Sashe 13
Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Yadda na kira sunan shi cikin karyewan Sauti ne yasa sai da ya samu kanshi da dukawa a gabana ya na kallon cikin kwayan idanuwana yace"Menene? Ko baki da lafiya ne?
Kai na girgiza masa kafin nace"Yau ma tafiya zaka yi ka bar ni?
Sadiq yaji kamar an kwarara masa ruwan sanyi saboda yadda jikinsa ya yi wani sanyi kalau.
Hucin zafi ya fitar daga bakin shi kafin yace"Hasiya ba na gayamiki yanayin aikin nawa ba?
Nan ya yi min nisa da wajen aikina ne sannan muna yawan tafiye tafiye ne ni da ubangidana."
So na ke ya kalleni ne ammh ya kasa kallona cikin idanuwana kansa na kallon kasa ne kwata kwata ya ki yarda ya had'a ido da ni.
Ganin haka yasa na kasa bud'e baki na yi mgana saboda ba ni da abun cewa.
Shi kuma nauyin jiki yasa ya kasa tashi ji ya ke yi kamar bai kyauta ba yana ji kamar wannan tsarin na shi ba tsari ba ne mai kyau.
Hakkin Hasiya na kanshi in ya aikata mata ba daidai ba Allah zai tambayeshi.
Bazai iya bude baki ya gayamata cewa auran su ba kamar yadda ta zata ba ne ya kasa yi ma Amma gaddama ne yasa ya karb'i auranta bazai iya gayamata cewa kafin ya gama Hidimar kasarsa nan da wata shidda sakinta zai yi ba.
Da sauri ya mike sai da ya juya mata baya yace"Ki yi hakuri zan rika zuwa ina dubaki Lokaci bayan Lokaci. Kuma ma ba ga shi kin samu abokiyar zama ba?
Bayansa na bi da kallo kafin nace"Hakane."
Jin na amsa shi yasa ya juyo ya na Fadin"Zan tafi. Ki kula da kanki in ban zo gobe ba jibi zan zo in sha Allahu."
Da toh na amsa masa ya fara tafiya ya na fadin"Taho ki kulle kofar.".
Ba musu na mike rike da kudin da ya ijiyemin a saman jikina har zuwa bakin kofa ya na fita ya juyo ya na kallona ni kuma ina rike da kofa kamar zan yi kuka.
Ganin haka yasa ya Rausayar da kai ya na fadin"Babu fa wani abu ki rika addu'a in zaki kwanta sannan ki rika Rufe kofarki kada ki bude ma wanda baki sani ba ok?
Jinjina masa kai na yi shi kuma sai ya zura hannayensa cikin Aljihun sa gabadaya kafin yace"Sai da Safe."
Nima na bi shi a sanyaye da Sai da Safe.
Har ya juya ya fara tafiya ina Tsaye bansan Lokacin da na kira sunan shi ba"ASSADIQ.."
Da Sauri ya juyo ya na kallona cikin mamaki.
Dawowa ya yi kofar dakin ya na fadin"Menene?
Kaina na kasa nace"Na koma wajen su?
Cikin mamaki yace"Wajen su wa?
Da hannu na nuna masa dakin da ke gefena da mu ke jin hayaniya.
Bi na ya yi da kallo cikin nazarina kafin yace"A'a ki zauna a dakin ki kin ji ko?
Saboda ya na tsoron kada naje su gane yanayi na su tambayane ni nw fad'amusu mijina baya kwana a gidan tunda muka tare.
Duk da rai na bai so ba ammh sai na Hakura tunda yace a'a bai tafi ba sai da yasakani na koma ciki na Rufe kofa sannan ya fita daga gidan ya na sauke numfashi.
Karfi da yaji halayensa na so su gurbace Sanadin haduwarsa da Hasiya ya fara karya da kumbibiya ya fara kokarin zama munafukin Namiji.
Ni ko ina kulle kofata ciki na shige na Dauro alwala na yi sallar isha'i sama sama nayi addu'a sannan na fito falo na duba ledar da yazo da shi tsireni mai uban yawa da yaji kuli da albasa da kokumba sai kyalli ya ke yi ga shi da zafi inaga da zai taho ya tsaya a siya.
Sai kuma Lemun fanta da maltina masu sanyi suma.
Miyau na har ya na tsinkewa ko samun daman Dauko Filet ban yi ba na zauna na fara ci sai da naji cikina ba waje daman ban yi girki da rana ba Taliya dawake na dafa da Dadddren jiya ita na Dumama da Safe da ta ragu ne na ci da Rana.
Na rage kusan rabi na kulle shi a ledan na kai kitchen na boye ban sha ruwa ba Maltina nan na shanye duka na yi gyatsa na koma na jingina da kujera ina maida numfsshi.
A bun ka ga wanda ya ci ya koshi sai naji na fara jin barci sama sama sai na tashi na haye saman kujera na kwanta ba jimawa sai barci.
Bansan na jima ina barci ba sai da naji bugun kofata kamar a sama na tashi a firgice kuma a tsorace.
Tashi na yi naje na bud'e sai naga Hajiya zainab matar nan masu danki.
Ashe sallama za su min sun gama zasu tafi sannan ta dawo min da jug dina da Kofina.
Na karb'a cikin murya barci muka yi sallama da juna har ta na cewa a gaida megidan rashin sani bata san ni kad'ai ce acikin dakin ba.
Maida kofata na yi na kulle saboda barcin da ke idona nan falo na ijiye jug din na shige ciki na kwanta ko kayan Jikina ban cire ba.
Washegari ma ban tashi da wuri ba, barci na sha sosai sai wajen goma na tashi, ban dafa komai ba Sauran tsiren nan na du'mama a tukunya na ci na sha Lemu fanta duk da ina da Ulcer ma naji ina Sha'awan lemum shiyasa na sha.
Da rana kuma Macaroni na Dafa jalop guda daya, naci ni kadai a gida sai da yammah wasu matan suka kara zuwa sun kawo wani kaya ba su jima ba dai suka tafi.
Kuma har dakina suka shigo muka gaisa na ba su ruwa suna ta min godiyan Dawainiya.
Wata mata acikin su ta kalleni ta na Fad'in"Ai ba ma zata wuce sa'an Ummi ba."
Ta gefenta tace"Nima haka nace acikin raina."
Su naji suna hiran su na ko a baya an daga bikin ne suna ta fad'in ba ga shi har Lokaci ya yi ba satin nan ne bikin da Daurin aure.
Acikin raina murna na ke yi kamar wacce za'a kawo wata yar'uwata.
Ko bakomai zaman kadaici bazai kasheni ni kad'ai ba.
Assadiq yace gobe ko jibi zai dawo ammh Shuru bai dawo ba ni ko har ina ta tsammanin shi.
Na fara tunanin meyasa bazai kwana anan ba? Hujjar da ya ba ni ba hujja bace mai karfi tunda muna gari daya ne ba wani gari ba ne zuwa wani gari ba.
Indai ko hakane ya na da dalilinsa na yin haka, kila ko ya na gujema hakanan ne saboda Canfin da ke kaina.
In dai ko zai cigaba da tsira da lafiyarsa gwara nesa nesa da kusa kusan nan da baya haifar da d'a mai ido.
Tunanin haka yasa na cire abun a raina na rika zirga zirgata.
ina kewar yan'uwa mussaman ma Amma ina so na kirata mu yi mgana na roketa ta yafemin domin na tabbata gatan da ta yi min ban da ita ba wanda zai iya yi min wannan gatan.
*****
Kai na girgiza masa kafin nace"Yau ma tafiya zaka yi ka bar ni?
Sadiq yaji kamar an kwarara masa ruwan sanyi saboda yadda jikinsa ya yi wani sanyi kalau.
Hucin zafi ya fitar daga bakin shi kafin yace"Hasiya ba na gayamiki yanayin aikin nawa ba?
Nan ya yi min nisa da wajen aikina ne sannan muna yawan tafiye tafiye ne ni da ubangidana."
So na ke ya kalleni ne ammh ya kasa kallona cikin idanuwana kansa na kallon kasa ne kwata kwata ya ki yarda ya had'a ido da ni.
Ganin haka yasa na kasa bud'e baki na yi mgana saboda ba ni da abun cewa.
Shi kuma nauyin jiki yasa ya kasa tashi ji ya ke yi kamar bai kyauta ba yana ji kamar wannan tsarin na shi ba tsari ba ne mai kyau.
Hakkin Hasiya na kanshi in ya aikata mata ba daidai ba Allah zai tambayeshi.
Bazai iya bude baki ya gayamata cewa auran su ba kamar yadda ta zata ba ne ya kasa yi ma Amma gaddama ne yasa ya karb'i auranta bazai iya gayamata cewa kafin ya gama Hidimar kasarsa nan da wata shidda sakinta zai yi ba.
Da sauri ya mike sai da ya juya mata baya yace"Ki yi hakuri zan rika zuwa ina dubaki Lokaci bayan Lokaci. Kuma ma ba ga shi kin samu abokiyar zama ba?
Bayansa na bi da kallo kafin nace"Hakane."
Jin na amsa shi yasa ya juyo ya na Fadin"Zan tafi. Ki kula da kanki in ban zo gobe ba jibi zan zo in sha Allahu."
Da toh na amsa masa ya fara tafiya ya na fadin"Taho ki kulle kofar.".
Ba musu na mike rike da kudin da ya ijiyemin a saman jikina har zuwa bakin kofa ya na fita ya juyo ya na kallona ni kuma ina rike da kofa kamar zan yi kuka.
Ganin haka yasa ya Rausayar da kai ya na fadin"Babu fa wani abu ki rika addu'a in zaki kwanta sannan ki rika Rufe kofarki kada ki bude ma wanda baki sani ba ok?
Jinjina masa kai na yi shi kuma sai ya zura hannayensa cikin Aljihun sa gabadaya kafin yace"Sai da Safe."
Nima na bi shi a sanyaye da Sai da Safe.
Har ya juya ya fara tafiya ina Tsaye bansan Lokacin da na kira sunan shi ba"ASSADIQ.."
Da Sauri ya juyo ya na kallona cikin mamaki.
Dawowa ya yi kofar dakin ya na fadin"Menene?
Kaina na kasa nace"Na koma wajen su?
Cikin mamaki yace"Wajen su wa?
Da hannu na nuna masa dakin da ke gefena da mu ke jin hayaniya.
Bi na ya yi da kallo cikin nazarina kafin yace"A'a ki zauna a dakin ki kin ji ko?
Saboda ya na tsoron kada naje su gane yanayi na su tambayane ni nw fad'amusu mijina baya kwana a gidan tunda muka tare.
Duk da rai na bai so ba ammh sai na Hakura tunda yace a'a bai tafi ba sai da yasakani na koma ciki na Rufe kofa sannan ya fita daga gidan ya na sauke numfashi.
Karfi da yaji halayensa na so su gurbace Sanadin haduwarsa da Hasiya ya fara karya da kumbibiya ya fara kokarin zama munafukin Namiji.
Ni ko ina kulle kofata ciki na shige na Dauro alwala na yi sallar isha'i sama sama nayi addu'a sannan na fito falo na duba ledar da yazo da shi tsireni mai uban yawa da yaji kuli da albasa da kokumba sai kyalli ya ke yi ga shi da zafi inaga da zai taho ya tsaya a siya.
Sai kuma Lemun fanta da maltina masu sanyi suma.
Miyau na har ya na tsinkewa ko samun daman Dauko Filet ban yi ba na zauna na fara ci sai da naji cikina ba waje daman ban yi girki da rana ba Taliya dawake na dafa da Dadddren jiya ita na Dumama da Safe da ta ragu ne na ci da Rana.
Na rage kusan rabi na kulle shi a ledan na kai kitchen na boye ban sha ruwa ba Maltina nan na shanye duka na yi gyatsa na koma na jingina da kujera ina maida numfsshi.
A bun ka ga wanda ya ci ya koshi sai naji na fara jin barci sama sama sai na tashi na haye saman kujera na kwanta ba jimawa sai barci.
Bansan na jima ina barci ba sai da naji bugun kofata kamar a sama na tashi a firgice kuma a tsorace.
Tashi na yi naje na bud'e sai naga Hajiya zainab matar nan masu danki.
Ashe sallama za su min sun gama zasu tafi sannan ta dawo min da jug dina da Kofina.
Na karb'a cikin murya barci muka yi sallama da juna har ta na cewa a gaida megidan rashin sani bata san ni kad'ai ce acikin dakin ba.
Maida kofata na yi na kulle saboda barcin da ke idona nan falo na ijiye jug din na shige ciki na kwanta ko kayan Jikina ban cire ba.
Washegari ma ban tashi da wuri ba, barci na sha sosai sai wajen goma na tashi, ban dafa komai ba Sauran tsiren nan na du'mama a tukunya na ci na sha Lemu fanta duk da ina da Ulcer ma naji ina Sha'awan lemum shiyasa na sha.
Da rana kuma Macaroni na Dafa jalop guda daya, naci ni kadai a gida sai da yammah wasu matan suka kara zuwa sun kawo wani kaya ba su jima ba dai suka tafi.
Kuma har dakina suka shigo muka gaisa na ba su ruwa suna ta min godiyan Dawainiya.
Wata mata acikin su ta kalleni ta na Fad'in"Ai ba ma zata wuce sa'an Ummi ba."
Ta gefenta tace"Nima haka nace acikin raina."
Su naji suna hiran su na ko a baya an daga bikin ne suna ta fad'in ba ga shi har Lokaci ya yi ba satin nan ne bikin da Daurin aure.
Acikin raina murna na ke yi kamar wacce za'a kawo wata yar'uwata.
Ko bakomai zaman kadaici bazai kasheni ni kad'ai ba.
Assadiq yace gobe ko jibi zai dawo ammh Shuru bai dawo ba ni ko har ina ta tsammanin shi.
Na fara tunanin meyasa bazai kwana anan ba? Hujjar da ya ba ni ba hujja bace mai karfi tunda muna gari daya ne ba wani gari ba ne zuwa wani gari ba.
Indai ko hakane ya na da dalilinsa na yin haka, kila ko ya na gujema hakanan ne saboda Canfin da ke kaina.
In dai ko zai cigaba da tsira da lafiyarsa gwara nesa nesa da kusa kusan nan da baya haifar da d'a mai ido.
Tunanin haka yasa na cire abun a raina na rika zirga zirgata.
ina kewar yan'uwa mussaman ma Amma ina so na kirata mu yi mgana na roketa ta yafemin domin na tabbata gatan da ta yi min ban da ita ba wanda zai iya yi min wannan gatan.
*****