← Book details Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 68

Sashe 25

Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Tunda ta fara aikin ita yake kallo ba yanda ake girkin ba,ita Kuma sai bayani take Masa,tace yanzu yanka min albasa mu gani,Yana can ya kura mata Ido tace ka yanka min Albasa nace me kake tunani? dawowa yayi hayyacinsa yace sorry me kika ce? ka yanka min Albasa zo na koya Maka,yace kin San a kayan aikin nan ma kyau kika yi,Khadija tace Dan Allah? Yace t-shirt din ta miki kyau,na gode ta furta tare da mika Masa wuka tace kaga yanda zaka yanka haka,kamar haka to fara,fara yi yayi a hankali Dan bai iya komai ba,Kayi kokari gaskiya kawo ka gani,ta rike hannayensa da wukar a hannunsa suna yankawa a haka,dariya yayi yace na iya daga yau wow,Ihsan ganin shuru yaki fitowa ta shugo kitchen din,a zabure fakat da sauri ya dauki wani cup ya basar ka rantse dama shi yazo dauka tuni ya matsa daga kusa da Khadija,agogonsa yake gyarawa ga cup a hannunsa,Mero Kuma tukunya ta bude itama tuni a zabure a tamanin itama ta fuske,har goshinta take sosawa sabo da babu gaskiya,Ihsan kamar ta gansu manne da juna amma sai Kuma taga kamar idonta ne ya mata gizo,kallon su ta hau yi sosai tana so ta fahimci wani Abu amma sai ji tayi Khadija tace Oga kawai ka bar naman nan yayi kaga bai dahu ba ka daina jira in yayi zan kawo maka,Kallon Khadija yayi lokacin ta dago Kai suka hada Ido"Ido daya ya kashe Mata tare da murmushi,labbanta ta tamke tana mannewa kar ma tayi murmushi.

Ihsan anci da rabonta tana danna waya tana dagowa har sun gama ya fice abinsa,Mama ya samu tana kallon film,Ihsan kuwa Mero ta kalla tace munafuka yanzu wato Kinga uwarsa kin saka kayan aiki,Mero tace Daya muke bakya girki ko cokali bakya dauke wa kince bakya so Yan aiki suyi miki girki,me take so zaki dafa mata ni Kuma Kinga Ina da kayan gayu na canja nasa na aiki,wlh kina fadar Abu a kaina sai na tona miki asiri yau kiyi karyarki da kika Saba kawai Nima nayi tawa,Ihsan ta Kalli Khadija tace karfa mayya sarkin naci an Kore ki kinki tafiya,na tsane ki Yar Zina,Khadija tace oho miki Kuma.

Khadija sai da ta gama miyarta gefe daya tana tuka tuwon danyar shinkafa,shugowa Haneef ya sake yi ya bude fridge ya dauki lemon gongoni,ya sake cewa kawo na gwada tukawa ya ajiye lemon a gefe,ta bashi tana murmushi Yana farawa yaji tafiya kamar mutum na tahowa sakin muciyar yayi ya dauki lemonsa ya juya baya a zuwan budewa yake,Ihsan ce ta sake biyo sawu ta ga me yake yi wai.Khadija bata kulata ba haka ta gama girkin ta kaiwa Mama,taci itama sai yabawa take yi sosai.
Mero ta dawo ta gyara wajen bayan ta gama ci tace Mama kina bukatar tausa? Mama tace a'a Yar nan na gode kawai dai ga magani na shafa min a Kafafuna,Haneef Yana zaune Khadija tace Oga ga aikin Lada kazo ka samu Ina Maka fatan samun wannan ladan, tashi yayi ya karbi maganin,Mama sai murmushi take yi tace kaji yarinyar kirki me Ankarar da bawa hanyar samun lada,murmushi Khadija tayi,Wallahi kin birge ni Kuma duk Wanda ya aure ki yayi dace Khadija,Haneef da sauri ya tambaya yace Allah Mama? tace duk Wanda ya aure ta ya samu macen kirki,Ihsan tana gefe baki ta tabe ta dauke kai,Mero tace Mama na gode za a miki wani abu ne? tace a'a an gode jeki uzurinki yarinyar kirki,Mero ta shige dakinta ta dinga sheka dariya tana tsalle a Saman bed tana cewa na ninke Mama bata Yar iska bace ni,babu wani ta gari,wai nice nutsatsiya dama ba Tinkiya aka yanka min ranar suna na ba.

Washe gari Arham kin fitowa yayi Sam kar Basma ta ganshi ta fada tace ya taba ta,Basma kuwa tunda ta tashi take zuba Ido ko zata ganshi ita hirar jiya tayi mata dadi kwana tayi tana tunawa,Mima ta tambaya a Palo tace Mima tana Sosa Kai,Mima tace ya aka yi? tace dama jiya ya manta abinsa zan bashi Kuma ban ganshi ba,Mima tace bai fita ba ai Yana nan zai fito ne,naje na Kai Masa? Mima tace a'a ki bari ya fito,tace to ta zauna,Maman Rafeeq tana zaune tace karki sake naga kafarki a part dinsu ba a zuwa wajen namiji ki dinga taka tsantsan,Papa ne ya shugo da alama fita zaiyi ya samu Maman Rafeeq suna yiwa Basma fada karta je part din Maza,Mima tace ki bari ya neme ki da kansa,yaran zamani sai addua kuwa,Basma tace ai kuwa sai dai kar a Kuma jiya zip ya bude min yace kwaro ne a ciki wlh ya taba min kirji na,Amma karki fada Masa yace kar na fada,Ran Papa ya baci yace yanzu auren da za ayi Masa bazai iya hakuri ba,Basma tace ba haka bane ba fa yace kar na fada Dan Allah kuyi hakuri na yafe Masa nidai,Papa ya fusata,Mima tace Dan Allah kayi hakuri,yace ba ruwanki a gabanki yarjejeniya muka yi da shi da sharadi idan ya sake sai ya bar gidan Nan yace ya yarda,Kuma yanzu ya Maida ni dan iska,Mima tace to yanzu in kace ya bar gidan Nan Ina zai je? Kuma wa zaka yiwa auren? Papa yace na fasa bashi ita sai ta auri Shaheed shi ya bar min gida.

Mima ranta ya baci tace yanzu...dakatar da ita yayi yace shi yasa suka gagari kowa,ke baza a yiwa yaranki fada ba baza a hora su ba,ya isa in zauna inyi yarjejeniya da shi sannan ya sake gwadawa shi din banza,Ina Arham ya tambayi Haly da shigowarta kenan,Yana part din su,yace kira min shi maza,ai Arham Yana ji ance papa na kiransa yasan ba lafiya,Haly tace da alama Basma ta fada Masa,Salati Arham ya saki Wanda ke shiryawa wanka yayi dama,yace guard room zai sa a sani ko ya kaini Barack a gana min azaba,Haly tace wlh kayi ta kanka Kai kasan ba iya korarka zaiyi ba kasan kalar korar Barack za a kaika kayi sauri na bude ma kofa ta baya,Arham ya kwashi takalma a hannu Suka fice a hankali ta bude Masa kofar kitchen ta baya yabi ya fita,ta waccen gate din na baya ya bi ya bar gidan Yana fita Papa Yana kiran securities sojoji yana bada sanarwa a rufe gida kar a bari Arham ya fita.

Suka kulle ko Ina suka hau zaga gida da bindigu,sama ko kasa an rasa Arham,Haly tace na duba ko Ina baya nan,karya kike papa yayi kanta da jibga,Basma ta mike ta gudu tana cewa nidai bakuwar ce kar a hada dani ta arce daki,Haly da kyar ta Sha a hannun Papa ta kulle kofa tana kuka,Mufee tace Allurar Papa ta motsa ta sojoji,Arham kuwa Spark ya kira ya fada Masa,Spark yace me kayi to? Yace Basma fa kawai na rungume,karya kake Arham wlh idan baka Fadi gaskiya ba bazan rufa Maka asiri ba duk Inda kake sai an Nemo ka,Arham yace to abin na taba,Kuma wlh ni kawai ji nayi akwai ko babu ba da iskanci nayi ba,shine ta fada,Spark yace tab yanzu karka je gidan abokai Dan za a bika kana Ina? yace gani a taxi? zo Office dina kayi sauri,Arham yace na tabowa kaina masifa nonon Basma ko Masifa,Yana zuwa" Office din Rafeeq Spark yakaishi ya sa key ta baya ya kulle su har Rafeeq a ciki,Rafeeq yace ni a bude ni na tafi gida, ni ba da iskanci ba a kulle da ni,Spark bai ko kula shi ba.

Rafeeq ya Kalli Arham yace kwarto,Ka taba me tsada yau dubunka ta cika,Arham yayi dariya yace bana dana sani Kuma ban Jin na gama tabawa, samun lafiya a daura auren nan,an lasa min zuma,yace wai Shaheed zai bawa ita,wlh bani ba Shaheed matukar ya karbi auren nan mun raba gari,Dariya Rafeeq yayi yace daga taba abu,yace ba haka bane,ai cin fuska ne wannan a bani mace ace za a canja ai ba daidai bane,ni har naji ma Ina Jin haushin Shaheed din.
Rafeeq ya Kalli Arham yace baka Jin magana Arham,muga hannun ya canja tunda an Sha Laushi,Arham dariya yayi yace Kai da ka kwana a gidan surukai wa yasan me kayi, a gidanmu kowa Yana da abin fada ba Wanda zaiwa wani gori tun daga kakanni manya har yaran,Rafeeq yace Allah? Kaka Zeenatu ma karuwanci tayi,ai ance shahararriyar Karuwa ce da,harda kasa kasa da Murya yace Shima Maleek din ai a can suka hadu a Bariki suka yi aure,Rafeeq ma yayi kasa da Murya yace Allah Kai? Allah da dadironta ne ya aure ta daga baya,ta nace masa ai ance Zeenatu tayi Zuma ta more,duk Wanda ya dandana sai ya koma ta tara abin duniya da Bariki,Misam ne dai da ya shiga shi haka ya fito ba uwar komai sai nasa da ya kashe,Ashar Rafeeq ya dura Masa yace Dan iska munafuki duk a Ina kaji labarin nan Kai? Suna dariya Arham yace zancen duniya Yana buya ne,Mamanka ma uwar goyonka ai ance tayi Uhum Uhum kadan,Wlh zan tona ma asiri Papa yazo ya tafi da kai.
Chapter 25 · 0% Book details