Sashe 4
Tmw Part 2 Complete Hausa Novel · about 11 min read
K'in zama Tahir ya yi sai da Sadiq da kansa ya saka hannu ya ja shi da karfi ya zaunar da shi.
Shima ya zauna a gabansa ya tankwashe kafa suna Kallon junansu.
Sadiq ya kalli Tahir ya na warware hannunsa lokaci d'aya ya na fad'in"me ka ke son sani yanzu? Me kuma ka ke bukatar a yi?
Tahir ya shaki iskan Takaici kafin yace"Abunda na so ayi lokaci ya riga ya kuremin. Abunda na ke bukata kuma na riga na sanar da kai tun farko"
Ya fad'a cikin cin mgani, Sadiq ya murmusa Allah kad'ai yasan Halin da zuciyarsa ta ke ciki ammh bai rasa kwarin gwiwa ba niyarsa ta Alheri bata bar shi ya ji ya yi Nadama ba.
Cikin sanyin murya yace"Me ka ke bukata Tahir?
Wata uwar Harara Tahir ya sakar masa kafin yace"Bansani ba. Ka fi kowa sanin abunda na ke bukata. Ka sake yarinyar nan domin kasancewata abokinka kamar yan'uwa muka dauki juna. Bazan jure ina ji ina gani ka jefa rayuwarka cikin Halaka ba."
Sadiq ya yi saurin cewa"Ba Halaka ba ne Tahir taimako na yi."
Cikin kufuluwa Tahir yace"Wai ka na ta cewa taimako, hala dole kai Allah ya wajabta ka taimaka musu? Meyasa sai kai? Mazaje nawa ne a gari ba'a neme su ba sai kai?
Sadiq sai ya kasa mgana ganin haka yasa Tahir ya cigaba da zazzaga masifa da kuma alwashin ko Sadiq ya saki Hasiya ko ya kira Umma ya Shaida mata komai tundaga fari.
Sadiq ya yi shuru bai yi mgana ba illah agogon hannunsa da ya kallah kafin yace"Mu yi sallah sai mu cigaba da mganar"
Ya yunkura zai mike cikin zafin Nama Tahir ya maida shi zaune lokaci d'aya ya na fadin"Ba inda zaka je sai mun gama mgana Mallam"
Sadiq ya kallesa cikin mamaki kafin yace"Tahir sallah na gaba da mganarmu."
Shuru Tahir ya yi jin ya fisa gaskiya ganin haka yasa Sadiq ya mike ya na fad'in"Mu yi sallah yau ina da Lokacin ka kaji."
Ya fad'a ya na yar dariya, Dariya ya girgiza kai bai kara mgana ba.
Sun riga sun makara shiyasa a gida suka yi sallar su abinci ma ba wanda ya nema hatta ko Tahir da baya wasa da abinci, suna idar da salla ko Addu'a Tahir bai bari Sadiq ya yi ba yace su cigaba da maganar da suka fara.
Sadiq ya koma ya gyara zama yasan ai yau sai Allah tunda ya shiga Hannun Tahir ya bani wai barawo a hannun mata.
Cikin Sarewa yace"Fad'i abunda ka ke so ayi Tahir."
Tahir yace"Meyasa ka ke so ka nuna kamar bakaji me na fad'a tun farko ba ne? Sakin ta na ce ka yi ko?
Sadiq ya yi shuru ya na kallon Adon Darduman gabanshi kafin ya dago ya na kallon Tahir cikin muryan Kaushi ya ce"A'a Tahir nace maka zan saketa ammh ba yanzu ba."
Tahir yace"Me ye hujjar ka?
Sadiq yace"Ba na sanar da kai ba, na tausayama rayuwarsu ba su da kowa sai Allah ka na fa gani kuma kaji me dan'uwan mahaifinta ya ke gayamin su kansu sun gujesu in na saketa a wannan Lokacin zan kara fasa gurbin bakinciki a rayuwarsu"
Tahir ya yi saurin taran shi da cewa"Dangin mahaifinsu sun gujesu kai kuma waye na su da zaka Rumgume su Sadiq?
Sadiq ya sauke numfashi kafin yace"Tahir kuka fa matar nan ta rika yi mini. Bazan iya juran ganin Uwa ta na kuka saboda matsalan da zan iya mata mganinta ba, Ita bukatar ta Rayuwar Hasiya ta inganta shiyasa na amince da bukatar ta ammh ni kaina ina da nawa tsarin akan haka."
Tahir ya kura masa ido bai basa damar mgana ba ya cigaba da fad'in"Ba son raina ba ne na yi wani abu batare da sanin iyayena ba Tahir. Da farko na so na sanar da su sai na fasa sanin ba wanda zai goyamin baya shiyasa na yanke wannan hukuncin."
Tahir yace"Naji ka yanke hukunci mafitar da zata bulle da kai fa batare da auran nan ya je kunnen su Umma ba?
Sadiq yace"Kai zaka ba ni wannan Mafitan Tahir"
Tahir ya ware ido kafin yace"Ni kuma? Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Eh Tahir saboda kai kad'ai ne na kusa danin da yasan da Labarin auran nan mafitan bangaranka shine ka yi Shuru da bakin ka har Abada ka da wani yasan da wannan mganar.".
Tahir ya yi shuru bai ce komai ba ganin haka yasa Sadiq ya dafa kafad'ansa ya na fad'in"Don Allah Tahir in ka yi min wannan taimakon ka gama sama min dukkan mafitan da na ke hange."
Tahir ya sauke Numfashi kafin yace"Kasan dai abunda zaka sani na aikata ko?
Sadiq yace"Na sani mana, niyyata zaka duba kai ma sai ka dubi ta ka niyar na taimakon abokin ka."
Tahir yace"Naji kai kuma mafitan bangaran ka fa?
Sadiq ya gyara zama ya na Fad'in"Mafitan bangarena shi ne har lokacin da zai cika na saketa ba wanda zai sani nan da zuwa wata shidda lokacin mun gama Hidimar kasarmu nan zariya ne dagani har kai ba Tushen mu ba ne tafiya zamu yi mu koma Mahaifarmu."
Tahir ya kura masa ido ya na neman karin bayani Ganin haka yasa Sadiq ya cigaba da fad'in"Sai dai kafin nan nayi alkwarin inganta rayuwarta da ilimi tare da jari mai karfin da ko bayan na saketa abun bazai dameta ba sosai."
Shuru suka yi dukkansu kamar masu nazari kafin Tahir yace"Har yanzu baka samar ma kanka wata mafitar ba" Sadiq cikin mamaki ya kallesa kafin yace"Kamar wacce mafita kenan?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Ka manta kace ta zauna gidan yar'uwata kafin ka sama mata Muhalli? mafitan in da zaka ijiyeta batare da kowa ya sani ba na ke mgana."
Sai gabad'ayansu suka kalli juna cikin nazari na wani Lokaci kafin Sadiq yace"Zamu samo wannan mafitar daga baya."
Tahir ya ciji lebensa kafin yace"Na kasa aminta da wannan al'amarin Sadiq. Kai ne ka auri bazawara wace auranta biyu fa ka sani."
Sadiq cikin Halin ko in kula yace"Kada ka fara duba wannan Tahir, Annabin mu da bazawara ya fara ya auri Nana Khadija ya na Saurayi dan Shekara ashirin da Biyar a duniya ita kuma ta na da Shekarun arba'in a lokacin. Ka ga da ba'a auran bazawara da Allah bai umarci Annabin Rahma salallahu alaihi wasallam da ya auri Nana Khadija ba.'
Tahir ya tare shi da fad'in"Yanzu sunna na wa kaga mutane na takewa Sadiq?
Sadiq yace"Wannan na su tsarin ne ina so na gayamaka auran bazawara ba Haramun ba ne, Kuma ka sani Annabi shine Jagoranmu abunda ya zo mana da shi ko ya aikata ko Sahabansa suka aikata shine abun koyin mu."
Tahir sai ya kasa mgana ya koma ya na kallon Sadiq kafin yace"Ko ka fara son yarinyar nan ne Sadiq?
A kaikace Sadiq yace"Wata yarinyar?
Tahir na gatsine yace"Zabiyar ka ko nace yar bazawarar amaryan ka."
Sadiq ya jinjina kai ya na mirmishi kafin yace"Sunanta Hasiya Tahir."
Tahir ya dage gira ya na fad'in"Ni kuma ban san sunanta ba."
Sadiq ya kallesa batare da ya yi mgana ba Tahir yace"in ka fara sonta ne ka fad'amin domin naga akan lamarinta kafi kowa zakewa ne"
Sadiq ya yace"In na fara son nata zan gayamaka Tahir ammh yanzu na gayamaka ba mganar so a tsakanina da wannan yarinyar ka gane?
Tahir yace"Zan gane nan da wata shidda in sha Allahu."
Sadiq ya bi Tahir da kallo mai ya Daukesa ya na Tunanin zai karya alkwari ne?zai ko ba shi mamaki in sha Allahu.
Sun yi shuru kenan wayar Sadiq da ke gefen Tahir saman gado ta hau Ruru da sauri ya dauko masa ya duba mai kira cikin zaro ido yace"Umma. umma ce ke kiran ka."
Sadiq cikin natsuwa ya mika hannu ya karbi wayar ya na fadin"To sai me in Umma na kira? Daman ta saba kirana."
Daga haka ya daga kiran lokaci d'aya da sallama bayan ya saka wayar a amsa kuwwa yadda Tahir zai ji.
Dagachan bangaran Umma ta amsa sallamarsa cikin fara'a kafin tace"Auta ka na lafiya ko? Jiya ba mu yi mgana ba yau ma haka."
Sadiq na shafa kanshi yace"Na yi uzurori ne jiya da yau Umma kuna lafiya?
Umma tace"Lafiya lau ya aiki? Ina Attahiru?
Sadiq na kallon Tahir da ya kafesa da ido yace"Ya na nan lafiya Umma ina Abba.?
Umma na mgana yaji Muryan Innani ta na fad'a sai cewa ta ke yi"Kaji min kisisina wajen salamatu ni fa na Dauko kafata nazo nace ta kiramin Magajin gida mu gaisa ammh ta tsaya ta na wani uban labari da shi, don Allah ni dai kin ga ba ni shi mu yi mgana."
Ta fad'a ta na kokarin warce wayar Hannun Umma daidai Lokacin da Umma ke fad'in"Auta ga Innani."
Kai ya dafe sanda Innani ta amshi wayar ta na fad'in"Ina kwana Magajin gida? Shikenan ka manta da ni ko mema na baka yi ba?
Cikin mirmishi yace"A ina zan neme ki? Kina da waya ne?
Innani tace"Wani bakin Munafukin ne yace ba ni da waya? Kaji mutane da son had'a fad'a in sulaimanu yaji ai ransa bazai yi masa dadi ba yaga ya siyamin waya ammh ana chan ana yamad'id'i da ni ba ni da waya"
Sadiq na kunshe Dariyarsa yace"To ai ke kikace an Dauke miki waya ki ka yi ta tsine tsine."
Innani ta Rafka dogon Salati kafin tace"Ni kuma? Yaushe na ce an sace min waya? Oh ni duniya da tsufana ammh har yanzu ba'a daina bi da kulli ba to ta Allah ba ta mutum ba, Ni dije dashen Allah ne na gagara wlh."
Sadiq ya kwashe da dariya kafin yace"Kedai ki ka sani. Sai ki fad'i mgana ki ce baki fad'a ba."
Innani ta sassauta murya ta na fadin"Allah dai ya rabamu da yan Uba kaji Magajin gida.'
Cikin Annushuwa ya amsa da Ameen zencen Innani ta cigaba da yi masa da ta tambayi Tahir yace ga shi a gabansa.
Ya mika ma Tahir suka cigaba da shan Hira suna shan Dariyan Innani da wayar ta dawo hannun Sadiq ne Innani tace"ka ganni yanzu wajen mamanka na ke yi ni Shashena ba kowa sulsana ta fara zuwa boko ba mai d'ebemin kewa."
Sadiq yace"Ki zauna da Umman sai ku rika yin hira."
Innnani ta tabe baki kamar ya na ganinta batace komai ba daga gani akwai mgana a bakinta.
Sanin haka yasa Sadiq yace"Yaushe ki ka dawo? Na dauka chan zaki mutu sai dai muje jana'iza."
Innani ta saki baki kafin tace"Kaji wani mugun baki kuma? Ni da mutuwa ai sai na aurar da ya'yan ku kai da Sulsana."
Sadiq ya kyakyace da dariya kafin yace"Kina da son duniya Innani ina Laifin ki ga auran namu na ya'yan mu kuma kina kabari za'ayi."
Innani ta yi gum Magajin gida ne ba Halin ta yi masa masifa.
Jin yadda ta yi shuru yasa yasan gabda ta ke da fashewa da kuka, yasa cikin barkwanci yace"Ya kika baro su Mallam zakarin?
Jin haka yasa Innani ta gyara zama ta na bashi labaran abunda ya faru achan ta karishe da fad'in"Kai dai bari magajin gida kamar kar in dawo. Ammh ya na iya sulaimanu da matansa sai kira suke wai yaushe zan dawo? Saboda ma a nuna min iyakata aikamin akayi da mota akace in ni bazan dawo ba na turo su sulsana zasu fara zuwa makaranta abunan ya yi min ciwo matuka ni fa saboda Salamatu naje kamar ya' na Dauketa ita kuma kaga a uwa ta Daukeni ko ba Haka ba.?
Sadiq yace"Hakane Innani kin Sada zumunci Allah ya baki lada"
Innani ta washe baki ta na fad'in"Ameen Magajin gida, ai da na dawo sun sha masifa nace ina Dalili kun dameni na dawo sai kace Nono zan ba ma shi Sulaimanu din mutum ya girma da iyalansa ammh baza'a bar ran Tsohu ya huta ba, chan wlh ana kula da ni naci na sha mai kyau mu yi ni muna Hira da Zakari gwanin ban sha'awa nan ko sai zama a katon gida kamar mayya Sulsanar da ke tayani zama an yi min nunafunci itama Sulaimanu yace Boko zata yi ai shikenan maji dai ma gani wai an Tura uwar amarya biko."
Sadiq duk halin da ya ke ciki sai da ya Biye ma Innani ya na ta cin dariya daga karshe suka fara Diraman sai ta zo zariya daman bata taba zuwa ba Dakyar ya lallasheta akan zai zo ya tafi da ita sannan ta Hakura.
Sun fi awa biyu suna Hira sai da kudin wayar Umma suka kare shi kuma yaki kira daman ya gaji Innani ce fa Lamarinta sai Allah.
Suna gama wayar alwala suka yi zuwa masallaci ba su dawo ba sai da suka yi isha'i.
Bayan sun dawo ba su nemi abinci ba Ruwan zafi Tahir ya dafa musu suka sha Tea saboda ya warware musu ciki.
Sadiq dai ya shiga uku da Tahir sai ya yi kamar yana goyon bayansa sai kuma ya Turje har ya gaji da basa mgana ya kyalesa duk da ya na da kyakyawan yakinin Tahir bazai iya Tona masa wannan Sirrin ba.
Washegari kuma da wuri kowannen su ya isa inda ya ke Hidimar kasarsa Sai dai ba Sadiq kad'ai ba hatta Tahir kowa ya fahimci wani abu na Damunsa ya rage kazar kazar.
Shi ko Sadiq duk da daman ba shi da Hayaniya sosai shima an Fahimci ya na cikin Damuwa.
Abokansa na wajen ne da sukaje masa Daurin aure suka so su fasa mgana ya rokesu da Allah kada wani yaji Labarin ya yi aure ba su nemi sanin ba'asi ba sukace in sha Allahu sun bar mganar a tsakaninsu.
Ya dauka al'amarin wasa ne sai da ya Faru sannan yasan abun ya wuce Tunaninsa.
Shima ya zauna a gabansa ya tankwashe kafa suna Kallon junansu.
Sadiq ya kalli Tahir ya na warware hannunsa lokaci d'aya ya na fad'in"me ka ke son sani yanzu? Me kuma ka ke bukatar a yi?
Tahir ya shaki iskan Takaici kafin yace"Abunda na so ayi lokaci ya riga ya kuremin. Abunda na ke bukata kuma na riga na sanar da kai tun farko"
Ya fad'a cikin cin mgani, Sadiq ya murmusa Allah kad'ai yasan Halin da zuciyarsa ta ke ciki ammh bai rasa kwarin gwiwa ba niyarsa ta Alheri bata bar shi ya ji ya yi Nadama ba.
Cikin sanyin murya yace"Me ka ke bukata Tahir?
Wata uwar Harara Tahir ya sakar masa kafin yace"Bansani ba. Ka fi kowa sanin abunda na ke bukata. Ka sake yarinyar nan domin kasancewata abokinka kamar yan'uwa muka dauki juna. Bazan jure ina ji ina gani ka jefa rayuwarka cikin Halaka ba."
Sadiq ya yi saurin cewa"Ba Halaka ba ne Tahir taimako na yi."
Cikin kufuluwa Tahir yace"Wai ka na ta cewa taimako, hala dole kai Allah ya wajabta ka taimaka musu? Meyasa sai kai? Mazaje nawa ne a gari ba'a neme su ba sai kai?
Sadiq sai ya kasa mgana ganin haka yasa Tahir ya cigaba da zazzaga masifa da kuma alwashin ko Sadiq ya saki Hasiya ko ya kira Umma ya Shaida mata komai tundaga fari.
Sadiq ya yi shuru bai yi mgana ba illah agogon hannunsa da ya kallah kafin yace"Mu yi sallah sai mu cigaba da mganar"
Ya yunkura zai mike cikin zafin Nama Tahir ya maida shi zaune lokaci d'aya ya na fadin"Ba inda zaka je sai mun gama mgana Mallam"
Sadiq ya kallesa cikin mamaki kafin yace"Tahir sallah na gaba da mganarmu."
Shuru Tahir ya yi jin ya fisa gaskiya ganin haka yasa Sadiq ya mike ya na fad'in"Mu yi sallah yau ina da Lokacin ka kaji."
Ya fad'a ya na yar dariya, Dariya ya girgiza kai bai kara mgana ba.
Sun riga sun makara shiyasa a gida suka yi sallar su abinci ma ba wanda ya nema hatta ko Tahir da baya wasa da abinci, suna idar da salla ko Addu'a Tahir bai bari Sadiq ya yi ba yace su cigaba da maganar da suka fara.
Sadiq ya koma ya gyara zama yasan ai yau sai Allah tunda ya shiga Hannun Tahir ya bani wai barawo a hannun mata.
Cikin Sarewa yace"Fad'i abunda ka ke so ayi Tahir."
Tahir yace"Meyasa ka ke so ka nuna kamar bakaji me na fad'a tun farko ba ne? Sakin ta na ce ka yi ko?
Sadiq ya yi shuru ya na kallon Adon Darduman gabanshi kafin ya dago ya na kallon Tahir cikin muryan Kaushi ya ce"A'a Tahir nace maka zan saketa ammh ba yanzu ba."
Tahir yace"Me ye hujjar ka?
Sadiq yace"Ba na sanar da kai ba, na tausayama rayuwarsu ba su da kowa sai Allah ka na fa gani kuma kaji me dan'uwan mahaifinta ya ke gayamin su kansu sun gujesu in na saketa a wannan Lokacin zan kara fasa gurbin bakinciki a rayuwarsu"
Tahir ya yi saurin taran shi da cewa"Dangin mahaifinsu sun gujesu kai kuma waye na su da zaka Rumgume su Sadiq?
Sadiq ya sauke numfashi kafin yace"Tahir kuka fa matar nan ta rika yi mini. Bazan iya juran ganin Uwa ta na kuka saboda matsalan da zan iya mata mganinta ba, Ita bukatar ta Rayuwar Hasiya ta inganta shiyasa na amince da bukatar ta ammh ni kaina ina da nawa tsarin akan haka."
Tahir ya kura masa ido bai basa damar mgana ba ya cigaba da fad'in"Ba son raina ba ne na yi wani abu batare da sanin iyayena ba Tahir. Da farko na so na sanar da su sai na fasa sanin ba wanda zai goyamin baya shiyasa na yanke wannan hukuncin."
Tahir yace"Naji ka yanke hukunci mafitar da zata bulle da kai fa batare da auran nan ya je kunnen su Umma ba?
Sadiq yace"Kai zaka ba ni wannan Mafitan Tahir"
Tahir ya ware ido kafin yace"Ni kuma? Sadiq ya jinjina kai kafin yace"Eh Tahir saboda kai kad'ai ne na kusa danin da yasan da Labarin auran nan mafitan bangaranka shine ka yi Shuru da bakin ka har Abada ka da wani yasan da wannan mganar.".
Tahir ya yi shuru bai ce komai ba ganin haka yasa Sadiq ya dafa kafad'ansa ya na fad'in"Don Allah Tahir in ka yi min wannan taimakon ka gama sama min dukkan mafitan da na ke hange."
Tahir ya sauke Numfashi kafin yace"Kasan dai abunda zaka sani na aikata ko?
Sadiq yace"Na sani mana, niyyata zaka duba kai ma sai ka dubi ta ka niyar na taimakon abokin ka."
Tahir yace"Naji kai kuma mafitan bangaran ka fa?
Sadiq ya gyara zama ya na Fad'in"Mafitan bangarena shi ne har lokacin da zai cika na saketa ba wanda zai sani nan da zuwa wata shidda lokacin mun gama Hidimar kasarmu nan zariya ne dagani har kai ba Tushen mu ba ne tafiya zamu yi mu koma Mahaifarmu."
Tahir ya kura masa ido ya na neman karin bayani Ganin haka yasa Sadiq ya cigaba da fad'in"Sai dai kafin nan nayi alkwarin inganta rayuwarta da ilimi tare da jari mai karfin da ko bayan na saketa abun bazai dameta ba sosai."
Shuru suka yi dukkansu kamar masu nazari kafin Tahir yace"Har yanzu baka samar ma kanka wata mafitar ba" Sadiq cikin mamaki ya kallesa kafin yace"Kamar wacce mafita kenan?
Tahir ya gyara zama ya na fad'in"Ka manta kace ta zauna gidan yar'uwata kafin ka sama mata Muhalli? mafitan in da zaka ijiyeta batare da kowa ya sani ba na ke mgana."
Sai gabad'ayansu suka kalli juna cikin nazari na wani Lokaci kafin Sadiq yace"Zamu samo wannan mafitar daga baya."
Tahir ya ciji lebensa kafin yace"Na kasa aminta da wannan al'amarin Sadiq. Kai ne ka auri bazawara wace auranta biyu fa ka sani."
Sadiq cikin Halin ko in kula yace"Kada ka fara duba wannan Tahir, Annabin mu da bazawara ya fara ya auri Nana Khadija ya na Saurayi dan Shekara ashirin da Biyar a duniya ita kuma ta na da Shekarun arba'in a lokacin. Ka ga da ba'a auran bazawara da Allah bai umarci Annabin Rahma salallahu alaihi wasallam da ya auri Nana Khadija ba.'
Tahir ya tare shi da fad'in"Yanzu sunna na wa kaga mutane na takewa Sadiq?
Sadiq yace"Wannan na su tsarin ne ina so na gayamaka auran bazawara ba Haramun ba ne, Kuma ka sani Annabi shine Jagoranmu abunda ya zo mana da shi ko ya aikata ko Sahabansa suka aikata shine abun koyin mu."
Tahir sai ya kasa mgana ya koma ya na kallon Sadiq kafin yace"Ko ka fara son yarinyar nan ne Sadiq?
A kaikace Sadiq yace"Wata yarinyar?
Tahir na gatsine yace"Zabiyar ka ko nace yar bazawarar amaryan ka."
Sadiq ya jinjina kai ya na mirmishi kafin yace"Sunanta Hasiya Tahir."
Tahir ya dage gira ya na fad'in"Ni kuma ban san sunanta ba."
Sadiq ya kallesa batare da ya yi mgana ba Tahir yace"in ka fara sonta ne ka fad'amin domin naga akan lamarinta kafi kowa zakewa ne"
Sadiq ya yace"In na fara son nata zan gayamaka Tahir ammh yanzu na gayamaka ba mganar so a tsakanina da wannan yarinyar ka gane?
Tahir yace"Zan gane nan da wata shidda in sha Allahu."
Sadiq ya bi Tahir da kallo mai ya Daukesa ya na Tunanin zai karya alkwari ne?zai ko ba shi mamaki in sha Allahu.
Sun yi shuru kenan wayar Sadiq da ke gefen Tahir saman gado ta hau Ruru da sauri ya dauko masa ya duba mai kira cikin zaro ido yace"Umma. umma ce ke kiran ka."
Sadiq cikin natsuwa ya mika hannu ya karbi wayar ya na fadin"To sai me in Umma na kira? Daman ta saba kirana."
Daga haka ya daga kiran lokaci d'aya da sallama bayan ya saka wayar a amsa kuwwa yadda Tahir zai ji.
Dagachan bangaran Umma ta amsa sallamarsa cikin fara'a kafin tace"Auta ka na lafiya ko? Jiya ba mu yi mgana ba yau ma haka."
Sadiq na shafa kanshi yace"Na yi uzurori ne jiya da yau Umma kuna lafiya?
Umma tace"Lafiya lau ya aiki? Ina Attahiru?
Sadiq na kallon Tahir da ya kafesa da ido yace"Ya na nan lafiya Umma ina Abba.?
Umma na mgana yaji Muryan Innani ta na fad'a sai cewa ta ke yi"Kaji min kisisina wajen salamatu ni fa na Dauko kafata nazo nace ta kiramin Magajin gida mu gaisa ammh ta tsaya ta na wani uban labari da shi, don Allah ni dai kin ga ba ni shi mu yi mgana."
Ta fad'a ta na kokarin warce wayar Hannun Umma daidai Lokacin da Umma ke fad'in"Auta ga Innani."
Kai ya dafe sanda Innani ta amshi wayar ta na fad'in"Ina kwana Magajin gida? Shikenan ka manta da ni ko mema na baka yi ba?
Cikin mirmishi yace"A ina zan neme ki? Kina da waya ne?
Innani tace"Wani bakin Munafukin ne yace ba ni da waya? Kaji mutane da son had'a fad'a in sulaimanu yaji ai ransa bazai yi masa dadi ba yaga ya siyamin waya ammh ana chan ana yamad'id'i da ni ba ni da waya"
Sadiq na kunshe Dariyarsa yace"To ai ke kikace an Dauke miki waya ki ka yi ta tsine tsine."
Innani ta Rafka dogon Salati kafin tace"Ni kuma? Yaushe na ce an sace min waya? Oh ni duniya da tsufana ammh har yanzu ba'a daina bi da kulli ba to ta Allah ba ta mutum ba, Ni dije dashen Allah ne na gagara wlh."
Sadiq ya kwashe da dariya kafin yace"Kedai ki ka sani. Sai ki fad'i mgana ki ce baki fad'a ba."
Innani ta sassauta murya ta na fadin"Allah dai ya rabamu da yan Uba kaji Magajin gida.'
Cikin Annushuwa ya amsa da Ameen zencen Innani ta cigaba da yi masa da ta tambayi Tahir yace ga shi a gabansa.
Ya mika ma Tahir suka cigaba da shan Hira suna shan Dariyan Innani da wayar ta dawo hannun Sadiq ne Innani tace"ka ganni yanzu wajen mamanka na ke yi ni Shashena ba kowa sulsana ta fara zuwa boko ba mai d'ebemin kewa."
Sadiq yace"Ki zauna da Umman sai ku rika yin hira."
Innnani ta tabe baki kamar ya na ganinta batace komai ba daga gani akwai mgana a bakinta.
Sanin haka yasa Sadiq yace"Yaushe ki ka dawo? Na dauka chan zaki mutu sai dai muje jana'iza."
Innani ta saki baki kafin tace"Kaji wani mugun baki kuma? Ni da mutuwa ai sai na aurar da ya'yan ku kai da Sulsana."
Sadiq ya kyakyace da dariya kafin yace"Kina da son duniya Innani ina Laifin ki ga auran namu na ya'yan mu kuma kina kabari za'ayi."
Innani ta yi gum Magajin gida ne ba Halin ta yi masa masifa.
Jin yadda ta yi shuru yasa yasan gabda ta ke da fashewa da kuka, yasa cikin barkwanci yace"Ya kika baro su Mallam zakarin?
Jin haka yasa Innani ta gyara zama ta na bashi labaran abunda ya faru achan ta karishe da fad'in"Kai dai bari magajin gida kamar kar in dawo. Ammh ya na iya sulaimanu da matansa sai kira suke wai yaushe zan dawo? Saboda ma a nuna min iyakata aikamin akayi da mota akace in ni bazan dawo ba na turo su sulsana zasu fara zuwa makaranta abunan ya yi min ciwo matuka ni fa saboda Salamatu naje kamar ya' na Dauketa ita kuma kaga a uwa ta Daukeni ko ba Haka ba.?
Sadiq yace"Hakane Innani kin Sada zumunci Allah ya baki lada"
Innani ta washe baki ta na fad'in"Ameen Magajin gida, ai da na dawo sun sha masifa nace ina Dalili kun dameni na dawo sai kace Nono zan ba ma shi Sulaimanu din mutum ya girma da iyalansa ammh baza'a bar ran Tsohu ya huta ba, chan wlh ana kula da ni naci na sha mai kyau mu yi ni muna Hira da Zakari gwanin ban sha'awa nan ko sai zama a katon gida kamar mayya Sulsanar da ke tayani zama an yi min nunafunci itama Sulaimanu yace Boko zata yi ai shikenan maji dai ma gani wai an Tura uwar amarya biko."
Sadiq duk halin da ya ke ciki sai da ya Biye ma Innani ya na ta cin dariya daga karshe suka fara Diraman sai ta zo zariya daman bata taba zuwa ba Dakyar ya lallasheta akan zai zo ya tafi da ita sannan ta Hakura.
Sun fi awa biyu suna Hira sai da kudin wayar Umma suka kare shi kuma yaki kira daman ya gaji Innani ce fa Lamarinta sai Allah.
Suna gama wayar alwala suka yi zuwa masallaci ba su dawo ba sai da suka yi isha'i.
Bayan sun dawo ba su nemi abinci ba Ruwan zafi Tahir ya dafa musu suka sha Tea saboda ya warware musu ciki.
Sadiq dai ya shiga uku da Tahir sai ya yi kamar yana goyon bayansa sai kuma ya Turje har ya gaji da basa mgana ya kyalesa duk da ya na da kyakyawan yakinin Tahir bazai iya Tona masa wannan Sirrin ba.
Washegari kuma da wuri kowannen su ya isa inda ya ke Hidimar kasarsa Sai dai ba Sadiq kad'ai ba hatta Tahir kowa ya fahimci wani abu na Damunsa ya rage kazar kazar.
Shi ko Sadiq duk da daman ba shi da Hayaniya sosai shima an Fahimci ya na cikin Damuwa.
Abokansa na wajen ne da sukaje masa Daurin aure suka so su fasa mgana ya rokesu da Allah kada wani yaji Labarin ya yi aure ba su nemi sanin ba'asi ba sukace in sha Allahu sun bar mganar a tsakaninsu.
Ya dauka al'amarin wasa ne sai da ya Faru sannan yasan abun ya wuce Tunaninsa.