← Book details Tmw Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 11 OF 75

Sashe 11

Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"ASSADIQ.."

Kayan Tea din na saka su cikin dirowan kitchen din, Gas din kuma na sama ma wajen zama zan kunna.
Sai kuma naga ba ashana sai idona ya raina fata, sai da na kara duba kayan da ya shigo da shi naga ashana sannan na kunna gas din na dora ruwan zafi cikin karaman tukunya na jira har ya tafasa na kashe gas din na samu karamin kofi na shiga na had'a tea na yanki buredi na fito falo na zauna kan kujera ina sha.
Gabadaya kadaici ya dameni ga shi ni ba waya ba sai yau na karajin takaicin da a baya Amma ta matsamin sai na siya waya na ki bin shawaranta.
Da ace na siya da yanzu na kira su mun yi mgana.
A zatona su Adda Fati za su zo min ammh sai ga shi har yamma ko kare ban gani ba sai dai haushin na makota masu manyan gidaje.
Sai dai na zauna nayi zuru tunanin duniya sun rufeni ina tunanin shi kuma wannan auran nawa ya sunan shi?
Kila shi kuma ahaka zai kare shima.
Sai dare na samu na Dafa taliya da mai da yaji tunda ba ni da kayam miya sannan ban ga ko almajiri ba ballatana na samu yaron aike.
Sai da dare ya yi na kara raina kaina a firgice na kwana kuka na sha har barci ya kwasheni shiyasa na tashi da Fuska duk ta yi ja.
Sannan ga sauro duk sun cicijeni ba maganin sauro.
Babu kuma wayar da zan samu na kira ko Adda Fati Allah Sarki ashe mutane Rahma ne.
Ni kadai acikin wannan gidan har na tsawon kwana Hudu ko kafar dakina ba na fita komai aciki na ke yi.
Barci duk sama sama ne kuma a firgice ko motsin iska naji ya taba get haka zan fara rawan jiki da na zuciya.
Ba Labarin Assadiq ba labarin su Adda sai ranar da kwana biyar da Safe sai ga Ramatu
Ashe ta jima ta na buga get ban ji ba ina wanka sai da ta zagaya ta bayan gida wajen falt dina ta rika kwalamin kiran sannan na jita.
Na fita naje na bude mata kofa haka na Rumgumeta ina murnan ganinta.
Ranar Ramatu tamin yini ina ta korafin ba su kara nema na ba.
Ramatu tace"Saboda menene zamu nemeki? Haka kurun ango na armaci mu takura masa"
Kallonta kawai nayi na kasa bude baki na fad'a mata tun washegarin da suka kawoni wannan gidan ban kara ganin Assadiq ba ammh sai naji na kasa gayamata gaskiya.
Har kuma tambaya ta yi ina ya ke? Nace mata ya fita ba da dadewa ba.
Ta shiga ko'ina ta na min murna tunda muna da ruwa.
Yini muka yi hira bayan na yi mana girki mun ci ina goye da Noor kamar ta barmin ita.
Ashe Adda ta koma Shekaranjiya shine ba wanda ya neme ni ya sanar dani.
Ramatu ke fad'amin matan gidanmu na son zuwa suna ta ma Inna talatu mgana.
Da sauri nace"Don Allah su zo ina son ganin su."
Ramatu ta yi dariya ba ta yi mgana nasan zata ce saboda kad'aici ne ba dadi.
Da wayarta na samu na kira Adda Fati ina rokonta da Allah tazo tace ba yanzu ba sai nace to ta turomin Habiba ta zo min da kayan miya bani da shi jin haka yasa tace sai gobe zata zo in ta dawo daga makaranta.
Sai mangariba Ramatu ta tafi kuma ni na rakata har bakin titi na ga anguwan sosai ba wasu yalwar jama'a sosai sai da ta samu adaidaitan sannan na dawo gida.
Washegari gari wajajen la'asar sai ga Habiba da Hanif sun kawomin kayan miya mai yawa.
Da sun so tafiya da wuri na rike su sai shidda na barsu suka tafi.
Yanzu neman mutane na ke yi ido a Rufe ban samu ba.
Sai da ranar da na cika Sati da wuri Adda Rukkaya ta zo min yini ba ta jima da zuwa ba sai ga Inna talatu da matan gidammu.
Duk da gulma ya kawosu haka na rika washe bakinsu ganinsu naga jama'a.
Ba inda ba su leka ba sannan ba su ga wani alaman wahala ko damuwa tare dani ba sai mamaki suke yi.
Sai dai sun ta tambayana ina angon? Ana so aji labari ni kuma naki ba su wani dama da zasu fahimci wannan karon abubuwan sun sha Bambam.
Sai yammah suka tafi Adda Rukayya ta riga su tafiya saboda mijinta.
Ta kawomin kalolin maggi da su korin kamshin girki.
Ta tambayeni ba matsala nace mata ba wata matsala.
Nasan suma a firgice suke ba sa son su kara jin wani abu kuma ya faru.
Ni kuma ba na so na tada musu  hankali ai da na fad'u musu wannan karon ba irin na sauran ba ne.
Har na kwana goma ban kara saka Assadiq a idona ba duk sai na damu.
In har ya sakeni ne gwara ya fad'amin da wannan zaman da na ke yi ba wani a tare da ni.
Sai kuma daga baya na fara Tunanin ko wani abu ya faru da shi ne bansani ba?
Ina cikin wannan firgicin ne da yammah naji ana buga gida.
Da sauri na saka Hijabi na fita jikina na rawa na Dauka ASSADIQ ne ashe ba shi ba ne.
Saboda rudewa ko tambayan waye ban yi ba na bude get.
Sai kawai na ci karo da wata mata yar babba haka.
Tamin mirmishi na yi mata ni na fara gaisheta ta amsa cikin sakewa kafin tace"Mun kawo kaya ne"
Cikin mamaki na kalleta ban samu zarafin mgana ba tace"Yarmu ce zata zauna a d'aya daga cikin flat din gidan"
Ina jin haka kamar an min bushara da gidan Aljannah
Da sauri na bata hanya ina fad'in"Sannun da zuwa."
Shigowa ta yi ni kuma na leka ina ganin motar kaya cike da kayan su kujeru da gado sannan na Rufe get din.
Matar na da fara'a ita ta gayamin ita ta fara yin gaba da motar kayan sauran matan suna hanya a daidaita za su zo yanzu ma surukin na su take jira ya kariso ya bata makulin dakin tare da yaran da zasu taimaka a kwashe kaya..
Jin haka yasa na ce ta shigo dakina ta yi tamin godiya kuwa.
Na kaita har dakina ta zauna na bata ruwa.
Na zo na zauna ta na min hira irin matan ne masu shigen surutu.
Daga zuwanta har sunan Amaryan ta fad'amin Fatima ana ce mata Ummi.
Har ta kayan dakin da aka siya mata sai da ta lissafa min.
Sannan ta gayamin ita kanwar babanta ce a saudiya ta ke zaune tazo ne.
Ni ban tambayeta ba ammh har ta fesamin Ummi ta gama Digree d'inta anan Abu zaria.
Koyarwa ta ke yi a wata makarantan Secondary a sabon gari.
Surukin na su kuma ma'aikacin gwammati ne a nan zariya.
Cikin jiran awa dayan da tayi ne fa duk ta sauke min wannan labarin.
Ni ko ina zaune ina jinta Eh a'a sai ko mirmishi.
gidan haya mai tara jama'a da Mutane kala kala.

*Janafty*
*TMWB2K005*

*TMW is a paid Novel, Pay 500 for regular or VIP N1K, Via 0552179550 Jamila Umar Gt bank, 09069067488*

https://chat.whatsapp.com/BARBh2begGc0KdlLEZDzhk

Ku zo ku yi sayayya tare da Yar Gidan Imam cikin aminci da kwanciyar hankali komai akwai harda kayan gyaran jiki hamshakan mata na supliments kala kala wanda ba su da illa, akwai kuma gagarumin haɗin mu na Arabian sabaya powder wanda babu kamarsa wannan ba irin sabayar da ki ka saba gani bace, kayan kicin dogayen riguna kuwa ba'a magana ke dai ki yi sauri ki shigo domin kwasar roman wadannan kayan.

Sai da Surukin na su yazo da yaran da zasu kwashe kayan zuwa cikin gida sannan ta min sallama ta fito daga dakina ni dai ban fito ba.
Ammh naji ba jimawa sauran tawagan da tace suna hanya suma suka iso, na leka ta window na gansu Rurututu kamar a nan ake yinin biki kusan zazzagawa akwai kara.
Duk ina cikin daki naji an fara shigowa da kayan dakin cikin gida ba gulma ba na mike na saka gwiyoyina saman kujera ina leken su.
Kaya ne na alfarma ma su kyau burin kowacce macen da ta isa har aka kira mangariba ba su gama shigo da kayan nan ba shiyasa na koma daki na Dauro alwala na yi sallah.
Ina kan darduma naji ana kwankwasamin kofa na tashi da hijabin jikina na fita na bude sai naga wannan matar da ta ce min sunanta Zainab.
Chapter 11 · 0% Book details