Sashe 3
Tantiriya A Gidan Yari Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Annoor kuwa Iman tunda ya samu ta dawo sai da ya lallabata da asuba ya sake Kwalbewa,Iman duk tayi zuru zuru da ita,abinci ma sai daga gida ake kawo musu ai kuwa ta Sha Allurai shine samun saukinta ma.
Iman yini tayi a kwance Bata iya tafiyar kirki sai zuwa yamma da ta Dan ji sauki,mayen Yana gefenta kamar zai cinyeta tace zan danyi tafiya dan Allah ko naji sauki,Annoor ya mike Yana murmushi abinsa shi duniya sabuwa,hannayenta ya rike a hankali ya mikar da ita tsaye harda cewa sama da ikon Allah,dariya ta fara tana dukan damtsensa Shima dariya yake cike shaukin so,ya riketa Yana koya mata tafiya a hankali,Hannu ta yarfe tana cije lips yace daure,ture shi tayi tana murmushi ya fada Saman bed,fadowa tayi kansa tare da sakin Kara,yace sorry tashi aci gaba ya sake riketa suna tafiya a hankali Yana ta faman tsokanarta,yace wai Ina Sunan da kika Sa min na love kin daina fada yanzu,Iman tace ai yanzu ranka ya dade kake wa zai ja da Kai,me gida ran gida baki aka fiku ba aiki ba,kune gaba da mu,yace wash Annoor ka kashe ni,murmushi tayi tace ka daina please,gwara ma ki bar fadi bazan daina ba.
Bangaren Nabeel kuwa shi jinyar Yar matarsa yake sosai kuda baya so ya taba ta,sai bakinta da ya bude sosai tun a ranar surutunta ya baci bata shuru Hidaya,ita first night din kamar an bude mata baki.
Naila ce ta kira Umma ta sanar mata tayi bari,Kubra tace Allah ya sawake ya kiyaye gaba,tace Ina Abba? Zaraf Abba yace gani Ina jinki bari kika yi Ashe to Alhmdllh yafi babu akan ace ko bari bata taba yi ba gwara ace ta taba bari ai Kinga ana sa rai,Naila tace hakane Abba kamar Dan kadangare,Abba yace ke Zubaina sati hudu ai jini ne Ina ya zama kamar kadangare din,Naila tayi dariya tace ai a haka na gane,Abba yace a'a ba da bane gaskiya gudan jini kika gani idonki ya rufe,Kubra tana jinsu Abba yace tunda lafiya kike ai anyi arziki duk wata karya ki ajiye abarki gefe Naila Allah ya baki wani ni kaina na matsu naga kin min jika wlh ki dage tun kafin Dara taci gida na fara miki gori da kaina don kuwa na gaji da Kara da kawaici na kusa fara gori,Naila tayi dariya tace Abba da kanka,to ni dai Kinga na haihu bare ace tunda nayi gori hakki ya kamani bazan haihu ba Nima da yarana,na kusa gajiya zan fara yi muku gori ke da mijinki,Naila tana dariya tace Abba Yana jinka.
Ta zaci Abba kunya zai ji sai yace bashi wayar ma,ta mikawa Spark Dake gefe Yana dariya Yana Jin Abba,ya karba suka gaisa, Abba yace wai Kai aiki ne yayi Maka yawa ne? ya kamata ka dauki hutu ka samu nutsuwa ance rashin hutu ma Yana hana haihuwa,na gaji da halinku ka zauna ka binciki Naila Anya ba wani Abu ta Sha ba Bata San tana da ciki ba ta gantalar da shi,Spark yace to ya mike zai bar wajen Naila ta rike shi Kam tace wlh ban yarda ba a gabana zaka gama wayar Nan ka karo volume,Spark yaki karo Volume tunda ya rage volume sai da ya gama wayarsa sannan ya kwanta abinsa a gefenta Yana tambaya yau tun safe me da me kika ci?Naila tace abincin da Kaci,wato Abba ne yace ka tambaye ni ai na gane ka.
Washe gari Abba ya bude shagonsa na kayan masarufi harda tiles yace saura katifa,takanas ya siyo katifa Yar Siririya ta Yan makaranta ya saka a can gefe kullum Yana Kai ko a zaune ko a kwance kowa in zai wuce Yana kallonsa ai ta sheka dariya shi kuwa ko a jikinsa yace kanku ake ji bazai yuwu Basir ya kashe ni ba akan Ina so gidanku a tuka tuwo sai dai idan kar a siyi Masara ta.
Rafeeq yau Mima yaje gaisarwa ya samu Arham gososo yayi matashi da cinyar Mima,Rafeeq yace Kai mene haka? Arham yace Kai kaje ka hau ta matarka mana ai kana da ita ni ka barni na hau ta Uwata ni wlh Mima da zata ci gaba da shayar Dani tsaf zan koma baya,Mima ya kalla yace Dan Allah ki Sha ruwan kaikayi su kawo,Rafeeq yayi dariya yace to ke Mima kinji danki shi yasa ya Raina ki Kinga irinta,Mima tace Kai dalla rufe min baki sanda muna talaucin mu kazo ne gudun mu kuka dinga yi sai yanzu zaka dame mu,Arham yace ai yayi mata yanzu ya daina lagawu da baki wlh da a baya ne da yanzu ya mana batsa,Dariya Rafeeq yayi yace yanzu kuwa nake batsa yaro kawai dai an daina yi a gaban ku baku da kunnen ji me kunnuwan ji tana gida,Arham yace muna ji mana me zai Hana ai mu muna Jin dadin wannan batu,Mima tashi tayi ta cire takalminta ta Kifa Rafeeq da gudu tana zage zage,Rafeeq ya shige bedroom tace zo ka tafi gidanka wlh,Mummy tana zaune tana faman kallon takadar sammacinta ta kotu,Arham ya kalleta suka hada Ido bakinsa ya danne da hannu Yana faman dariya,Mummy ta kalle shi tace Kai dan Uwarka da wa kake? Yace ba fa dake nake ba ni,wai Ina Alhaji Baseeru ne? Ina ma kin samu ciki abinki,Mummy tace Dan iska shege ba Yana can Dan wahala,kamar ni zanje bikonsa don a San ya za ayi ko wani auren nayi na fito ya sake aurena wai shi a baya ma kaddara ce dama na Masa tsufa Mamansa ce ni,Arham ya boye dariyarsa yace gaskiya bashi da mutunci duk garar da ya kwasa,Mummy tace ai ya manta,Dan Adam butulu cewar Arham,Mima ce ta fito tace kin biyewa Arham kina Hira Yana ta zurma ki wannan yaran akwai na dauka ciki tashi kaima ta fatattaki Arham Shima.
Shaheed ne ya dawo Yana shugowa tace juya kasan Inda dare yayi Maka,me nayi Kuma ni daga dawowata school fa naje,Mima tace kasan Allah wlh zan fadawa Papan ku,ka wuce part dinku kawai bana son magana,Mummy tace yawwa haba yara duk sun addabi mutane,Mima tace wlh ni da zasu samu mata ma duk a musu auren yafi min ai sun Isa,Shaheed ya fara murna Yana Shoky ahh Shoky ai bamu sani ba ni wlh a daura ma data Annabi,ko wace a bata ni sadaka 9mnths sai jikoki ta ko Ina,Junior ne kawai Bai Isa aure ba cewar Mummy,Shaheed yace ku bashi yarinya ku gani a kulle su a daki wlh sai ta haihu,Rafeeq ne ya fito yace daga zuwa gaisuwa ni ku tsaya na fice na tafi ya lallaba ta gefe ya fice,Shaheed ma ya tafi abinsa Yana murna ance za a musu aure.
Hanif Usman Dan asalin Adamawa ne,Fulani ne gaba da baya,tun Yana dan 3yrs Babansa ya rasu sai mahaifiyarsa a gabanta ya taso ya girma ta tsaya Masa yayi makaranta har masters a kalla zai Kai 33yrs,kyakyawan matashi ne na gaske,fari ne amma ba irin Kal Kal ba,Yana da dogon hanci,bakinsa dan daidai ne me kyau,hakoransa masu matukar kyau haka idanuwansa,Yana da yalwar gashi baki wuluk me kyau,shi bai cika tsayi ba Kuma dole a kira shi da dogo,komai na Hanif me kyau ne,haka gashi ko wanne sutura ya saka sai ya zuba kyau ta amshe shi,baida hayaniya sannan ba a fiye fada da shi ba kawai harkarsa yake, har Mamansa ta auri kanin babansa suka yi Yar gida,bayan Alhajin nasa Yana da mata da yaransa biyar amma duk mata ne Kuma duk an musu aure a yanzu suna da yara ma ko wacce.
Hanif tunda ya taso yake da kashin arziki Ya fara aikin gomnati Yana kasuwanci sai kasuwancin nasa yazo ya danne komai,kudin da yake samu har da na hauka ma Allah ya sa Masa Albarka,Yana da kudi matuka sosai,Business dinsa yafi karfi a Kano state a Nan ya kera gida na karshe a GRA Yana zaune shi kadai iyayensa suna Adamawa da dangi,Yana da kadarori sosai matashin me kudi ne.
A Yan uwansu Adamawa akwai wata Khairat wacce Alhaji kanin babansa ke riketa,tun tana karama Hanif yake son Khairat kamar ransa,wacce Kuma a sanadin gobara data kama gidan Umminsa wato gidan kanin babansa tayi ajalin Khairat wacce ya Sha kuka kullum a cikin damuwa yake sabo da ita.
Dalilin zuwansa prison kuwa a cikin Yan uwansa ne bangaren Umminsa mahaifiyarsa ta samu Dan gidan Yayarta wacce ta Dade da rasuwa ana ce Masa Sudeis zai Kai 25yrs ta turo shi Kano wajen Hanif akan zai koya Masa business zai Maida shi yaronsa,kaddara tasa satin Sudeis biyu aka neme shi aka rasa daga fita kasuwa ba a sake ganinsa ba,Hankalin Hanif ya tashi matuka sabo da a gidansa yaron yake zaune Kuma wajensa aka turo shi,dangin uban yaro suka ce baza su yarda ba dama Hanif Dan mafia ne kudin mafia yake da su matsafi ne,iya nema da cigiya an rasa Sudeis,Uban yaro ya Kai Kara bazai yarda Wanda aka kama Hanif aka tsare shi a prison bangaren Wanda ake tuhuma ana sauraron kararsu,Alkalin ma nasu yayi tafiya yaki dawowa shi yasa har yanzu ba a yanke hukunci ba,Yana Nan a ciki shima kamar Mero basu San zaman da suke ba.
Umminsa da Alhaji suna zuwa ko yaushe sannan Hanif abinci me tsada ake kawo Masa kullum,haka sutura da komai nasa classic ne,kana ganinsa kasan babu maganar wahala a tare da shi,shine Kuma Wanda Mero take kallo a TikTok tana sonsa.
Iman yini tayi a kwance Bata iya tafiyar kirki sai zuwa yamma da ta Dan ji sauki,mayen Yana gefenta kamar zai cinyeta tace zan danyi tafiya dan Allah ko naji sauki,Annoor ya mike Yana murmushi abinsa shi duniya sabuwa,hannayenta ya rike a hankali ya mikar da ita tsaye harda cewa sama da ikon Allah,dariya ta fara tana dukan damtsensa Shima dariya yake cike shaukin so,ya riketa Yana koya mata tafiya a hankali,Hannu ta yarfe tana cije lips yace daure,ture shi tayi tana murmushi ya fada Saman bed,fadowa tayi kansa tare da sakin Kara,yace sorry tashi aci gaba ya sake riketa suna tafiya a hankali Yana ta faman tsokanarta,yace wai Ina Sunan da kika Sa min na love kin daina fada yanzu,Iman tace ai yanzu ranka ya dade kake wa zai ja da Kai,me gida ran gida baki aka fiku ba aiki ba,kune gaba da mu,yace wash Annoor ka kashe ni,murmushi tayi tace ka daina please,gwara ma ki bar fadi bazan daina ba.
Bangaren Nabeel kuwa shi jinyar Yar matarsa yake sosai kuda baya so ya taba ta,sai bakinta da ya bude sosai tun a ranar surutunta ya baci bata shuru Hidaya,ita first night din kamar an bude mata baki.
Naila ce ta kira Umma ta sanar mata tayi bari,Kubra tace Allah ya sawake ya kiyaye gaba,tace Ina Abba? Zaraf Abba yace gani Ina jinki bari kika yi Ashe to Alhmdllh yafi babu akan ace ko bari bata taba yi ba gwara ace ta taba bari ai Kinga ana sa rai,Naila tace hakane Abba kamar Dan kadangare,Abba yace ke Zubaina sati hudu ai jini ne Ina ya zama kamar kadangare din,Naila tayi dariya tace ai a haka na gane,Abba yace a'a ba da bane gaskiya gudan jini kika gani idonki ya rufe,Kubra tana jinsu Abba yace tunda lafiya kike ai anyi arziki duk wata karya ki ajiye abarki gefe Naila Allah ya baki wani ni kaina na matsu naga kin min jika wlh ki dage tun kafin Dara taci gida na fara miki gori da kaina don kuwa na gaji da Kara da kawaici na kusa fara gori,Naila tayi dariya tace Abba da kanka,to ni dai Kinga na haihu bare ace tunda nayi gori hakki ya kamani bazan haihu ba Nima da yarana,na kusa gajiya zan fara yi muku gori ke da mijinki,Naila tana dariya tace Abba Yana jinka.
Ta zaci Abba kunya zai ji sai yace bashi wayar ma,ta mikawa Spark Dake gefe Yana dariya Yana Jin Abba,ya karba suka gaisa, Abba yace wai Kai aiki ne yayi Maka yawa ne? ya kamata ka dauki hutu ka samu nutsuwa ance rashin hutu ma Yana hana haihuwa,na gaji da halinku ka zauna ka binciki Naila Anya ba wani Abu ta Sha ba Bata San tana da ciki ba ta gantalar da shi,Spark yace to ya mike zai bar wajen Naila ta rike shi Kam tace wlh ban yarda ba a gabana zaka gama wayar Nan ka karo volume,Spark yaki karo Volume tunda ya rage volume sai da ya gama wayarsa sannan ya kwanta abinsa a gefenta Yana tambaya yau tun safe me da me kika ci?Naila tace abincin da Kaci,wato Abba ne yace ka tambaye ni ai na gane ka.
Washe gari Abba ya bude shagonsa na kayan masarufi harda tiles yace saura katifa,takanas ya siyo katifa Yar Siririya ta Yan makaranta ya saka a can gefe kullum Yana Kai ko a zaune ko a kwance kowa in zai wuce Yana kallonsa ai ta sheka dariya shi kuwa ko a jikinsa yace kanku ake ji bazai yuwu Basir ya kashe ni ba akan Ina so gidanku a tuka tuwo sai dai idan kar a siyi Masara ta.
Rafeeq yau Mima yaje gaisarwa ya samu Arham gososo yayi matashi da cinyar Mima,Rafeeq yace Kai mene haka? Arham yace Kai kaje ka hau ta matarka mana ai kana da ita ni ka barni na hau ta Uwata ni wlh Mima da zata ci gaba da shayar Dani tsaf zan koma baya,Mima ya kalla yace Dan Allah ki Sha ruwan kaikayi su kawo,Rafeeq yayi dariya yace to ke Mima kinji danki shi yasa ya Raina ki Kinga irinta,Mima tace Kai dalla rufe min baki sanda muna talaucin mu kazo ne gudun mu kuka dinga yi sai yanzu zaka dame mu,Arham yace ai yayi mata yanzu ya daina lagawu da baki wlh da a baya ne da yanzu ya mana batsa,Dariya Rafeeq yayi yace yanzu kuwa nake batsa yaro kawai dai an daina yi a gaban ku baku da kunnen ji me kunnuwan ji tana gida,Arham yace muna ji mana me zai Hana ai mu muna Jin dadin wannan batu,Mima tashi tayi ta cire takalminta ta Kifa Rafeeq da gudu tana zage zage,Rafeeq ya shige bedroom tace zo ka tafi gidanka wlh,Mummy tana zaune tana faman kallon takadar sammacinta ta kotu,Arham ya kalleta suka hada Ido bakinsa ya danne da hannu Yana faman dariya,Mummy ta kalle shi tace Kai dan Uwarka da wa kake? Yace ba fa dake nake ba ni,wai Ina Alhaji Baseeru ne? Ina ma kin samu ciki abinki,Mummy tace Dan iska shege ba Yana can Dan wahala,kamar ni zanje bikonsa don a San ya za ayi ko wani auren nayi na fito ya sake aurena wai shi a baya ma kaddara ce dama na Masa tsufa Mamansa ce ni,Arham ya boye dariyarsa yace gaskiya bashi da mutunci duk garar da ya kwasa,Mummy tace ai ya manta,Dan Adam butulu cewar Arham,Mima ce ta fito tace kin biyewa Arham kina Hira Yana ta zurma ki wannan yaran akwai na dauka ciki tashi kaima ta fatattaki Arham Shima.
Shaheed ne ya dawo Yana shugowa tace juya kasan Inda dare yayi Maka,me nayi Kuma ni daga dawowata school fa naje,Mima tace kasan Allah wlh zan fadawa Papan ku,ka wuce part dinku kawai bana son magana,Mummy tace yawwa haba yara duk sun addabi mutane,Mima tace wlh ni da zasu samu mata ma duk a musu auren yafi min ai sun Isa,Shaheed ya fara murna Yana Shoky ahh Shoky ai bamu sani ba ni wlh a daura ma data Annabi,ko wace a bata ni sadaka 9mnths sai jikoki ta ko Ina,Junior ne kawai Bai Isa aure ba cewar Mummy,Shaheed yace ku bashi yarinya ku gani a kulle su a daki wlh sai ta haihu,Rafeeq ne ya fito yace daga zuwa gaisuwa ni ku tsaya na fice na tafi ya lallaba ta gefe ya fice,Shaheed ma ya tafi abinsa Yana murna ance za a musu aure.
Hanif Usman Dan asalin Adamawa ne,Fulani ne gaba da baya,tun Yana dan 3yrs Babansa ya rasu sai mahaifiyarsa a gabanta ya taso ya girma ta tsaya Masa yayi makaranta har masters a kalla zai Kai 33yrs,kyakyawan matashi ne na gaske,fari ne amma ba irin Kal Kal ba,Yana da dogon hanci,bakinsa dan daidai ne me kyau,hakoransa masu matukar kyau haka idanuwansa,Yana da yalwar gashi baki wuluk me kyau,shi bai cika tsayi ba Kuma dole a kira shi da dogo,komai na Hanif me kyau ne,haka gashi ko wanne sutura ya saka sai ya zuba kyau ta amshe shi,baida hayaniya sannan ba a fiye fada da shi ba kawai harkarsa yake, har Mamansa ta auri kanin babansa suka yi Yar gida,bayan Alhajin nasa Yana da mata da yaransa biyar amma duk mata ne Kuma duk an musu aure a yanzu suna da yara ma ko wacce.
Hanif tunda ya taso yake da kashin arziki Ya fara aikin gomnati Yana kasuwanci sai kasuwancin nasa yazo ya danne komai,kudin da yake samu har da na hauka ma Allah ya sa Masa Albarka,Yana da kudi matuka sosai,Business dinsa yafi karfi a Kano state a Nan ya kera gida na karshe a GRA Yana zaune shi kadai iyayensa suna Adamawa da dangi,Yana da kadarori sosai matashin me kudi ne.
A Yan uwansu Adamawa akwai wata Khairat wacce Alhaji kanin babansa ke riketa,tun tana karama Hanif yake son Khairat kamar ransa,wacce Kuma a sanadin gobara data kama gidan Umminsa wato gidan kanin babansa tayi ajalin Khairat wacce ya Sha kuka kullum a cikin damuwa yake sabo da ita.
Dalilin zuwansa prison kuwa a cikin Yan uwansa ne bangaren Umminsa mahaifiyarsa ta samu Dan gidan Yayarta wacce ta Dade da rasuwa ana ce Masa Sudeis zai Kai 25yrs ta turo shi Kano wajen Hanif akan zai koya Masa business zai Maida shi yaronsa,kaddara tasa satin Sudeis biyu aka neme shi aka rasa daga fita kasuwa ba a sake ganinsa ba,Hankalin Hanif ya tashi matuka sabo da a gidansa yaron yake zaune Kuma wajensa aka turo shi,dangin uban yaro suka ce baza su yarda ba dama Hanif Dan mafia ne kudin mafia yake da su matsafi ne,iya nema da cigiya an rasa Sudeis,Uban yaro ya Kai Kara bazai yarda Wanda aka kama Hanif aka tsare shi a prison bangaren Wanda ake tuhuma ana sauraron kararsu,Alkalin ma nasu yayi tafiya yaki dawowa shi yasa har yanzu ba a yanke hukunci ba,Yana Nan a ciki shima kamar Mero basu San zaman da suke ba.
Umminsa da Alhaji suna zuwa ko yaushe sannan Hanif abinci me tsada ake kawo Masa kullum,haka sutura da komai nasa classic ne,kana ganinsa kasan babu maganar wahala a tare da shi,shine Kuma Wanda Mero take kallo a TikTok tana sonsa.