Sashe 4
Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Khadija Sani Uba Mero kenan Yar kauyen Kano ce cikin wani kauye dake Danbatta,Khadija su biyu Iyayensu suka Haifa,Khadija itace ta farko sai kaninta Muneer,Babar Khadija Bata da tausayi gata da masifa kamar me Wanda ba boka babu Malam ta mallake mijinta sai abinda tace kasancewar Sani shi wani gashi nan ne dai sanyin Hali ne da shi sai abinda aka ce da shi,duk Inda akace Yayi to Hakan zaiyi kuwa,bashi da gidan kansa,Yana kallo tana cutar da yaransa ba karatun addini bare na Boko sai talla da aikatau baya so amma bazai iya magana ba,komai tace an gama kawai.
Gashi duk Inda zata je kamar jaka sai tace sai ya rakata idan da kayan shi zai daukar mata har Inda zata je kawai umarni take bashi,Kuma shi zai fita ya Nemo,banbancinsa da su Abba Dolo shi Yana da zafin nema amma Kuma sai abinda aka ce da shi,matarsa Hajiya Jummai ta hanashi rawar gaban hantsi ga masifa,su Khadija haka suka taso suka ga tana yiwa ubansu,taci kwalarsa ta zazzage shi ba abinda zasu iya.
Yau ma gidan ya shugo ya Kai wani gero kasuwa Yana dawowa ya fito da kudin ya zube mata a gabanta yace gasu ki duba kiyi abinda ya dace ni na dauki dubu uku ciki,Baki ta bude ta ajiye tire din dake hannunta gata kyakyawa da ita sai masifa,tace ban gane ba akan wanne dalili zaka dauki dubu uku zube ka dauki dubu daya ta isheka,Muneer Yana zaune Yana cin tuwo yace haba Inna mutum da amfanin gonarsa ya siyar duk ya Baki kudin akan ya dauki dubu uku shine zaki ce bazai dauka ba,Kai rufe min baki ko nazo na taka wuyanka,Sani Wanda suke kira da Uba yace kyale a bata Muneer ba komai dubu dayan ma ta isheni" ya dauki dubu dayansa kawai ya koma dakinsa ya kwanta.
Zuwa yamma ta fito zata je gidan suna ta gama shiryawa tace Sani fito ka daukar min kayan barkar nan muje,haka ya fito ya karbi Yar ledar suka fice da yadinsa brown ishirunka maraya,ita Kuma ta Sha atamfa blue da hijab,suna tafiya suna Hira sai kace wasu matasa,abinda take so ita kenan duniya ta San ta mallake mijinta sai abinta tace,ana ta gulmar su ita kuwa tana Jin dadi,yace yaushe zamu je wajen Khadija ne? tace sai an siyar da Masarar da zata zo kwana nan,kasan kudin mota tsada rayuwa tayi tsada.
Yace ke da yarki kamar ba ke kika haife ta ba,fuska ta bata ya ja bakinsa ya tsuke Yana tsoro,nesa da ita ya matsa Yana tafiya tace dawo wannan hanyar,yace ta Nan tafi sauri mubi ta nan,to bazan bi ba ta nan nake so" haka ya dawo Inda tace suka ci gaba da tafiya.
Yau abokin Sani ya gaji ya sake dawowa har gida ya kira Sani,yace gaskiya ka canja hali abinda kake yi Sani a garin Nan bai dace ba Sam,ace mace ta Maida ka kamar Rakumi da akala wlh mu Maza bama Jin dadin Hakan Sam,ka duba yau fa wai gidan suna ka rakata,Sani fuska ya Bata yace Dan na raka matata laifi ne? Shi yasa ku mutanen kauye har kullum Jummai take fada min na fita sabgar ku baza ku waye ba,tace dama na daina kulaka nine na nace nake Maka alfarma,amma mene aibun Hakan? Ko Jummai ta fada min tace a Makkah ma haka ake yi karewar garin addini kenan haka Maza suke wa matansu,to Kai Sani Balarabe ne ko al'adarmu Daya? Koyi nake da su karku dameni Kuma duk Wanda ya zageni ko yayi gulmata da gulmar Iyalina ban yafe ba,Abokin Sani ana ce Masa Malam yace yanzu yau fa har hannu ka rike mata a titi haba yara suna kallo ba tsari,matar tawa Dan na rike mata hannu koyi nake da Larabawa ko a gaban yarana na cikina zan rike mata hannu,baya ga haka ma ba yin kaina bane itace tace na rike mata shike nan bazan yi ba sai na watsa mata kasa a Ido.
Tayi min komai na gidan ta tuka min tuwo na ci da yarana Dan kawai tace rike min hannu Sani sai na kasa sabo da ni Dan iska ne ko me? Ko a garin Fir'auna aka haife ni,karku sake shiga harkarta da iyalina,gaisawa dai mu gaisa amma Banda shiga lamarin auratayya ta,gaisuwar ma ba dole In Kuna ganin da matsala ku kyaleni,amma ni sai me Dankwali sai abinda Jummai tace yawwa.
Malam yace Allah ya ganar da Kai,yace Ameen ya shige gidansa
Yana shiga gidan ya kwashe zancen ya fadawa Jummai,Jummai tace ai na Dade da fahimtar Malam munafuki ne rabu da su makiya mahassada.
Chika tana zaune a Palonta ta mimmike Misam Yana mata tausa sabo da tana da ciki,sai langabewa take tana Nishi,Me unguwa Maman Chika da Baban Chika mahaifi ne suka zo,Chika tayi mamaki babu Sanarwa,Misam ne ya bude musu kofa suka shugo Sanyi da kamshi ya daki hancin su,Chika tana ganin Me unguwa ta hade rai tace me ya kawoka gidana,Abban Chika yace Suhailat bana son shashanci ki nutsu,Misam gaida su yayi a mutunce Yana musu sannu da zuwa.
Chika ta zauna ta hade rai ganin Me Unguwa,Mamanta ce ta kalleta ta Harareta sannan ta gaishe su ta mike taje ta kawo musu kayan Sha da ci tace kar wannan ya sake ya Sha min lemo na,Kin San Allah zan Saba miki me yasa bakya ji ne,Misam ne ya mata rada yace calm down su Abba ne fa,Abba ne yayi magana yace dama Me unguwa ne yayi nadamar abinda yayi yazo baki hakuri akan ki yafe Masa,bazan yafe Masa ba kuwa sai dai a bar shari'ar nan ayi ta a gaban Allah.
Abba ne ya share Suhailat ya Kalli Misam yace Kai nasan kana da hankali,Suhailat da kake Ganinta bata Jin magana,ni na haife ta amma nasan halinta sarai,lokacin Ina auren babarta Ashe Me Unguwa tsohon saurayin Maman Suhailat ne" to ni ban sani ba Ashe haushina yake ji na kasa shi na aure Masa budurwa,tunda na aureta ta haifi Suhailat yarta ta fari kenan muna zaune lafiya ashe me Unguwa shi kullum budurwarsa tana ransa burinsa ya kashe mata aure ta fito ya aure ta.
To bayan Suhailat ta girma ta Kai 13yrs Bata sake haihuwa ba,da ta samu ciki sai bari,Ashe Me unguwa ne yayi mata asiri ake zubar da cikin bamu sani ba,karshe da yaga dai baza ta fito ba sai ya hada baki da wani ya bashi kudi ya shiga dakin matata da dare lokacin tana kitchen ni Kuma na shiga Ina shiga na iske Kato a kan gadona na sunna a tube zigidir,kuskure na banyi bincike ba sai na saketa saki uku,ta koma gida katsina kenan Inda Me Unguwa suke dake duk unguwar su daya,da Suhailat ta tafi,cikin ikon Allah data fito shima bai aure ta ba sai ta auri wani,daga Nan ya fara Jin haushi Yana binta da sharri,ita Kuma Suhailat haushinsa take ji Yana son uwarta tunda taji Labari.
Ganin bai samu uwa ba sai ya dawo kan Suhailat tsofai tsofai wai ita yake so,tayi tayi ya daina kulata yaki,sai sharri ma da yayi mata duk abinda ya faru sai yace Suhailat tana ciki,Kullum tana wajen Yan sanda,karshen sharri wata yarinya aka tsinta a bola an mata Yankan rago,me Unguwa kiri kiri kiri yace yaga Suhailat da idonsa da mutane sun sauke yarinya a mota karama,ya kira Yan sanda ya bada rahoto kawai bata San zance ba aka kamata Kuma ya dage da hadin bakin wasu dattawan na unguwa tsofaffin banza sai da aka kaita gidan yari bada hakkinta ba,sharri ba Wanda baiyi mata ba,yaje ya bada shedar zirrrr a kotu,gashi yanzu Yana dana sani da nadama,Misam Yana gama saurara yace ahhh da gaskiyar Suhailat a bar sharia sai a lahira
Me unguwa ya dinga rokon Suhailat da kyar da lallashi Chika tace ta yafe Masa a haka ma dole aka mata,Maman Chika ta furta idan Allah Bai baka abu ba duk duniya ba Wanda ya isa ya baka,Me unguwa ka cuceni ka kashe min aure Kuma da na fito ban aure ka ba shine ka koma kan 'yata itama Allah baiyi ba sai da ka kulla mata sharri,wani mutumin babu amfanin saninsa a rayuwa wlh,Me unguwa kansa a kasa yace a yafe min sharrin shedan ne inshaallah zan gyara Halayena,Misam shi dai tunda yaji ance ai ya taba cewa Yana son Chika sai haushin Me unguwa yake ji ya matsu su tafi,Chika ya kira bedroom ya bata hijab yace ungo saka ga tsohon saurayinki nan matsiyaci Dan iska tsohon banza tsohon wofi,ai a haka zai kare rayuwarsa azzalumi wlh na tsane shi tunda yace Yana sonki ni da shi gaba har mutuwa,Chika tayi dariya tace Dan ma baka sani ba lokacin ya zaci bani da wayo naje wucewa watarana ta kusa da gidansa da dare ya taba min duwawu,ai kuwa na saka kuka naje na Kai kararsa sai da aka mana tsakani.
Misam ya rike baki yace fyade zai miki ai da haka ake yin fyade ni kiyi sauri su tafi suma su mama mene na zuwa da shi ko ta waya ai a yafe Masa,Hannunsa taja tare da dorawa a Saman cikinta tace kaji babyn mu,Murmushi yayi tare da shafa cikin yace ko mace ko namiji Allah yayi albarka, suka fito suna zuwa palon Misam yace ai Mama da Kun sani ma ta waya kuka kira sai a yafe Masa ko kuzo ku kadai ba sai da shi ba,gwara dai da muka zo yafi yana ta binmu Yana bada hakuri,Misam haka ya kaisu har wajen Mima suka gaisa suka ce tafiya zasu yi harda sauri siya musu ticket din jirgi sabo da kar ma ace dare yayi zasu kwana,da dai iya Iyayen Chika ne ba matsala,Yana kaisu airport bayan sun tafi ya dawo ya iske Haly da Mufee wai sunzo zasu kwana.
Gashi duk Inda zata je kamar jaka sai tace sai ya rakata idan da kayan shi zai daukar mata har Inda zata je kawai umarni take bashi,Kuma shi zai fita ya Nemo,banbancinsa da su Abba Dolo shi Yana da zafin nema amma Kuma sai abinda aka ce da shi,matarsa Hajiya Jummai ta hanashi rawar gaban hantsi ga masifa,su Khadija haka suka taso suka ga tana yiwa ubansu,taci kwalarsa ta zazzage shi ba abinda zasu iya.
Yau ma gidan ya shugo ya Kai wani gero kasuwa Yana dawowa ya fito da kudin ya zube mata a gabanta yace gasu ki duba kiyi abinda ya dace ni na dauki dubu uku ciki,Baki ta bude ta ajiye tire din dake hannunta gata kyakyawa da ita sai masifa,tace ban gane ba akan wanne dalili zaka dauki dubu uku zube ka dauki dubu daya ta isheka,Muneer Yana zaune Yana cin tuwo yace haba Inna mutum da amfanin gonarsa ya siyar duk ya Baki kudin akan ya dauki dubu uku shine zaki ce bazai dauka ba,Kai rufe min baki ko nazo na taka wuyanka,Sani Wanda suke kira da Uba yace kyale a bata Muneer ba komai dubu dayan ma ta isheni" ya dauki dubu dayansa kawai ya koma dakinsa ya kwanta.
Zuwa yamma ta fito zata je gidan suna ta gama shiryawa tace Sani fito ka daukar min kayan barkar nan muje,haka ya fito ya karbi Yar ledar suka fice da yadinsa brown ishirunka maraya,ita Kuma ta Sha atamfa blue da hijab,suna tafiya suna Hira sai kace wasu matasa,abinda take so ita kenan duniya ta San ta mallake mijinta sai abinta tace,ana ta gulmar su ita kuwa tana Jin dadi,yace yaushe zamu je wajen Khadija ne? tace sai an siyar da Masarar da zata zo kwana nan,kasan kudin mota tsada rayuwa tayi tsada.
Yace ke da yarki kamar ba ke kika haife ta ba,fuska ta bata ya ja bakinsa ya tsuke Yana tsoro,nesa da ita ya matsa Yana tafiya tace dawo wannan hanyar,yace ta Nan tafi sauri mubi ta nan,to bazan bi ba ta nan nake so" haka ya dawo Inda tace suka ci gaba da tafiya.
Yau abokin Sani ya gaji ya sake dawowa har gida ya kira Sani,yace gaskiya ka canja hali abinda kake yi Sani a garin Nan bai dace ba Sam,ace mace ta Maida ka kamar Rakumi da akala wlh mu Maza bama Jin dadin Hakan Sam,ka duba yau fa wai gidan suna ka rakata,Sani fuska ya Bata yace Dan na raka matata laifi ne? Shi yasa ku mutanen kauye har kullum Jummai take fada min na fita sabgar ku baza ku waye ba,tace dama na daina kulaka nine na nace nake Maka alfarma,amma mene aibun Hakan? Ko Jummai ta fada min tace a Makkah ma haka ake yi karewar garin addini kenan haka Maza suke wa matansu,to Kai Sani Balarabe ne ko al'adarmu Daya? Koyi nake da su karku dameni Kuma duk Wanda ya zageni ko yayi gulmata da gulmar Iyalina ban yafe ba,Abokin Sani ana ce Masa Malam yace yanzu yau fa har hannu ka rike mata a titi haba yara suna kallo ba tsari,matar tawa Dan na rike mata hannu koyi nake da Larabawa ko a gaban yarana na cikina zan rike mata hannu,baya ga haka ma ba yin kaina bane itace tace na rike mata shike nan bazan yi ba sai na watsa mata kasa a Ido.
Tayi min komai na gidan ta tuka min tuwo na ci da yarana Dan kawai tace rike min hannu Sani sai na kasa sabo da ni Dan iska ne ko me? Ko a garin Fir'auna aka haife ni,karku sake shiga harkarta da iyalina,gaisawa dai mu gaisa amma Banda shiga lamarin auratayya ta,gaisuwar ma ba dole In Kuna ganin da matsala ku kyaleni,amma ni sai me Dankwali sai abinda Jummai tace yawwa.
Malam yace Allah ya ganar da Kai,yace Ameen ya shige gidansa
Yana shiga gidan ya kwashe zancen ya fadawa Jummai,Jummai tace ai na Dade da fahimtar Malam munafuki ne rabu da su makiya mahassada.
Chika tana zaune a Palonta ta mimmike Misam Yana mata tausa sabo da tana da ciki,sai langabewa take tana Nishi,Me unguwa Maman Chika da Baban Chika mahaifi ne suka zo,Chika tayi mamaki babu Sanarwa,Misam ne ya bude musu kofa suka shugo Sanyi da kamshi ya daki hancin su,Chika tana ganin Me unguwa ta hade rai tace me ya kawoka gidana,Abban Chika yace Suhailat bana son shashanci ki nutsu,Misam gaida su yayi a mutunce Yana musu sannu da zuwa.
Chika ta zauna ta hade rai ganin Me Unguwa,Mamanta ce ta kalleta ta Harareta sannan ta gaishe su ta mike taje ta kawo musu kayan Sha da ci tace kar wannan ya sake ya Sha min lemo na,Kin San Allah zan Saba miki me yasa bakya ji ne,Misam ne ya mata rada yace calm down su Abba ne fa,Abba ne yayi magana yace dama Me unguwa ne yayi nadamar abinda yayi yazo baki hakuri akan ki yafe Masa,bazan yafe Masa ba kuwa sai dai a bar shari'ar nan ayi ta a gaban Allah.
Abba ne ya share Suhailat ya Kalli Misam yace Kai nasan kana da hankali,Suhailat da kake Ganinta bata Jin magana,ni na haife ta amma nasan halinta sarai,lokacin Ina auren babarta Ashe Me Unguwa tsohon saurayin Maman Suhailat ne" to ni ban sani ba Ashe haushina yake ji na kasa shi na aure Masa budurwa,tunda na aureta ta haifi Suhailat yarta ta fari kenan muna zaune lafiya ashe me Unguwa shi kullum budurwarsa tana ransa burinsa ya kashe mata aure ta fito ya aure ta.
To bayan Suhailat ta girma ta Kai 13yrs Bata sake haihuwa ba,da ta samu ciki sai bari,Ashe Me unguwa ne yayi mata asiri ake zubar da cikin bamu sani ba,karshe da yaga dai baza ta fito ba sai ya hada baki da wani ya bashi kudi ya shiga dakin matata da dare lokacin tana kitchen ni Kuma na shiga Ina shiga na iske Kato a kan gadona na sunna a tube zigidir,kuskure na banyi bincike ba sai na saketa saki uku,ta koma gida katsina kenan Inda Me Unguwa suke dake duk unguwar su daya,da Suhailat ta tafi,cikin ikon Allah data fito shima bai aure ta ba sai ta auri wani,daga Nan ya fara Jin haushi Yana binta da sharri,ita Kuma Suhailat haushinsa take ji Yana son uwarta tunda taji Labari.
Ganin bai samu uwa ba sai ya dawo kan Suhailat tsofai tsofai wai ita yake so,tayi tayi ya daina kulata yaki,sai sharri ma da yayi mata duk abinda ya faru sai yace Suhailat tana ciki,Kullum tana wajen Yan sanda,karshen sharri wata yarinya aka tsinta a bola an mata Yankan rago,me Unguwa kiri kiri kiri yace yaga Suhailat da idonsa da mutane sun sauke yarinya a mota karama,ya kira Yan sanda ya bada rahoto kawai bata San zance ba aka kamata Kuma ya dage da hadin bakin wasu dattawan na unguwa tsofaffin banza sai da aka kaita gidan yari bada hakkinta ba,sharri ba Wanda baiyi mata ba,yaje ya bada shedar zirrrr a kotu,gashi yanzu Yana dana sani da nadama,Misam Yana gama saurara yace ahhh da gaskiyar Suhailat a bar sharia sai a lahira
Me unguwa ya dinga rokon Suhailat da kyar da lallashi Chika tace ta yafe Masa a haka ma dole aka mata,Maman Chika ta furta idan Allah Bai baka abu ba duk duniya ba Wanda ya isa ya baka,Me unguwa ka cuceni ka kashe min aure Kuma da na fito ban aure ka ba shine ka koma kan 'yata itama Allah baiyi ba sai da ka kulla mata sharri,wani mutumin babu amfanin saninsa a rayuwa wlh,Me unguwa kansa a kasa yace a yafe min sharrin shedan ne inshaallah zan gyara Halayena,Misam shi dai tunda yaji ance ai ya taba cewa Yana son Chika sai haushin Me unguwa yake ji ya matsu su tafi,Chika ya kira bedroom ya bata hijab yace ungo saka ga tsohon saurayinki nan matsiyaci Dan iska tsohon banza tsohon wofi,ai a haka zai kare rayuwarsa azzalumi wlh na tsane shi tunda yace Yana sonki ni da shi gaba har mutuwa,Chika tayi dariya tace Dan ma baka sani ba lokacin ya zaci bani da wayo naje wucewa watarana ta kusa da gidansa da dare ya taba min duwawu,ai kuwa na saka kuka naje na Kai kararsa sai da aka mana tsakani.
Misam ya rike baki yace fyade zai miki ai da haka ake yin fyade ni kiyi sauri su tafi suma su mama mene na zuwa da shi ko ta waya ai a yafe Masa,Hannunsa taja tare da dorawa a Saman cikinta tace kaji babyn mu,Murmushi yayi tare da shafa cikin yace ko mace ko namiji Allah yayi albarka, suka fito suna zuwa palon Misam yace ai Mama da Kun sani ma ta waya kuka kira sai a yafe Masa ko kuzo ku kadai ba sai da shi ba,gwara dai da muka zo yafi yana ta binmu Yana bada hakuri,Misam haka ya kaisu har wajen Mima suka gaisa suka ce tafiya zasu yi harda sauri siya musu ticket din jirgi sabo da kar ma ace dare yayi zasu kwana,da dai iya Iyayen Chika ne ba matsala,Yana kaisu airport bayan sun tafi ya dawo ya iske Haly da Mufee wai sunzo zasu kwana.