Sashe 73
Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanci tashi ba wuya a wajen Allah, ga shi har sha'anin bikin Assadiq da Sultana ya kawo saura Sati uku, dukkan Shiryen shiryen sun gama kamallah a nan garin Gusai.
Tuni har an yima sultana Jerenta da kayan alfarman da Abba ya siya mata, a kuma jera mata su a cikin kayattacen gidan da Abba ya mallaka ma Assadiq Hakal makal.
Sannan Surayya ta gama had'a akwatina Guda takwas shake da kayan alfarma, sai wanda ya gani kaya na gani na fad'a na ya'yan gata.
Ta bangaram matan sun fi shirye shiryen Bangaren Ango Sadiq kuma sai in ma Tahir ya kirasa ne ya ke Tunawa da zencen auran.
Shi dai ya na gefe sai abunda aka kirasa akace masa ya ke amsawa.
Shi dai bai zira jikinsa ba, sannan bai yi baya ba.
Tunda auran gata Abba zai yi masa, sai ya kudira a ransa zai ba ma Sultana kudin gyaran jiki da kwalliya sannan shi yanzu Fafutukarsa na Kudin da zai bama Siya ta siya kaya ne bisa adalci Tunda ita bai yi mata Lefe ba.
Kudin da ya ke Turamata ta acct dinta sun kai yanzu Kimanin dubu Dari biyu da wani abu ya na so su kai uku ne yace ta Dauka ta siya abubuwan da ta ke so.
Sannan ko mganar kayan angwanci Big sis tace Abba ya ba da kudi an had'a masa akwati guda, sannan Tahir ya yi masa wasu, ko katin Biki na waya da na Hannu Tahir ne zai yi komai
Yana Abuja Tahir ya kirasa kan mganar inda za'a Daura aure saboda Buga kati, shi kuma ba shi da Say akan haka duk da suna mgana da Abba da Umma sosai Sisters dinsa ma suna yawan Kiransa, ita kanta Sultana ya na Kiranta ammh kuma sai ya tuna da Siya sai goma ya Kirata kafin ya Tuna da Sultana ya kirata.
Ce ma Tahir ya yi ya bari in ya yi mgana da Abba zai kirasa ya fad'a masa.
Sai dai ya yi ta kiran Abba bai Sameshi ba har zuwa Dare sai ya Kira Umma ya yi mata zencen.
Ita kuma ta warware masa Halin da ake ciki saboda kara Abba yace a shinkafi gidan Mallam Shitu Mahaifin Sultana za'a Daura aure.
Ammh Innani ta Daka Tsalle tace Uban kuturu ya yi kad'an in kuma Sulaimanu ya Dage to ita dai ba da yawunta ba, ga shi Abba ya kira ya Furta Kowa ya sani ya rasa yadda zai yi da Innani.
Sadiq na jin haka ransa ya baci da innani a satin Zariya ya so tafiya saboda ya cikama Siya kudin nan, ammh sai ya sauya Tsari washegari jumma'a Gusai ya tafi, yasan wacece Innani kan wannan mgamar sai ta yi Sanadiyar da Rayukan wasu bayin Allah za su baci.
Ya kuma je ya isketa a na daru da ita ammh tace ba'a isa ba sai faman Zagin Mallam Shitu ta ke yi ta na kawo wasu labarai marasa Tushe ballatana makama, baiwar Allah Sultana sai kuka ta ke yi abun da zafi a rika zagin mahaifinka a kunnen ka.
Su Umma sun gaji da mgana Daga karshe Innani ta had'a da su ta Zage daman kwanaki sai da ta yi kan kayan Dakin Sultana, wai shima sai an yi masa mgana ya kawo wani abu Tunda Ubanta ne shi, kuma an yi masa kokari an riketa na Shekaru sha ba tare da sisinsa ba.
Kuma sanda Mallam Shitu ya zo a gabansa Innani ta rika mganganun har ta na yi masa gori, abun ba dadin ji, kuma Tsakani ga Allah ya kawo kudad'e ya bama Abba sai yaki karb'a yace ko Hauwa na da rai Sultana yarsa ce har gaban Abada, ammh Innani ta rika bala'i ta na masifa.
An samu wanchan mganar ta wuce ga wannan kuma ta tsiro da shi.
Sadiq Abba ya fara samu ya yi ma mganar bude bakin Abba sai yace"Magajij gida Innani uwa ce a wajena kuma akwai Rikicin Tsufa a tare da ita, gwara ku tayani lallabata mu Rabu lafiya."
Sadiq na jin haka yasan Abba ya tsaya a matsayar Innani Tunda har ya na mganar zai samu Baba Sammani ya gayamasa yasan yadda zai yagama Mallam Shitu Saboda yana jin kunyarsa.
Sadiq na jin haka yasan sai ya samu Innani ya fito mata ta bayan gida.
Sai da ya bari dare ya yi ba kowa a shashen nata sai ita kad'ai yadda zai ji dadin yi mata abunda ya shirya.
Kamar ko ya sani batare da ya tambayetaa ba ta fara rattaba masa Labarin abunda ya faru har ta na fad'in"Yo ni za'a kawo ma iskanci? Yarinya tun ta na jarriyarta Sulaimanu ya yi wahala da ita sai yau Rana Tsaka a wani ce gidansa za'a je daura aure in ya isa shegiya na ke, ai na ce in dai chan za'a je ni Dije ba da yawuna ba."
Kallonta kawai ya ke yi cikin tattaro mganar bakinsa, Cikin kaushim murya yace"Daman gidan Ubanta nan ne a hakku a daura mata aure."
Innani ta yi galala ta na kallonsa kafin tace"me ka ke nufi Magajin gida?
Kai Tsaye yace"Abunda na ke nufi a shinkafi za'a daura auran nan a kuma gidan mahaifin Sultana."
Innani ta ballamai Harara kafin tace"Au to daman turo ka suka yi ko?
To wlh wannan karon ba wanda ya isa nan gidan Sulaimanu nan za'a Daura wannan auran naga Uban da ya isa ya ce Ba haka ba."
Sadiq yace"Ba isa ba ne Innani, Sai dai ki sani matukar kika dage sai anan za'a Daura auran nan ni kuma wlh Tallahi kin ji na rantse miki da Allah zan fasa auran Sultana kuma da gaske na ke yi."
Sai Innani ta yi shuru ta kasa mgana, shi kuma ya kura mata ido ya na kallonta ganin ta yi shuru yasa ya cigaba da fadin"Ke shikenan bakya yafiya? Ki rika afuwa Innani Domin ke kam baki san Tarin laifukan ki wajen Allah ba, da Allah baya yafiya ma da Tuni An dade da shafemu a wannan Duniyar, ya kamata ki Sassuta ma kanki wannan kiyayyar in ba haka ba zaki Mutu ana murna da Mutuwarki."
Sai kawai Innani ta Fashe da kuka ta na Fadin"Ai shikenan na bar mganar ka gayama Sulaimanu na hakura aje a daura auran a shinkafi wlh na bar mganar har Abada."
Jinjina kai Sadiq ya yi kafin ya ce"Dakyau naji dadin haka , Ni ina so in kin mutu Ranar Lahira ki Rabauta kakata, na baki wani kissar da zai taimaka miki wajen cire jin haushin wani a ranki?
Bai bata Damar mgana ba ya Cigaba da fadin"A zamanin Annabi muhammad Sallahu alaihi wasallama, watarana ya na zaune acikin masallaci Tare da Sahabbai kawai sai Annabi yace ga dan Aljannah nan zai shigo, Sai Sahabbai suka yi shuru tare da kurama kofar masallaci ido su ga waye zai shigo.
Sai ga wani bawan Allah ya shigo cikin masallaci kuma bayan Shi ba wanda ya kara shigowa, sai abun ya ba ma Sahabbai mamaki da jin abunda Annabi yace, na cewa shi d'in d'an Aljanmah ne, sai cikin Sahabban Annabi wani ya bishi gida yace ya ba shi masauki na kwanaki sai ya bashi da niyar ya rika ganin wani irin Ibada ya ke yi da Tun a Duniya Annabi yace shi dan Aljanna ce, sai yaga duk tsawon kwanakin da suka yi tare ko sallar Dare ba ya gani yana yi ban da kamsil salatu a ranar na uku ne wannan Sahabin ya sameshi ya gayamasa abunda Annabi ya gayama su game da shi, Dalilin da yasa ya zo wajensa saboda yaga wani irin Ibada ya ke da har tun a duniya Allah ya bashi Aljannah.
Sai wannan bawan Allah ya yi Kabbara sau uku kafin yace" bai san har yakai haka ba, abu d'aya kawai ya sani Tunda ya ke bai taba kwana da wani a ransa ba duk abunda aka yi masa nan ta ke yake yafewa kwana yake zuciyarsa wasai ba kowa acikinta"
Dan dakatawa Sadiq ya yi ya na kallon Innani da ta natsu ta na ji harda jan Doguwar kabbara."Allahu Akbar" lokaci daya ta na faman sharan kwallah.
Sai Assadiq ya sauke ajiyar rai kafin yace"To kisance mai yawan yafiya Innani domin masu yawan afuwa Samakonsu na wajen Allah"
Da Sauri Innani tace"Allahu Akbar Wlh na yafe ma kowa Allah Sarki. na yafe ma kowa ni yanzu shima Shitun na yafe masa duniya da Lahira Magajin gida ni yanzu zuciyata wasai."
Sadiq yace"To ina fatan bazaki kara tada wata mgana ba.?
Da Sauri tace"In sha Allahu Magajin gida kai dai Allah ya yi maka albarka kawai."
Ya amsa da Ameen, Shikenan magana ta Mutu, sai dai su Abba sukaji sabon zencen Innani da kanta tace ko Bikin ma in chan za'a yi sai su kwasa su je gabadaya chan Abba yace nan dai za'ayi Sha'anin Daurin auran ne dai za'ayi achan.
Duk da bai fito ya fad'a ba kowa yasan aikin Magajij gida shine kawai Maganganunsa ke sa ka Innani Ladabi da Nadaman Dole, kafin kwana Biyu ta koma gidan jiya.
Ranar lahadi ya koma Abuja Da Safe ya tafi da cewa sai a satin biki zai dawo, sai da ya koma sannan ya Kira Tahir ya gayamasa ga inda za'a Daura auran Shima Tahir yace hakan ya yi daidai bisa adalci.
Duk Abba yaki karban komai sai da Mallam shitu ya aiko masa da Buhuhunan shinkafa da gero da masara yace ya karb'a ba Saboda sultana ya ba shi ba domin Allah ya ba shi sannan ya karb'a bayan Sadiq ya saka baki.
Tuni har an yima sultana Jerenta da kayan alfarman da Abba ya siya mata, a kuma jera mata su a cikin kayattacen gidan da Abba ya mallaka ma Assadiq Hakal makal.
Sannan Surayya ta gama had'a akwatina Guda takwas shake da kayan alfarma, sai wanda ya gani kaya na gani na fad'a na ya'yan gata.
Ta bangaram matan sun fi shirye shiryen Bangaren Ango Sadiq kuma sai in ma Tahir ya kirasa ne ya ke Tunawa da zencen auran.
Shi dai ya na gefe sai abunda aka kirasa akace masa ya ke amsawa.
Shi dai bai zira jikinsa ba, sannan bai yi baya ba.
Tunda auran gata Abba zai yi masa, sai ya kudira a ransa zai ba ma Sultana kudin gyaran jiki da kwalliya sannan shi yanzu Fafutukarsa na Kudin da zai bama Siya ta siya kaya ne bisa adalci Tunda ita bai yi mata Lefe ba.
Kudin da ya ke Turamata ta acct dinta sun kai yanzu Kimanin dubu Dari biyu da wani abu ya na so su kai uku ne yace ta Dauka ta siya abubuwan da ta ke so.
Sannan ko mganar kayan angwanci Big sis tace Abba ya ba da kudi an had'a masa akwati guda, sannan Tahir ya yi masa wasu, ko katin Biki na waya da na Hannu Tahir ne zai yi komai
Yana Abuja Tahir ya kirasa kan mganar inda za'a Daura aure saboda Buga kati, shi kuma ba shi da Say akan haka duk da suna mgana da Abba da Umma sosai Sisters dinsa ma suna yawan Kiransa, ita kanta Sultana ya na Kiranta ammh kuma sai ya tuna da Siya sai goma ya Kirata kafin ya Tuna da Sultana ya kirata.
Ce ma Tahir ya yi ya bari in ya yi mgana da Abba zai kirasa ya fad'a masa.
Sai dai ya yi ta kiran Abba bai Sameshi ba har zuwa Dare sai ya Kira Umma ya yi mata zencen.
Ita kuma ta warware masa Halin da ake ciki saboda kara Abba yace a shinkafi gidan Mallam Shitu Mahaifin Sultana za'a Daura aure.
Ammh Innani ta Daka Tsalle tace Uban kuturu ya yi kad'an in kuma Sulaimanu ya Dage to ita dai ba da yawunta ba, ga shi Abba ya kira ya Furta Kowa ya sani ya rasa yadda zai yi da Innani.
Sadiq na jin haka ransa ya baci da innani a satin Zariya ya so tafiya saboda ya cikama Siya kudin nan, ammh sai ya sauya Tsari washegari jumma'a Gusai ya tafi, yasan wacece Innani kan wannan mgamar sai ta yi Sanadiyar da Rayukan wasu bayin Allah za su baci.
Ya kuma je ya isketa a na daru da ita ammh tace ba'a isa ba sai faman Zagin Mallam Shitu ta ke yi ta na kawo wasu labarai marasa Tushe ballatana makama, baiwar Allah Sultana sai kuka ta ke yi abun da zafi a rika zagin mahaifinka a kunnen ka.
Su Umma sun gaji da mgana Daga karshe Innani ta had'a da su ta Zage daman kwanaki sai da ta yi kan kayan Dakin Sultana, wai shima sai an yi masa mgana ya kawo wani abu Tunda Ubanta ne shi, kuma an yi masa kokari an riketa na Shekaru sha ba tare da sisinsa ba.
Kuma sanda Mallam Shitu ya zo a gabansa Innani ta rika mganganun har ta na yi masa gori, abun ba dadin ji, kuma Tsakani ga Allah ya kawo kudad'e ya bama Abba sai yaki karb'a yace ko Hauwa na da rai Sultana yarsa ce har gaban Abada, ammh Innani ta rika bala'i ta na masifa.
An samu wanchan mganar ta wuce ga wannan kuma ta tsiro da shi.
Sadiq Abba ya fara samu ya yi ma mganar bude bakin Abba sai yace"Magajij gida Innani uwa ce a wajena kuma akwai Rikicin Tsufa a tare da ita, gwara ku tayani lallabata mu Rabu lafiya."
Sadiq na jin haka yasan Abba ya tsaya a matsayar Innani Tunda har ya na mganar zai samu Baba Sammani ya gayamasa yasan yadda zai yagama Mallam Shitu Saboda yana jin kunyarsa.
Sadiq na jin haka yasan sai ya samu Innani ya fito mata ta bayan gida.
Sai da ya bari dare ya yi ba kowa a shashen nata sai ita kad'ai yadda zai ji dadin yi mata abunda ya shirya.
Kamar ko ya sani batare da ya tambayetaa ba ta fara rattaba masa Labarin abunda ya faru har ta na fad'in"Yo ni za'a kawo ma iskanci? Yarinya tun ta na jarriyarta Sulaimanu ya yi wahala da ita sai yau Rana Tsaka a wani ce gidansa za'a je daura aure in ya isa shegiya na ke, ai na ce in dai chan za'a je ni Dije ba da yawuna ba."
Kallonta kawai ya ke yi cikin tattaro mganar bakinsa, Cikin kaushim murya yace"Daman gidan Ubanta nan ne a hakku a daura mata aure."
Innani ta yi galala ta na kallonsa kafin tace"me ka ke nufi Magajin gida?
Kai Tsaye yace"Abunda na ke nufi a shinkafi za'a daura auran nan a kuma gidan mahaifin Sultana."
Innani ta ballamai Harara kafin tace"Au to daman turo ka suka yi ko?
To wlh wannan karon ba wanda ya isa nan gidan Sulaimanu nan za'a Daura wannan auran naga Uban da ya isa ya ce Ba haka ba."
Sadiq yace"Ba isa ba ne Innani, Sai dai ki sani matukar kika dage sai anan za'a Daura auran nan ni kuma wlh Tallahi kin ji na rantse miki da Allah zan fasa auran Sultana kuma da gaske na ke yi."
Sai Innani ta yi shuru ta kasa mgana, shi kuma ya kura mata ido ya na kallonta ganin ta yi shuru yasa ya cigaba da fadin"Ke shikenan bakya yafiya? Ki rika afuwa Innani Domin ke kam baki san Tarin laifukan ki wajen Allah ba, da Allah baya yafiya ma da Tuni An dade da shafemu a wannan Duniyar, ya kamata ki Sassuta ma kanki wannan kiyayyar in ba haka ba zaki Mutu ana murna da Mutuwarki."
Sai kawai Innani ta Fashe da kuka ta na Fadin"Ai shikenan na bar mganar ka gayama Sulaimanu na hakura aje a daura auran a shinkafi wlh na bar mganar har Abada."
Jinjina kai Sadiq ya yi kafin ya ce"Dakyau naji dadin haka , Ni ina so in kin mutu Ranar Lahira ki Rabauta kakata, na baki wani kissar da zai taimaka miki wajen cire jin haushin wani a ranki?
Bai bata Damar mgana ba ya Cigaba da fadin"A zamanin Annabi muhammad Sallahu alaihi wasallama, watarana ya na zaune acikin masallaci Tare da Sahabbai kawai sai Annabi yace ga dan Aljannah nan zai shigo, Sai Sahabbai suka yi shuru tare da kurama kofar masallaci ido su ga waye zai shigo.
Sai ga wani bawan Allah ya shigo cikin masallaci kuma bayan Shi ba wanda ya kara shigowa, sai abun ya ba ma Sahabbai mamaki da jin abunda Annabi yace, na cewa shi d'in d'an Aljanmah ne, sai cikin Sahabban Annabi wani ya bishi gida yace ya ba shi masauki na kwanaki sai ya bashi da niyar ya rika ganin wani irin Ibada ya ke yi da Tun a Duniya Annabi yace shi dan Aljanna ce, sai yaga duk tsawon kwanakin da suka yi tare ko sallar Dare ba ya gani yana yi ban da kamsil salatu a ranar na uku ne wannan Sahabin ya sameshi ya gayamasa abunda Annabi ya gayama su game da shi, Dalilin da yasa ya zo wajensa saboda yaga wani irin Ibada ya ke da har tun a duniya Allah ya bashi Aljannah.
Sai wannan bawan Allah ya yi Kabbara sau uku kafin yace" bai san har yakai haka ba, abu d'aya kawai ya sani Tunda ya ke bai taba kwana da wani a ransa ba duk abunda aka yi masa nan ta ke yake yafewa kwana yake zuciyarsa wasai ba kowa acikinta"
Dan dakatawa Sadiq ya yi ya na kallon Innani da ta natsu ta na ji harda jan Doguwar kabbara."Allahu Akbar" lokaci daya ta na faman sharan kwallah.
Sai Assadiq ya sauke ajiyar rai kafin yace"To kisance mai yawan yafiya Innani domin masu yawan afuwa Samakonsu na wajen Allah"
Da Sauri Innani tace"Allahu Akbar Wlh na yafe ma kowa Allah Sarki. na yafe ma kowa ni yanzu shima Shitun na yafe masa duniya da Lahira Magajin gida ni yanzu zuciyata wasai."
Sadiq yace"To ina fatan bazaki kara tada wata mgana ba.?
Da Sauri tace"In sha Allahu Magajin gida kai dai Allah ya yi maka albarka kawai."
Ya amsa da Ameen, Shikenan magana ta Mutu, sai dai su Abba sukaji sabon zencen Innani da kanta tace ko Bikin ma in chan za'a yi sai su kwasa su je gabadaya chan Abba yace nan dai za'ayi Sha'anin Daurin auran ne dai za'ayi achan.
Duk da bai fito ya fad'a ba kowa yasan aikin Magajij gida shine kawai Maganganunsa ke sa ka Innani Ladabi da Nadaman Dole, kafin kwana Biyu ta koma gidan jiya.
Ranar lahadi ya koma Abuja Da Safe ya tafi da cewa sai a satin biki zai dawo, sai da ya koma sannan ya Kira Tahir ya gayamasa ga inda za'a Daura auran Shima Tahir yace hakan ya yi daidai bisa adalci.
Duk Abba yaki karban komai sai da Mallam shitu ya aiko masa da Buhuhunan shinkafa da gero da masara yace ya karb'a ba Saboda sultana ya ba shi ba domin Allah ya ba shi sannan ya karb'a bayan Sadiq ya saka baki.