace ma Innar "zan tafi" kud'i innar ta miko mata naira sittin tace"A dawo lpy" Allah yasa" haulat tace ta nufi hanyar k'ofar gida,don ita fatuu tuni ta fuce.
A kan hanyarsu ta zuwa bakin titi inda zasu hau Bus fatuu sai faman masifa take ma haulat tana cewa ai in suka rasa Bus itace a matsala don tasan bata da isassun kud'in da zata hau Napep ko mashin,baiwar Allah haulatun ita dai tayi shiru tana sauraranta da alama tana da hakuri,gashi da gani ta girmi fatun ko a yanayin jiki tafi fatuu tsawo a sanyaye tace"Insha Allahu ma zamu samu,in kuma ba'a samun ba sai in dawo ba wani abu,in Allah ya kaimu Monday naje"daga haka ba wanda ya kara cewa wani abu.
Suna isowa bakin hanyar kuwa sai ga Bus din da yar fara'a haulat tace "Alhamdulillah",juyowa fatuu tayi tai mata wani kallo fuska a d'aure.
Haulatu kawar fatuu ce,tun lokacin da tazo garin,lokacin da gwaggo tasa ta a makaranta har gida taje ta had'a su suyi kawance,don tasan halin haulat yarinya ce mai hakuri da natsuwa,ita kadai ce zata iya jure halin fatun a yaran unguwar,gwaggo ta roki haulat da ta d'auki fatuu a matsayin kanwarta ta rik'a nuna mata abubuwa masu kyau,ta kuma rika hanata maras kyau,gwaggo bata 6oye ma haulat komai ba game da halin fatuu, a gabanta kuma tayi ma fatu fad'a sosai akan ta zauna lpy da haulat ta rik'a jin maganarta,intaji sun yi fad'a tasan itace ta ja,kuma sai ta sa6a mata,Innarsu haulat ta tabbatar ma gwaggo cewa haulat bata da matsala karta damu,dama kuma ana ganin mutuncin Gwaggo a unguwar,Ita kuwa haulat tunda taga fatu taji tayi mata,jininta ya had'u da ita,tace ma gwaggo zata kula da ita insha Allahu,A haka kawancen su ya k'ullu,duk da ance wai sai hali yazo d'aya ake abota,to nan dai halin sam bai zo daya ba,dama kuma sai ansamu bambanci abota ke lasting,misali,daya mai wayo daya mara wayo ko daya mara hakuri daya kuma mai hakuri kaman su kenan,Amman duk da hakurin Haulat wani lokacin sai fatu ta k'ule ta har tayi fushi,sai kuma ta dawo taita bata hakuri har sai taga ta hakura,dama ko gwaggonta haka take mata.