← Book details Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 68

Sashe 27

Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Mima dai tace in Arham yayi tafiya baza ta damu ba ko kiranshi baza tayi ba amma kullum itace take fara kiransa,a rana sai ta kira shi yafi sau uku,yanzu ma kiransa tayi ya daga yace kika ce idan nayi tafiya ko nema na baza kiyi ba amma gashi yanzu kullum ke kike fara kirana,Mima tace ai ba wani missing Dinka nayi ba kawai dai Dan na tabbar da kana gidan Spark dinne kar ka tafi wani wajen,dariya yayi yace to na gode Ina Nan ai,ya fara hakura ai Basma tace zata bar gidan ta tafi baza ta hada Da da Uba fada ba,shine ya sakko yace ka dawo gida gobe,Arham yace ni nafi Jin dadin nan ma sai abinda naga dama a nan,to dai in ba so kake ka sake bata komai ba ka dawo gobe yace,Sai dai mu taho da Spark,to koma dai mene ta kashe wayar.

Washe gari da wuri su Basma suka zo,Arham Yana bedroom abinsa Yana kwance Yana danna waya,Yana Jin surutun su,Basma taji ance yana nan amma bata ganshi ba,gajiya tayi tace Aunty Ina Arham din? Naila tace Yana bedroom waccen room din,Basma ta mike taje ta kwankwasa yace come in,ta tura kofar ta shiga,Ido ta zaro tace bleaching kayi? Naga ka sake haske,wlh saurin girma ne da Kai kwana nawa da barin gida amma har ka Kara girma,Arham yace me zaki ce dani kin Sa an Kore ni daga gidanmu,a gefen bed din ta zauna tace ban zaci haka ba ganin Kuna abinda kuka ga dama na zaci baza a Maka komai ba shi yasa,amma ai gaskiya tana da zaki Kuma tana da daci ko baka yi ba? Baza ma ki bani hakuri ba? Da kayan sata ka kamani da zan baka hakuri,nifa mijin Naila shine dai dai ni dai dai shekaru na ba Kai ba Dan ma ka samu Ina kula ka,alfarma nake Maka fa,Arham yace na gode zaki San kina min alfarma, dariya tayi tace hmm ta mike tace na tafi,tashi yayi ya mike ta ganshi da tsayi tace kana zuba saurin girma a duniya,kullum sai ka Kara tsayi,ki bari sai an daura aure ki fada min haka.
Fitowa suka yi Yace kar a zargeni tunda ni yanzu na zama abin zargi a wajen mutane akan nono,abinda ma kowacce tashi tayi taga ya fito ba roka tayi ba Taga an bata shike nan sai a damu mutum sabo da anga mu bamu da shi sai mata su dinga wulakanta mu.

Sai dare su Basma suka tafi tare da Spark da Arham,Arham sai buya yake a bayan Spark Yana cewa Papa ko bai hakura ba wa ya sani wlh Allurarsa ta motsa,part din Papa suka shiga matan suka wuce bangarensu,Papa Yana Palo shi da Mima suka shugo,Arham yace Ina yini barka da dare,Papa yace zo nan Arham,Arham ya ja da baya yaki zuwa,Kazo nace rigar Spark ya rike,Spark yace baza ka sake ni ba,Dan Allah Papa kayi hakuri wlh bazan sake tabawa kowa ba nayi alkawari,dama wannan ma sharrin shedan ne ji nayi an ja hannuna ban San dalili ba,bana cikin hankalina nidai kawai sai Jin Abu nayi a hannuna ban San komai ba,please Papa dama ni shedan ya dade da yi min fitsari a ka,amma yanzu zan dage da Azkhar na Kore shi,Papa mikewa yayi yace zaka ga shedan ya Maka fitsari a ka,Arham ya rike Spark zai gudu,Papa yace ai ba abinda zan Maka ni,da zan Maka da tuni nayi tunda nasan gidan da kake kyaleta kawai nayi,ruwa ya dauka ya zauna,Spark ya fisge rigarsa ya zauna,Yana cewa Papa kayi hakuri mana haka ya tuba bazai sake ba cewar Spark,Arham yace wallahi tallahi in sake tabawa sai na halak,baza kayi shuru ba kenan? Mima ta furta,shuru yayi ya zauna a gaban Papa Yana bashi hakuri,Papa yace ai na daina yi Maka fada Arham na gaji,Arham yace a'a Wanda ya rasa mafadi ya shiga uku ai sai na tabe,Kaci gaba da yi min na daina wlh,dama rashin hakuri nane amma Shekara biyu Ina Shan na uwata,Yaya Rafeeq ne ya zugani yace kar na bari kaina ya kulle Shima haka yayi,Misam ma Yana wajen lokacin yace Shi da yayi Bariki ma ya tuba ba abinda ya faru da shi bare ni,shine na kama zancen su suka kaini suka baro ni,to sarkin karya cewar Mima,tace haka fa ya fadawa Basma yarinyar da zata zama surukata yace wai ni na zuga shi ya aikata mata haka,Papa yaso yayi dariya ya boye yace ai Allah ya Kara tunda bakya son laifin su,Arham gobe yaushe? Yace Friday ka shirya gobe daurin aurenka,idan aka daura daga baya ayi bikin sai a Kai Maka Amaryar,Arham yace a bari Papa in aka gama shiryawa sai ayi bikin a Kai Amarya lokacin kaga maybe na fara sonta,baka sonta ka taba ta,Spark yace gaskiya a bari sai an gama shiri wannan sai a kaita tana laulayi,Arham yace a'a da kunyata ni ba ruwana da ita ni,Papa yace na gama shiri wlh gobe ana Sallah za a daura yanda nace haka za ayi tunda shi baya Jin magana.

A daren Umma ta fadawa Abba cewar Beauty ta haihu,Abba yace amma kin ci amanata da baki fada min tun wuri ba, Kubra wlh watarana in kika yi min wani abin sai naji kamar na ambato kakanki Sarkin gandu Tanimu na zage shi,Yar Inna tace ai ka riga ka zage shi Kuma tunda ka Fadi Sunan,yace da Kuluwa me Kwan zabi,dariya Kubra tayi tace sai kazo ta kashe wayarta,duk kakannin Yar Inna ya ambata, minti kadan Abba yazo asibitin.

Ya kalli Mohsin yace ya suruka ta lafiyar ta kuwa? Mohsin yace tana ciki zaka iya shiga,Abba yace o'o'o Yar Inna ce kadai zata shiga wannan dakin na gumurzu na iya shiga kowa ya ji da tasa tunda dai lafiya take shike nan in ta fito na ganta,ya kira Jauro yace kayi jika na biyu Jauro,Jauro yace Matar Dan namu ta haihu ne? ta haifi Da namiji,yace Allah ya raya tunda lafiya take ai anyi arziki,gobe zamu zo Inshaallah. Washe gari aka sallami Beauty fes da ita da Baby,direct gidan Umma aka kaita in tayi sati biyu sai ta koma gidanta.

Abba yace wai nan aka kawota? wato mu a bata mana gida su Kuma su koma nasu gidan fes wannan ai wayo ne,kunci darajar babban bako me sunana,tun lokacin Abba ya bawa jariri suna Hasheem,ya kankane yace sunansa za a saka Masa,Mohsin yace dama ai sunan zan saka da mace ce Naila zan sa my love,Abba yace ai dama nasan sai ka mayar da sunanta itama haka Allah ya muku Albarka ya sake hada kanmu gaba daya,Mohsin yayi dariya yace harda Kai? Ku iyaye ai dole Kuna son mu ba matsalar komai mu yara mu za ace Allah ya hada kanmu,Abba yace harda ni mana idan na fandare fa na daina yi muku addua ai kaga gwara ace harda ni kanmu ya hadu,Mohsin yace to shike nan Ameen Yana dariya,Abba yace Azo a shiryawa Me jego farfesu suruka zata ci kudina a banza Nan da sati biyu tattalin arzikina Kuma ya kare ai,to kullum Yan barka zasu cika gida ayi ta girki ana saukewa ana dorawa,Allah ya taimake ku Abba ba irin na da bane Yan barka da Kun yini da yunwa a gidan Nan sai dai Kubra ta ci da ku ko Wanda aka haifar wa.

Spark a waya ya kira Mohsin da Beauty ya kira su Umma ya musu barka,Abba ya kira Shima ya Masa barka.
Kudin auren Rahma da Nabeela aka kawo sun fitar da mazajen Aure,Rahma Wanda suke rage zafi da shi suna Tabesting shine yaga gwara ya aure ta kawai bazai iya rabuwa da ita ba Sam,Shima Likita ne matashi bai fi mate din Annoor ba,Nabeela kuwa wani Wanda suke School tare ne da kadan ya girme ta sa'anta ne tare suka yi secondary har university,iyayensa suna da hali sosai shi yasa suka amince da yace zaiyi aure.
Jauro sai murna yake zai rabu da wasu yaran nasa lafiya shi dai.
Chapter 27 · 0% Book details