Sashe 40
Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Bayan na idar na koma na zauna kawai na jingina da kujera, na kasa ma addu'a na kuma rasa irin addu'an ma da zan yi sai kawai na koma na yi shuru ina jin cikina na kugin yunwa.
Daman jiya da Daddare ban yi abinci ba taliyar da na Daface tayi saura sai naci da daddare.
Shine da Safe na tashi na Dafa shinkafa da wake ko ci ban tsaya yi ba na fita kaima Ummi, shine suka Fahimtar dani cewa ni Annoba ce maganina sai Allah.
Ba ni da karfin gwiwan cin wani abincin bakina kuma ya yi takaf kamar wacce ta tashi jinya.
Shiyasa ban yi wani yunkurin tashi na taimaki kaina ba, a raina nace in yunwa ce ta kasheni ban mutu kafura ba in dai ko hakane bazan kara cin abinci ba ballatana na sha Ruwa har sai Ubangiji ya Dauki raina domin na gaji da wannan rayuwar.
Ina jin ana ta sake kiran wayata ammh yadda jikina ya nemi ya fara saki ne yasa ban ko iya jirgirtawa kusa da wayar ba, ballatana nasan wake kira a tunanina ko Adda Fati ne ban taba Tunanin Assadiq zai damu ba, ballatana har ya cigaba da kiran wayata a kai a kai ba.
Wayar ta na yankewa naji ana bugamin kofa, ko ina iya tashi ma da karfin jikina bazan tashi ba domin Tunanina ya gama gayamin su Ummi ne sun dawo ne domin su kara cin zarafina kamar yadda suka yi a farko.
Ina jin ana bugun da karfi sai kawai na kara fashewa da kuka.
A fili na furta"Innalilillahi wani'inna ilaihirraju'un ni Hasiya yaushe zan huta daga wannan bala'in ne? Daga wannan sai wannan?
Haka na ke fad'a a fili ina gunjin kuka lokaci daya ina had'e kaina a gefen kujera kamar wata marainiyar da ta rasa komai, Eh mana marainiyar ce mana tunda ba ni da Uba sannan ba ni da wani bangon abun jingina na.
Kamar wasa sai naji kuma ana Buga kofar dakina kuma ana Kiran sunana.
Shiyasa na mike a kasalance kamar zan fad'i, na nufi kofar dakin na bude da Niyar na yi shuru har su ummi su gama fad'in abunda za su fad'i su tafi.
Sai dai kuma me? Ina bude kofar ban tsaya kallon wajen ba na juya baya na ina sharan hawayena.
Sai jin tattausan muryansa na yi ya na fad'in"Hasiya me ya faru? Amma ce ciwonta ya tashi?
Da sauri na juyo muka had'a ido Hudu da shi ban taba Tunanin ganinsa ba.
Yana sanye cikin Riga da wando,Rigar Ash ce mai ruwan kasa sannan akwai Dogon Hannu,sannan sai bakin wando a jikinsa,sai karamin akwatin Trolley a hannunsa da jakarsa goye a bayansa.
Na kasa mgana illah kallonsa da na ke yi wasu hawayen na kara ambaliya a saman Fuskata.
Shi kuma daman ashe bugawar kofata da ya dinga yi da karfi ya fito da su Ummi Daga Dakunansu suna ta kallonsa ita da Fadila, shiyasa ya yi saurin shigowa cikin Dakin Lokaci d'aya ya maida kofar ya kulle.
Ni kuma da gudu na koma falo na zube a kasa ina gunjin kuka, cikin tashin Hankali ya sauke akwatin hannunsa lokaci d'aya da jakar bayansa ya Nufeni.
Duk a Tunaninsa wani abu ne ya samu Amma zuciyarsa na fatan Allah yasa ba ta rasu ba ne.
Tun sanda ya kirani yaji ina kuka kuma yana ta kara kira ban Dauka ba sai hankalinsa ya tashi, Baisan ya akayi ba kawai ya fara shirya kayansa ba shi dai yaji ya kasa natsuwa abunda ransa ya kawo masa wani abu ya samu Amma ko na ciwo ko na Mutuwa.
Yaji hankalinsa ya tashi, ya kasa samun natsuwa da sukuni, ya san cewa Hasiya ba ta da wani abunda ta ke kaunar bayan mahaifiyatan rasata ko wani abu ya sameta babban tashin Hankaline a gareta.
Shiyasa ya shirya tahowa Zariya batare da shawara da ko zuciyarsa ba Ruhinsa ne kawai ke jansa zuwa ga Hasiya.
Abba ma baya gida Umma ce kad'ai ya samu ya yi ma sallama itama sai da ta yi ta nanata tafiyarsa har dai ta kare ta baya ce zai jima a gida ba wannan karon? Kai tsaye yace mata daga wajen da ya ke hidimar kasa ne suka Kira shi, Umma dai ba yarda ta iya illa rakasa da addu'an Allah ya tsare.
Innani da mama bai samu shiga bangaransu ba tsabar yadda ya matssu ya gansa a zariya suna mota ji yake yi kamar ya yi tsuntsuwa ya gansa a gaban Hasiya.
A gabana ya duka cikin Damuwar da ta bayyana har a saman fuskarsa sannan ta nuna kanta a cikin muryansa, Cikin wani yanayi ya fara kiran sunana.
"Hasiya.. Hasiya."
Ina jinsa na kasa amsa masa saboda kukan da ya ke murkukusan raina a lokacin, ganin ban amsa kiran da ya yi min ba yasa ya saka Hannuwansa ya Dago Fuskata da ta kumbura ta yi jajir saboda kuka ya na kallona cikin sanyim murya yace"Me ya faru? Amma ce?
Ya fad'a lokaci daya yana bubbuga kumatuna idanuwana na Runtse sai ga hawaye sharr, sun sake zubomin cikin shakewar murya nace"Amma na lafiya, ba ita ba ce ni ne."
Daganan sai kawai sai na kara fashewa da kuka wannan karon harda Sauti kamar wata karamar yarinya.
Cikin damuwa ya tarairayoni a jikinsa ya na fad'in"Me ya same ki Hasiya? Ko baki da lafiya ne?
Ya ke fad'a ya na kokarim kama Fuskata da hannayensa duka Biyun ni kuma ina zillewa kokarina na koma kasan tayels din na kwanta na cigaba da kukana, shi kuma ya hanani sai Faman Rikeni ya ke yi, ya na kuma ta maimaitamin tambayan me ke damuna? Ko ba ni da lafiya ne?
Dakyar na yarda ya rikeni dakyau a cikin jikinsa, sannan fuskata na cikin Tafukan Hannayensa cikin tashin Hankali a muryansa ya kira sunana "Hasiya.."
Dakyar na bude kumburarrun idanuwana ina kallonsa cikin Muryansa mai cike da Sanyi yace"Gayamin me ke faruwa? Wani abu ne ya same ki? Ko baki da lafiya me?
Sai kuma hawaye sharr, kamar an bude famfo, ina kokarin kara zille masa ya kara rikeni gam ya na fadin"Me ya faru Hasiya?
Cikin kakkausan murya da alamu ya fara gajiya da jiran amsata.
Sai da na bud'e idanuwana jajir ina kallonsa ido cikin ido sannam muryata a shake nace"ASSADIQ...."
Sai kuma na kasa karisawa cikin kosawa yace"Menene Hasiya?
Cikin kuka nace"Ka sake ni. Don Allah ka sakeni Assadiq."
Gabansa ya yi wani Rugugu ya fad'i kuramin ido ya yi a ransa sai ya fara Tunanin ko dai nasan shirinsa ne na sakina nan da Lokaci kad'an?
Yana wannan Tunanin na katseshi da cewa"Gwara ka sakeni saboda ina son ka tsira da lafiyarka. Ban taba jin fargaban kada wani abu ya samu wani ba irin yadda na ke fargaban kada wani abu ya sameka ba"
Cikin ido muke kallon juna kafin yace"Me ya kawo wannan mganar kuma?
Kwace jikina nayi na koma gefe na jingina da kujera ina kuka cikin kukan na fara gayamasa abunda ya Faru Tsakanina da su Ummi na karishe da Fad'in"Ba na son wani abu kaima ya sameka shiyasa gwara ka sauwake min ka yi tafiyarka ka rabu dani Tun kafin wani abu ya sameka.
"Ba abunda zai sameni face abunda Ubangijina ya kaddaramin Hasiya."
Daman jiya da Daddare ban yi abinci ba taliyar da na Daface tayi saura sai naci da daddare.
Shine da Safe na tashi na Dafa shinkafa da wake ko ci ban tsaya yi ba na fita kaima Ummi, shine suka Fahimtar dani cewa ni Annoba ce maganina sai Allah.
Ba ni da karfin gwiwan cin wani abincin bakina kuma ya yi takaf kamar wacce ta tashi jinya.
Shiyasa ban yi wani yunkurin tashi na taimaki kaina ba, a raina nace in yunwa ce ta kasheni ban mutu kafura ba in dai ko hakane bazan kara cin abinci ba ballatana na sha Ruwa har sai Ubangiji ya Dauki raina domin na gaji da wannan rayuwar.
Ina jin ana ta sake kiran wayata ammh yadda jikina ya nemi ya fara saki ne yasa ban ko iya jirgirtawa kusa da wayar ba, ballatana nasan wake kira a tunanina ko Adda Fati ne ban taba Tunanin Assadiq zai damu ba, ballatana har ya cigaba da kiran wayata a kai a kai ba.
Wayar ta na yankewa naji ana bugamin kofa, ko ina iya tashi ma da karfin jikina bazan tashi ba domin Tunanina ya gama gayamin su Ummi ne sun dawo ne domin su kara cin zarafina kamar yadda suka yi a farko.
Ina jin ana bugun da karfi sai kawai na kara fashewa da kuka.
A fili na furta"Innalilillahi wani'inna ilaihirraju'un ni Hasiya yaushe zan huta daga wannan bala'in ne? Daga wannan sai wannan?
Haka na ke fad'a a fili ina gunjin kuka lokaci daya ina had'e kaina a gefen kujera kamar wata marainiyar da ta rasa komai, Eh mana marainiyar ce mana tunda ba ni da Uba sannan ba ni da wani bangon abun jingina na.
Kamar wasa sai naji kuma ana Buga kofar dakina kuma ana Kiran sunana.
Shiyasa na mike a kasalance kamar zan fad'i, na nufi kofar dakin na bude da Niyar na yi shuru har su ummi su gama fad'in abunda za su fad'i su tafi.
Sai dai kuma me? Ina bude kofar ban tsaya kallon wajen ba na juya baya na ina sharan hawayena.
Sai jin tattausan muryansa na yi ya na fad'in"Hasiya me ya faru? Amma ce ciwonta ya tashi?
Da sauri na juyo muka had'a ido Hudu da shi ban taba Tunanin ganinsa ba.
Yana sanye cikin Riga da wando,Rigar Ash ce mai ruwan kasa sannan akwai Dogon Hannu,sannan sai bakin wando a jikinsa,sai karamin akwatin Trolley a hannunsa da jakarsa goye a bayansa.
Na kasa mgana illah kallonsa da na ke yi wasu hawayen na kara ambaliya a saman Fuskata.
Shi kuma daman ashe bugawar kofata da ya dinga yi da karfi ya fito da su Ummi Daga Dakunansu suna ta kallonsa ita da Fadila, shiyasa ya yi saurin shigowa cikin Dakin Lokaci d'aya ya maida kofar ya kulle.
Ni kuma da gudu na koma falo na zube a kasa ina gunjin kuka, cikin tashin Hankali ya sauke akwatin hannunsa lokaci d'aya da jakar bayansa ya Nufeni.
Duk a Tunaninsa wani abu ne ya samu Amma zuciyarsa na fatan Allah yasa ba ta rasu ba ne.
Tun sanda ya kirani yaji ina kuka kuma yana ta kara kira ban Dauka ba sai hankalinsa ya tashi, Baisan ya akayi ba kawai ya fara shirya kayansa ba shi dai yaji ya kasa natsuwa abunda ransa ya kawo masa wani abu ya samu Amma ko na ciwo ko na Mutuwa.
Yaji hankalinsa ya tashi, ya kasa samun natsuwa da sukuni, ya san cewa Hasiya ba ta da wani abunda ta ke kaunar bayan mahaifiyatan rasata ko wani abu ya sameta babban tashin Hankaline a gareta.
Shiyasa ya shirya tahowa Zariya batare da shawara da ko zuciyarsa ba Ruhinsa ne kawai ke jansa zuwa ga Hasiya.
Abba ma baya gida Umma ce kad'ai ya samu ya yi ma sallama itama sai da ta yi ta nanata tafiyarsa har dai ta kare ta baya ce zai jima a gida ba wannan karon? Kai tsaye yace mata daga wajen da ya ke hidimar kasa ne suka Kira shi, Umma dai ba yarda ta iya illa rakasa da addu'an Allah ya tsare.
Innani da mama bai samu shiga bangaransu ba tsabar yadda ya matssu ya gansa a zariya suna mota ji yake yi kamar ya yi tsuntsuwa ya gansa a gaban Hasiya.
A gabana ya duka cikin Damuwar da ta bayyana har a saman fuskarsa sannan ta nuna kanta a cikin muryansa, Cikin wani yanayi ya fara kiran sunana.
"Hasiya.. Hasiya."
Ina jinsa na kasa amsa masa saboda kukan da ya ke murkukusan raina a lokacin, ganin ban amsa kiran da ya yi min ba yasa ya saka Hannuwansa ya Dago Fuskata da ta kumbura ta yi jajir saboda kuka ya na kallona cikin sanyim murya yace"Me ya faru? Amma ce?
Ya fad'a lokaci daya yana bubbuga kumatuna idanuwana na Runtse sai ga hawaye sharr, sun sake zubomin cikin shakewar murya nace"Amma na lafiya, ba ita ba ce ni ne."
Daganan sai kawai sai na kara fashewa da kuka wannan karon harda Sauti kamar wata karamar yarinya.
Cikin damuwa ya tarairayoni a jikinsa ya na fad'in"Me ya same ki Hasiya? Ko baki da lafiya ne?
Ya ke fad'a ya na kokarim kama Fuskata da hannayensa duka Biyun ni kuma ina zillewa kokarina na koma kasan tayels din na kwanta na cigaba da kukana, shi kuma ya hanani sai Faman Rikeni ya ke yi, ya na kuma ta maimaitamin tambayan me ke damuna? Ko ba ni da lafiya ne?
Dakyar na yarda ya rikeni dakyau a cikin jikinsa, sannan fuskata na cikin Tafukan Hannayensa cikin tashin Hankali a muryansa ya kira sunana "Hasiya.."
Dakyar na bude kumburarrun idanuwana ina kallonsa cikin Muryansa mai cike da Sanyi yace"Gayamin me ke faruwa? Wani abu ne ya same ki? Ko baki da lafiya me?
Sai kuma hawaye sharr, kamar an bude famfo, ina kokarin kara zille masa ya kara rikeni gam ya na fadin"Me ya faru Hasiya?
Cikin kakkausan murya da alamu ya fara gajiya da jiran amsata.
Sai da na bud'e idanuwana jajir ina kallonsa ido cikin ido sannam muryata a shake nace"ASSADIQ...."
Sai kuma na kasa karisawa cikin kosawa yace"Menene Hasiya?
Cikin kuka nace"Ka sake ni. Don Allah ka sakeni Assadiq."
Gabansa ya yi wani Rugugu ya fad'i kuramin ido ya yi a ransa sai ya fara Tunanin ko dai nasan shirinsa ne na sakina nan da Lokaci kad'an?
Yana wannan Tunanin na katseshi da cewa"Gwara ka sakeni saboda ina son ka tsira da lafiyarka. Ban taba jin fargaban kada wani abu ya samu wani ba irin yadda na ke fargaban kada wani abu ya sameka ba"
Cikin ido muke kallon juna kafin yace"Me ya kawo wannan mganar kuma?
Kwace jikina nayi na koma gefe na jingina da kujera ina kuka cikin kukan na fara gayamasa abunda ya Faru Tsakanina da su Ummi na karishe da Fad'in"Ba na son wani abu kaima ya sameka shiyasa gwara ka sauwake min ka yi tafiyarka ka rabu dani Tun kafin wani abu ya sameka.
"Ba abunda zai sameni face abunda Ubangijina ya kaddaramin Hasiya."