Sashe 14
Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Sadiq kunyar kallon Hasiya ya ke yi shiyasa ya kasa komawa.
Gefe d'aya Tahir na gayamsaa in ya cika zuwa za'a zo a samu matsala.
Wanda samuwarta bazai haifar masa da d'a mai ido ba.
Ya nuna ma Tahir ba wanda ya san shi anan ballatana yace ya na tsoron kada labari ya kai gusai.
Shi kuma Tahir ba ma wannan ne Tunaninsa ba yasan tunda nan din babu wanda yasan daga ina suke abokan karatunsu d'ai d'ai ku ne yan zariya duk yan wasu jahohin ne.
Gwara ma shi za'a iya sanin wanene shi ammh Sadiq tun farkonsa ba mai iya nuna kansa ko shi waye bane.
In ba na kusa da shi ba balle ka Fahimci wanene shi ba.
Shi Tsoron sa d'aya Kada Sadiq ya cigaba da shigema zabiyar yarinyar nan ta ribacesa ya fara sonta ko wani abu ya shiga tsakaninsu ta Bata masa Rayuwa.
Domin shi har ga Allah ya aminta da Mganar mutane akan Hasiya ballatana da yaji daga bakin iyayenta da yan'uwanta.
Ba rami fa ba abunda zai kawo mganar rami gwara dai tunda ya Riga ya kai kansa to a samu hanyar da zasu rabu lafiya shine kawai taimakon da zai iya yima Sadiq ya saka masa da Tarin alherinsa garesa.
Shi kuma Sadiq a lokacin ya zama wani ga shi nan ne abunda ya aikata ba da sanin iyayenshi ba ya fara Damunshi shiyasa duk abunda Tahir sai ya kasa masa musu, duk da yana jin Tausayin Hasiya fargabansa kada ciwo ko wani abu ya sameta cikin Dare ba bu wani a kusa da ita gida ita kad'ai, fargabansa ta ragu ne ma da yaga dakin kusa da ita mutane za su shiga da Sauki sauki zata rika jin motsin mutane.
Yanzu haka Dari dari ya ke da kiran Abba ko Umma sai yaji kamar suna kallonsa da abunda ya aikata batare da sanin su ba ko yarda ko kar ya yarda yaci Amanar iyayenshi da ya iya aikata babban al'amari batare da saninsu ba.
Baisan me ya shiga kansa ba har ya amince da auran Hasiya ba sai dai komai ya faru sannan ya dawo hayyacinsa.
Shiyasa ya rage kiransu a waya sai dai su su kirashi suma baya tsawaita mgana da su hakama Sauran Sisters dinsa kowa ya Fahimci yanzu Magajin gida ya sauya ya rage sakin jiki da su su sha hira ko a waya ammh sun masa uzuri Tunaninsa aiki ne ya yi masa yawa tunda ya kusa gama Hidimar kasar na shi..
Ya gama tsara yadda abubuwa za su cigaba da kasancewa gwara ya siyama Hasiya karamar wayar da zata kiran yan'uwanta ta na rage kewa kafin ya yi natsuwar da zai san irin taimakon da ya yi niyar yi mata na inganta Rayuwarta kafin su rabu.
Sannan shima zai rage fargaban ko wani abu zai sameta zai rika kiranta yana jin lafiyanta.
Sannan kuma in wani abu ya same ta ko ta na bukatar wani abu zata iya kiransa.
Shi kad'ai ya yi wannan tunanin shiyasa bai aiwatar ba sai da ya tambayi Tahir shawara.
Shi kuma sai yace shawaran tasa ta yi ya siya mata waya ammh sai ya gargadeta.
Sadiq ya kallesa cikin mamaki kafin yace"Gargad'in me?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Kada ta fallasa sirin zaman ku ga yan'uwanta ko kawayenta. Saboda in sukaji zasu dora ayar tambaya akan motsinka da kuma Dalilin ka."
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Hakane to ta ya zan ce mata kada ta gayama kowa?
Tahir yace"gayamata zaka yi kai tsaye."
Sadiq ya yi shuru bai yi mgana ba ya na Tunani Tahir yace"Kada dai ka gayamata mganar rabuwar ku yanzu sai mun kusa komawa gida tukunnah Lokacin ka bata taimakon da kace kaga bazata damu ba sosai."
Shi dai Sadiq bai amsa ma Tahir ba ammh kallonsa ya yi da mamaki yana jinsa ne kawai in yace wai bazata damu ba in suka rabu.
Aure sunan shi aure ko ya ya yake kuwa kuma saki ba shi dad'i ko da a fatar baki ne kuwa.
Da kansa yaje pizzet ya siya karamar waya Tecno dubu takwas tare da layi ya kuma yi mata Rigister bai kai mata ba sai da ya chaja mata ya saka mata lambarsa a wayar ya kuma yi saving da sunan da ta ke kiran shi ASSADIQ.
Gefe d'aya Tahir na gayamsaa in ya cika zuwa za'a zo a samu matsala.
Wanda samuwarta bazai haifar masa da d'a mai ido ba.
Ya nuna ma Tahir ba wanda ya san shi anan ballatana yace ya na tsoron kada labari ya kai gusai.
Shi kuma Tahir ba ma wannan ne Tunaninsa ba yasan tunda nan din babu wanda yasan daga ina suke abokan karatunsu d'ai d'ai ku ne yan zariya duk yan wasu jahohin ne.
Gwara ma shi za'a iya sanin wanene shi ammh Sadiq tun farkonsa ba mai iya nuna kansa ko shi waye bane.
In ba na kusa da shi ba balle ka Fahimci wanene shi ba.
Shi Tsoron sa d'aya Kada Sadiq ya cigaba da shigema zabiyar yarinyar nan ta ribacesa ya fara sonta ko wani abu ya shiga tsakaninsu ta Bata masa Rayuwa.
Domin shi har ga Allah ya aminta da Mganar mutane akan Hasiya ballatana da yaji daga bakin iyayenta da yan'uwanta.
Ba rami fa ba abunda zai kawo mganar rami gwara dai tunda ya Riga ya kai kansa to a samu hanyar da zasu rabu lafiya shine kawai taimakon da zai iya yima Sadiq ya saka masa da Tarin alherinsa garesa.
Shi kuma Sadiq a lokacin ya zama wani ga shi nan ne abunda ya aikata ba da sanin iyayenshi ba ya fara Damunshi shiyasa duk abunda Tahir sai ya kasa masa musu, duk da yana jin Tausayin Hasiya fargabansa kada ciwo ko wani abu ya sameta cikin Dare ba bu wani a kusa da ita gida ita kad'ai, fargabansa ta ragu ne ma da yaga dakin kusa da ita mutane za su shiga da Sauki sauki zata rika jin motsin mutane.
Yanzu haka Dari dari ya ke da kiran Abba ko Umma sai yaji kamar suna kallonsa da abunda ya aikata batare da sanin su ba ko yarda ko kar ya yarda yaci Amanar iyayenshi da ya iya aikata babban al'amari batare da saninsu ba.
Baisan me ya shiga kansa ba har ya amince da auran Hasiya ba sai dai komai ya faru sannan ya dawo hayyacinsa.
Shiyasa ya rage kiransu a waya sai dai su su kirashi suma baya tsawaita mgana da su hakama Sauran Sisters dinsa kowa ya Fahimci yanzu Magajin gida ya sauya ya rage sakin jiki da su su sha hira ko a waya ammh sun masa uzuri Tunaninsa aiki ne ya yi masa yawa tunda ya kusa gama Hidimar kasar na shi..
Ya gama tsara yadda abubuwa za su cigaba da kasancewa gwara ya siyama Hasiya karamar wayar da zata kiran yan'uwanta ta na rage kewa kafin ya yi natsuwar da zai san irin taimakon da ya yi niyar yi mata na inganta Rayuwarta kafin su rabu.
Sannan shima zai rage fargaban ko wani abu zai sameta zai rika kiranta yana jin lafiyanta.
Sannan kuma in wani abu ya same ta ko ta na bukatar wani abu zata iya kiransa.
Shi kad'ai ya yi wannan tunanin shiyasa bai aiwatar ba sai da ya tambayi Tahir shawara.
Shi kuma sai yace shawaran tasa ta yi ya siya mata waya ammh sai ya gargadeta.
Sadiq ya kallesa cikin mamaki kafin yace"Gargad'in me?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Kada ta fallasa sirin zaman ku ga yan'uwanta ko kawayenta. Saboda in sukaji zasu dora ayar tambaya akan motsinka da kuma Dalilin ka."
Sadiq ya yi shuru kafin yace"Hakane to ta ya zan ce mata kada ta gayama kowa?
Tahir yace"gayamata zaka yi kai tsaye."
Sadiq ya yi shuru bai yi mgana ba ya na Tunani Tahir yace"Kada dai ka gayamata mganar rabuwar ku yanzu sai mun kusa komawa gida tukunnah Lokacin ka bata taimakon da kace kaga bazata damu ba sosai."
Shi dai Sadiq bai amsa ma Tahir ba ammh kallonsa ya yi da mamaki yana jinsa ne kawai in yace wai bazata damu ba in suka rabu.
Aure sunan shi aure ko ya ya yake kuwa kuma saki ba shi dad'i ko da a fatar baki ne kuwa.
Da kansa yaje pizzet ya siya karamar waya Tecno dubu takwas tare da layi ya kuma yi mata Rigister bai kai mata ba sai da ya chaja mata ya saka mata lambarsa a wayar ya kuma yi saving da sunan da ta ke kiran shi ASSADIQ.