Sashe 48
Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haneef a wajen ya tsaya kamar gunki ransa ya baci,idonsa ya canja kala,Nan take zazzabi ya fara lullube shi yaji wani jiri Yana daukansa yuuu yuuuu....mota ya koma ya shiga ya kwanta a bayan mota tare da rike kansa yace da driver juya mu koma gida kaini asibiti kawai,Driver ya fyalle mota da gudu sai birni suka wuce asibiti.
Mero kuwa tun a hanya ta fara kuka tayi sauri ta fada gidan su tana zuwa ta shiga da kuka,Jummai ta gama tace awararta ta saka a faranti zata fara yankawa Mero ta shugo tabi ta kan awarar da takalmi ta taketa tace wlh yau baza ayi ciniki ba,kowa bazai zo siyen awara ba ta wuce cikin daki ta zuge jakar kayanta ta zazzage su a kasa ta fada Saman katifarta ta hau rusa kuka tana wayyoooo Haneef Ina sonkaaaaa......Allah ka Gani Ina sonsa,sai shiga Raina yake kullum.....Jummai ta fita unguwa ta dawo ta samu Mero tana kuka ga awararta kaca kaca a faranti,tace Khadija kece kika min barna haka ko kuwa wani mugun ne daga shiga makwafta in dawo shine kika yi min haka,sabo da baki da mutunci,wallahi wallahi ko ki yarda ko karki yarda Haneef Yana zuwa zansa ya Kai kudin aurenki wajen iyayenki Maza tunda Yana sonki,Khadija tace ni Abdul zan aura nace ma ya turo gobe ko jibi.
Wanne Abdul din? Abdul na gidan Magaji wanzami?Mero tace ae shi,Jummai tace idan kin aure shi Allah ya tsine min Khadija,wlh gwara na mutu,wannan Dan shaye shayen? ga talauci da me zai ci dake da wacce sana'ar? Bashi da sana'a fa,wannan kazamin ma in banda doyi me Abdul zaiyi,ki aure shi ai Kya Sha doyi kuwa,ga me kamshi Haneef wannan kamshin kadai in kina shaka a turaka Rahma ce da Ni'ima,wlh ko ni da zan iya Maida kaina budurwa da na mayar na kwace Haneef din ni ya aure ni,Mero tace a gidan nan wacce kazantar ce ba a ayi, kazanta iri iri badan yanzu ba da nake gyarawa nidai bazan auri Wanda ya lalatani ya cuce ni ba,to zanga wacce zata yarda ki aure Abdulfata din.
Abdul fata kuwa tunda Mero tace ya turo bashi da ko sisi na sigari ma ya gagare shi,ya rasa Inda zai sa kansa,akuyar Tinkiya guda biyu na babansa ya sace cikin dare ya kaisu gidan abokinsa ya ajiye washe gari zasu kai su kasuwa.
Haneef ana wucewa da shi asibiti ya kasa tashi ya fito da kafafunsa sai driver da wasu daga cikin asibitin ma'aikata aka fito da shi tare da Kai shi ciki,Driver Mama ya kira tana zaune tunda Taga kiran driver ta firgita,ta daga yace Mama muna asibiti wlh munje unguwar to ya hadu da yarinyar da yake zuwa wajenta kawai ya ganta da wani saurayin suna zance to sai ta bawa waccen saurayin dama ya Kai kudin aurenta zata aure shi,daga nan ya dawo mota tun a mota yace na kaishi asibiti,wlh muna zuwa ya kasa fitowa da kansa sai shigar shi aka yi,Yana nan ana bashi kulawa,Mama tace wanne asibitin kuke? Global health clinic,Gani Nan cewar Mama,hankalinta a tashe ta nufi asibiti.
Zuwanta ke da wuya ta samu Likita ya fito Yana cewa zaku iya shiga kuga Jikin shock ya samu saura kadan zuciyarsa ta samu matsala amma Allah ya kiyaye,Mama ta shiga tana salati,Haneef ta samu a kwance Yana bacci ta hau kuka a hankali sabo da kar ta tashe shi,Driver ta samu tace Dan Allah kula da shi dole na tafi gidan su Khadija bani address,Driver yace mama ki bari yamma tayi,Mama tace a'a kyale ni yaron nan shi kadai na Haifa duk duniya bani da kamarsa Allah ne gatana shine gatana,Driver ya bata number kuwa ta tafi garin,Bata Isa can ba sai da magriba,da tambaya aka nuna mata gidan su Khadija ta shiga,lokacin Khadija bata nan ta tafi gidan Yan uwan Mahaifinta.
Jummai tana ganin Mama taga suna yanayi da Haneef,hannu bibiyu ta karbeta a dakinta ta kawo mata ruwa da tuwon daren data kwashe,Mama Sallah ta fara gabatarwa sannan tace nasan baki sanni ba,ai nice mahaifiyar Haneef,Jummai tace ai kuwa naga kamanni, nasan kin San mene ne ya faru tsakanin Khadija da Haneef,kaddarar data fada musu,wlh sharrin shedan ne,Dan Allah ku yafe masa,Khadija nazo na bawa hakuri tayi hakuri ta yafe Masa Dan Allah,tace a sanadin wannan abin Haneef yana kwance a asibiti,Mero ce ta shugo gidan ta tsinci Mama tana cewa Haneef yazo ya samu Khadija tace wani ya turo wlh bai koma gida da lafiya ba sai asibiti aka kaishi Yana can bai San Ina yake ba,zuciyarsa ce ta samu shock saura kadan ta samu matsala Allah ya tsare,Dan Allah kuyi hakuri ku yafe Masa,Sallama Khadija tayi kamar bata ji zancen ba amma hankalinta a tashe yake.
Ciki ta shiga tace laaa Mama kece? Mama taji dadin yanda Khadija ta mata tace nice Khadija nazo baki hakuri har gida,Dan Allah ki yafewa Haneef,Khadija ta furta ai na yafe Masa ni tuni,Mama taji dadi tace na gode, Dan Allah ki aure shi Khadija,Mero tace ai ni wani nake so Mama,Dan Allah yayi hakuri,Jummai tace Kinga Maman Haneef na bashi ita rabu da ita,a kawo kudin aure wlh ko a gobe a daura indai kun kawo kudin aure da sadaki a ranar za a daura,Khadija zata yi magana Jummai tace kina magana wlh sai mun raba gari,Shuru Khadija tayi ta tashi ta fice,Mama tace kar ayi mata dole dan Allah,Kyaleta karya take tana sonsa wlh cewar Jummai,suka gama Kus Kus dinsu da Maman Haneef sannan taci tuwon kadan tace ta koshi a daren ta samu me taxi dan garin ya kawota birni drop.
Asibitin ta koma ta samu Haneef a zaune Yana cin Ayaba,farin ciki tayi ta zauna a gefensa tana tambayarsa ya jikin? yace da sauki,Yana cin Ayaba Yana Jan tsaki shi kadai,Mama tace Haneef ka kwantar da hankalinka Inshaallah gobe sai an daura Maka aure da Khadija,Haneef yasan ma bazai yuwu ba,yace hmm kawai Allah ya kaimu,ka shirya gobe da kawunka zasu zo har abokinka Isma'il ka gayyato tunda Kai naga baka fiye abokai ba,Haneef ya kalleta kawai dan bai San taje garin ba ma Kuma bata fada Masa ba.
Washe gari da safe aka sallame su Mama ta damu sai Haneef yayi shiri,cikin sababbin kayansa ya saka wata tsadajiiyar shadda fara kar,bai sa hula ba tace ai dole sai ya saka,haka ya saka ya shirya sosai ya fito a angonsa,jikinsa a sanyaye yasan tatsuniya ce,ita kuwa Mama har ta fara Shirin hada Lefen ma,Su Kawu su biyar suka iso daga Adamawa suka tafi a mota biyu har abokin Haneef Isma'il suka tafi garin su Khadija,Munnir shi ya raka su har gidan dangin Sani ubansu Wanda Jummai taje ta fada Masa Khadija ta samu miji na kirki amma taki yarda,ita ta gaji da girman Khadija a gida,zasu kawo kudin aure da sadaki kawai a daura aure.
Yace ai dama kune kuke kyaleta duk garin Nan babu sa'an Khadija Allah ya kaimu za a daura indai kin gamsu da tarbiyyarsa da Halayensa da gidan da ya taso ba matsala,Jummai tace na gamsu,sun San masifar Jummai sannan sun gaji da ganin Khadija taki aure a kauye ko wacce ana mata aure banda ita,Yan uwa ya fadawa,kowa yaji sai murna za a aurar da Khadija a daina musu gori a gari.
Washe gari tun kafin suga angwaye suka Tara mutane a masallaci ana jira,Munnir yasa Yar wankakkiyar shaddarsa ya rakasu masallacin,Haneef ji yayi kawai ana cewa ga angwaye sunzo,mamaki ya kamashi dan bai zaton hakan ba,su Kawunsa ne akan komai sune suka Bada dubu Dari biyu kudin aure sannan Kuma aka Bada sadaki dubu dari biyu Shima,Dangin Khadija suka ce yayi tsada gaskiya su a rage,Haneef yace baza a rage mata ba ai sunyi ma kadan,Isma'il Yana ta mamakin auren Haneef haka Emergency,Nan take Liman yayi Khuduba mutane suka sheda aka daura auren Khadija Sani da Haneef.
Ana gamawa Haneef yaji hankalinsa ya kwanta nutsuwa ta zo Masa,wani irin farin ciki da nishadi ne suka lullube shi,ji yayi a duniya Kam baida Matsala shi dai,yace Anya kuwa da gaske ne ba mafarki nake ba? Isma'il yace da gaske ne duk mun sheda sai mu tafi gida sai an kawo Amarya,Haneef yace ni a nan zan yini kabi su Kawu ku tafi driver na muna tare, Isma'il ya zaro ido amma Haneef shi ba komai Aboki ke sani nasa ba shi yasa Isma'il bai San komai ba akan Haneef sai kadan.
Su Kawu yabi suka tafi Haneef da driver dinsa suka je gidan Khadija,yaga ana ta shiga Allah Sanya Alkhairi yace ashe dai da gaske ne,yaro ya tura gidan yace a kira Khadija inji Angonta,Khadija tana ta kuka an daura aurenta da Haneef,tana daki ta boye kanta,itama Jummai bata nunawa mutane ita,Yaro ne ya shugo yace Khadija tazo inji Angonta Jummai tace kace gata nan,da kanta ta shiga dakin Khadija tace tashi ko na ci ubanki,Kuma wlh in Baki je ba Khadija sai na tsine miki ki tashi kije tun wuri saura ki Masa fitsara,Khadija ta tashi tana hawaye,wanka ma da kyar tayi,taki yin kwalliya ta zauna daga ita sai vest da skert na atamfa,Hijab Jilbab ta dauka har kasa dogo me hannu ta saka tana goge hawayenta Wanda ya kasa daina zuba.
Yana ganin ta fito ya sallami driver yace zan kira ka,Driver ya Kalli Khadija yace ki shiga bayan mota Yana ciki,maganar mahaifiyarta ta tuna dole ta bude motar cikin fushi ta shiga ta zauna bata Kalli Inda yake ba ta sake fashewa da kuka,Haneef ko a jikinsa shi hankali kwance,yayi murmushi tare da riko hannunta,da sauri tasa hannu ta make Masa hannu ya saki ba shiri,yace kiyi hakuri Khadija,ba laifina bane na miki dole ki aure ni, Dan Allah kiyi hakuri ya kwantar da kansa a kafadarta ta janye jikinta da sauri tana harararsa,Kyaleta yayi yace zan tafi,mota ta bude fuuuuuu ta shige gida abinta,driver ya kira suka wuce,sai bayan ya koma gida Mama ta bashi labarin yanda aka yi har aka daura Masa auren da Khadija.
Mero kuwa tun a hanya ta fara kuka tayi sauri ta fada gidan su tana zuwa ta shiga da kuka,Jummai ta gama tace awararta ta saka a faranti zata fara yankawa Mero ta shugo tabi ta kan awarar da takalmi ta taketa tace wlh yau baza ayi ciniki ba,kowa bazai zo siyen awara ba ta wuce cikin daki ta zuge jakar kayanta ta zazzage su a kasa ta fada Saman katifarta ta hau rusa kuka tana wayyoooo Haneef Ina sonkaaaaa......Allah ka Gani Ina sonsa,sai shiga Raina yake kullum.....Jummai ta fita unguwa ta dawo ta samu Mero tana kuka ga awararta kaca kaca a faranti,tace Khadija kece kika min barna haka ko kuwa wani mugun ne daga shiga makwafta in dawo shine kika yi min haka,sabo da baki da mutunci,wallahi wallahi ko ki yarda ko karki yarda Haneef Yana zuwa zansa ya Kai kudin aurenki wajen iyayenki Maza tunda Yana sonki,Khadija tace ni Abdul zan aura nace ma ya turo gobe ko jibi.
Wanne Abdul din? Abdul na gidan Magaji wanzami?Mero tace ae shi,Jummai tace idan kin aure shi Allah ya tsine min Khadija,wlh gwara na mutu,wannan Dan shaye shayen? ga talauci da me zai ci dake da wacce sana'ar? Bashi da sana'a fa,wannan kazamin ma in banda doyi me Abdul zaiyi,ki aure shi ai Kya Sha doyi kuwa,ga me kamshi Haneef wannan kamshin kadai in kina shaka a turaka Rahma ce da Ni'ima,wlh ko ni da zan iya Maida kaina budurwa da na mayar na kwace Haneef din ni ya aure ni,Mero tace a gidan nan wacce kazantar ce ba a ayi, kazanta iri iri badan yanzu ba da nake gyarawa nidai bazan auri Wanda ya lalatani ya cuce ni ba,to zanga wacce zata yarda ki aure Abdulfata din.
Abdul fata kuwa tunda Mero tace ya turo bashi da ko sisi na sigari ma ya gagare shi,ya rasa Inda zai sa kansa,akuyar Tinkiya guda biyu na babansa ya sace cikin dare ya kaisu gidan abokinsa ya ajiye washe gari zasu kai su kasuwa.
Haneef ana wucewa da shi asibiti ya kasa tashi ya fito da kafafunsa sai driver da wasu daga cikin asibitin ma'aikata aka fito da shi tare da Kai shi ciki,Driver Mama ya kira tana zaune tunda Taga kiran driver ta firgita,ta daga yace Mama muna asibiti wlh munje unguwar to ya hadu da yarinyar da yake zuwa wajenta kawai ya ganta da wani saurayin suna zance to sai ta bawa waccen saurayin dama ya Kai kudin aurenta zata aure shi,daga nan ya dawo mota tun a mota yace na kaishi asibiti,wlh muna zuwa ya kasa fitowa da kansa sai shigar shi aka yi,Yana nan ana bashi kulawa,Mama tace wanne asibitin kuke? Global health clinic,Gani Nan cewar Mama,hankalinta a tashe ta nufi asibiti.
Zuwanta ke da wuya ta samu Likita ya fito Yana cewa zaku iya shiga kuga Jikin shock ya samu saura kadan zuciyarsa ta samu matsala amma Allah ya kiyaye,Mama ta shiga tana salati,Haneef ta samu a kwance Yana bacci ta hau kuka a hankali sabo da kar ta tashe shi,Driver ta samu tace Dan Allah kula da shi dole na tafi gidan su Khadija bani address,Driver yace mama ki bari yamma tayi,Mama tace a'a kyale ni yaron nan shi kadai na Haifa duk duniya bani da kamarsa Allah ne gatana shine gatana,Driver ya bata number kuwa ta tafi garin,Bata Isa can ba sai da magriba,da tambaya aka nuna mata gidan su Khadija ta shiga,lokacin Khadija bata nan ta tafi gidan Yan uwan Mahaifinta.
Jummai tana ganin Mama taga suna yanayi da Haneef,hannu bibiyu ta karbeta a dakinta ta kawo mata ruwa da tuwon daren data kwashe,Mama Sallah ta fara gabatarwa sannan tace nasan baki sanni ba,ai nice mahaifiyar Haneef,Jummai tace ai kuwa naga kamanni, nasan kin San mene ne ya faru tsakanin Khadija da Haneef,kaddarar data fada musu,wlh sharrin shedan ne,Dan Allah ku yafe masa,Khadija nazo na bawa hakuri tayi hakuri ta yafe Masa Dan Allah,tace a sanadin wannan abin Haneef yana kwance a asibiti,Mero ce ta shugo gidan ta tsinci Mama tana cewa Haneef yazo ya samu Khadija tace wani ya turo wlh bai koma gida da lafiya ba sai asibiti aka kaishi Yana can bai San Ina yake ba,zuciyarsa ce ta samu shock saura kadan ta samu matsala Allah ya tsare,Dan Allah kuyi hakuri ku yafe Masa,Sallama Khadija tayi kamar bata ji zancen ba amma hankalinta a tashe yake.
Ciki ta shiga tace laaa Mama kece? Mama taji dadin yanda Khadija ta mata tace nice Khadija nazo baki hakuri har gida,Dan Allah ki yafewa Haneef,Khadija ta furta ai na yafe Masa ni tuni,Mama taji dadi tace na gode, Dan Allah ki aure shi Khadija,Mero tace ai ni wani nake so Mama,Dan Allah yayi hakuri,Jummai tace Kinga Maman Haneef na bashi ita rabu da ita,a kawo kudin aure wlh ko a gobe a daura indai kun kawo kudin aure da sadaki a ranar za a daura,Khadija zata yi magana Jummai tace kina magana wlh sai mun raba gari,Shuru Khadija tayi ta tashi ta fice,Mama tace kar ayi mata dole dan Allah,Kyaleta karya take tana sonsa wlh cewar Jummai,suka gama Kus Kus dinsu da Maman Haneef sannan taci tuwon kadan tace ta koshi a daren ta samu me taxi dan garin ya kawota birni drop.
Asibitin ta koma ta samu Haneef a zaune Yana cin Ayaba,farin ciki tayi ta zauna a gefensa tana tambayarsa ya jikin? yace da sauki,Yana cin Ayaba Yana Jan tsaki shi kadai,Mama tace Haneef ka kwantar da hankalinka Inshaallah gobe sai an daura Maka aure da Khadija,Haneef yasan ma bazai yuwu ba,yace hmm kawai Allah ya kaimu,ka shirya gobe da kawunka zasu zo har abokinka Isma'il ka gayyato tunda Kai naga baka fiye abokai ba,Haneef ya kalleta kawai dan bai San taje garin ba ma Kuma bata fada Masa ba.
Washe gari da safe aka sallame su Mama ta damu sai Haneef yayi shiri,cikin sababbin kayansa ya saka wata tsadajiiyar shadda fara kar,bai sa hula ba tace ai dole sai ya saka,haka ya saka ya shirya sosai ya fito a angonsa,jikinsa a sanyaye yasan tatsuniya ce,ita kuwa Mama har ta fara Shirin hada Lefen ma,Su Kawu su biyar suka iso daga Adamawa suka tafi a mota biyu har abokin Haneef Isma'il suka tafi garin su Khadija,Munnir shi ya raka su har gidan dangin Sani ubansu Wanda Jummai taje ta fada Masa Khadija ta samu miji na kirki amma taki yarda,ita ta gaji da girman Khadija a gida,zasu kawo kudin aure da sadaki kawai a daura aure.
Yace ai dama kune kuke kyaleta duk garin Nan babu sa'an Khadija Allah ya kaimu za a daura indai kin gamsu da tarbiyyarsa da Halayensa da gidan da ya taso ba matsala,Jummai tace na gamsu,sun San masifar Jummai sannan sun gaji da ganin Khadija taki aure a kauye ko wacce ana mata aure banda ita,Yan uwa ya fadawa,kowa yaji sai murna za a aurar da Khadija a daina musu gori a gari.
Washe gari tun kafin suga angwaye suka Tara mutane a masallaci ana jira,Munnir yasa Yar wankakkiyar shaddarsa ya rakasu masallacin,Haneef ji yayi kawai ana cewa ga angwaye sunzo,mamaki ya kamashi dan bai zaton hakan ba,su Kawunsa ne akan komai sune suka Bada dubu Dari biyu kudin aure sannan Kuma aka Bada sadaki dubu dari biyu Shima,Dangin Khadija suka ce yayi tsada gaskiya su a rage,Haneef yace baza a rage mata ba ai sunyi ma kadan,Isma'il Yana ta mamakin auren Haneef haka Emergency,Nan take Liman yayi Khuduba mutane suka sheda aka daura auren Khadija Sani da Haneef.
Ana gamawa Haneef yaji hankalinsa ya kwanta nutsuwa ta zo Masa,wani irin farin ciki da nishadi ne suka lullube shi,ji yayi a duniya Kam baida Matsala shi dai,yace Anya kuwa da gaske ne ba mafarki nake ba? Isma'il yace da gaske ne duk mun sheda sai mu tafi gida sai an kawo Amarya,Haneef yace ni a nan zan yini kabi su Kawu ku tafi driver na muna tare, Isma'il ya zaro ido amma Haneef shi ba komai Aboki ke sani nasa ba shi yasa Isma'il bai San komai ba akan Haneef sai kadan.
Su Kawu yabi suka tafi Haneef da driver dinsa suka je gidan Khadija,yaga ana ta shiga Allah Sanya Alkhairi yace ashe dai da gaske ne,yaro ya tura gidan yace a kira Khadija inji Angonta,Khadija tana ta kuka an daura aurenta da Haneef,tana daki ta boye kanta,itama Jummai bata nunawa mutane ita,Yaro ne ya shugo yace Khadija tazo inji Angonta Jummai tace kace gata nan,da kanta ta shiga dakin Khadija tace tashi ko na ci ubanki,Kuma wlh in Baki je ba Khadija sai na tsine miki ki tashi kije tun wuri saura ki Masa fitsara,Khadija ta tashi tana hawaye,wanka ma da kyar tayi,taki yin kwalliya ta zauna daga ita sai vest da skert na atamfa,Hijab Jilbab ta dauka har kasa dogo me hannu ta saka tana goge hawayenta Wanda ya kasa daina zuba.
Yana ganin ta fito ya sallami driver yace zan kira ka,Driver ya Kalli Khadija yace ki shiga bayan mota Yana ciki,maganar mahaifiyarta ta tuna dole ta bude motar cikin fushi ta shiga ta zauna bata Kalli Inda yake ba ta sake fashewa da kuka,Haneef ko a jikinsa shi hankali kwance,yayi murmushi tare da riko hannunta,da sauri tasa hannu ta make Masa hannu ya saki ba shiri,yace kiyi hakuri Khadija,ba laifina bane na miki dole ki aure ni, Dan Allah kiyi hakuri ya kwantar da kansa a kafadarta ta janye jikinta da sauri tana harararsa,Kyaleta yayi yace zan tafi,mota ta bude fuuuuuu ta shige gida abinta,driver ya kira suka wuce,sai bayan ya koma gida Mama ta bashi labarin yanda aka yi har aka daura Masa auren da Khadija.