Sashe 72
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ni kam haihuwar ta yi jinkiri don sai na shekara ɗaya da rabi a gidan aure kafin na haifi ɗa na miji santalele da shi, da sati ya gayayo ya ci sunan Abbana ana yi masa alkunya da Abul-khair watansa biyar a duniya aka yi bikin Amir da ya angwance da ƙanwar mijin Anty Zulaihatu mun sha biki don tare wa na yi a gidan Anty Sawwama, haka Yaya Alhassan ya gama fushinsa har ya sauƙo don kansa, a rage saura Umar kawai wanda kullum nake yi masa tsiya da cewar sai mun daina ba shi abinci.
Lokacin auren Muhammad Taufik gayya muka yi muka je mu bikin iyalan Sheikh suka karrama mu matuƙa har muka je muka dawo mu na jinjina halin girma da dattaku irin na su. Na zamo abar alfahari ga mijina iyayen da kuma ƴan uwa har ma da matan cikin unguwan da nake, a ko a kan hanya nake tafiya na ga uwa tana furta munanan furuci ga ɗanta, sai na dakata na sanar da ita illar hakan a wasu lokatan har na kan yanko wani sashi na cikin tarihi don hakan ya sama iznina a gare su. Don tabbas na ishe kowa misali cewar DAFIN HARSHE mussamman na uwa akan ƴaƴanta ya fi dafin maciji illa don shi kassara rayuwa yake yi gabaɗaya. Har gida Saifullah da Muhammad Taufik suka kawo mini matanyensu, Zinariya ma sa ta rikiɗa ta koma sunanta na yanka watau Maryam ta kawo mini mun sha kuka ni da ita, mussamman da ta labarta mini cikin tsananin da ta fuskata da barazana daga wajen Hajiya Babba a yayin da ta yi ƙoƙarin sauya rayuwa, ta ce da ni har hauka sai da ta sa ta yi hauka tuburan har sai an ɗaure ta da mari don in ta bazama ta fice daga cikin gida to fa sai lokacin da Allah ya nufa. Da taimakon Allah da kuma addu'o'i ta sama sauƙi har hankalinta ya dawo jikinta.
Ranar wata juma'a mun dawo daga gidan Anty Sawwama da muka kai mata wuni, ina gaba Yaya Alhassan yana baya yayin da yake riƙe da Abul-khair a hannunsa, na zaro makullin daga cikin jakata na buɗe ƙofar falon muka shiga ciki a nan cikin falon muka yada zango. Na amshi Abul-khair da ya fara bacci na je na kwantar da shi kana na dawo.
Kusa da shi na zauna na tisa shi a gaba ina kallonsa har sai ya yi magana.
"Ke lafiyanki kuwa wannan kallon kamar za ki cinye ni?".
Taƙaitaccen murmushi na saka kafin na ce"kawai ina tunanin da wasu kalamai ya dace na gode wa Allah ne, bisa kyautar da ya yi mini da kuma ni'iman da ya lulluɓe rayuwata da ita".
"Ban gane ba".
"Yaya Alhassan ni da kai mun san cewa ban dace da kai ba, amma duk da hakan ka aure ni ka killace ni a cikin gidanka ka ba ni dukkan kulawan da ya dace. A zamanmu da kai kullum cikin neman sabon hanyan da za kyautata mini kake yi......". Ban ƙarisa ba ya ɗaura ɗan yatsansa a saman leɓena.
"Shit! Ba na son na ji wannan kalmar ta ƙara fito wa daga cikin bakinki. Bari na faɗa miki abin da ban taɓa faɗa miki ba, ni fa daman tun da ran Abba ina sonki a cikin zuciyata kawai na rasa ta yadda zan faɗa miki ne, ban san kuma yadda za ki fahimci maganar ba sa boda lokaci da yarinta a tattare da ke".
Hannunsa da yake saman leɓena na ture"wai daman tun lokacin kake so na?".
Ya ɗage mini giransa"ƙwara kuwa kawai ban faɗa miki ba, amma na san da na faɗa miki da yanzu mun haifi ƴaƴan ya kai dozin biyu". Babu shiri na kai masa duka a kafaɗarsa ya yi saurin zame wa.
"Dozin biyu sai ka ce ka sama akuya". Dariya ya ƙyalƙyale da shi sai da ya tsagaita kana ya ce"to me ye a ciki? Ai duk za mu iya kula da su. In kuma ba za ki iya haifa min ƴaƴa ba sai na je na auro wacce za ta iya". Harara na galla masa wanda ya ke yawan cewa a duk lokacin da na yi masa sai ya tsorita.
Zan yi magana ya katse ni"kin ga mayar da wuƙan wasa nake yi miki, Amatu ke ce wacce nake so kuma ba zan taɓa iya haɗa soyayyarki da na wata mace ba, ina fatan ki kasance matata har a cikin gidan aljanna". Ya ƙare zancen ya na jawo ni jikinsa ya rungume a ƙirjinsa, luf na kwantar da kaina tare da lumshe idanuna. Ya kawo bakinsa daidai kunnena kamar mai raɗa ya ce"Ina sonki matar Alhassan".
"Ina sonka mijin Amatullah".
A hankali ya ke shafa kaina kafin na ji ya É—auke ni cak ya wuce da ni cikin É—aki, na yi luf abina.
Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! A yau Allah ya ba ni ikon kammala wannan littafin mai suna DAFIN HARSHE . Ina roƙon Allah ya yafe mini kuskuren da na yi a cikinsa abubuwan alkhairin da na yi a ciki kuma Allah ya haɗa mu akan ladan. Ina godiya ga masoyana da suka yi jimirin bibibiyar littafin tun daga farko har ƙarshe ba tare da gajiya wa ba, ina godiya Allah ya bar ƙauna. Ga masu buƙatan littafaina, tambaya, ba da shawara ko wani gyara ƙofa a buɗe take, za a iya tuntuɓa ta ta wannan lambar kamar haka 07038908713.
Sai na ji ku.......
Lokacin auren Muhammad Taufik gayya muka yi muka je mu bikin iyalan Sheikh suka karrama mu matuƙa har muka je muka dawo mu na jinjina halin girma da dattaku irin na su. Na zamo abar alfahari ga mijina iyayen da kuma ƴan uwa har ma da matan cikin unguwan da nake, a ko a kan hanya nake tafiya na ga uwa tana furta munanan furuci ga ɗanta, sai na dakata na sanar da ita illar hakan a wasu lokatan har na kan yanko wani sashi na cikin tarihi don hakan ya sama iznina a gare su. Don tabbas na ishe kowa misali cewar DAFIN HARSHE mussamman na uwa akan ƴaƴanta ya fi dafin maciji illa don shi kassara rayuwa yake yi gabaɗaya. Har gida Saifullah da Muhammad Taufik suka kawo mini matanyensu, Zinariya ma sa ta rikiɗa ta koma sunanta na yanka watau Maryam ta kawo mini mun sha kuka ni da ita, mussamman da ta labarta mini cikin tsananin da ta fuskata da barazana daga wajen Hajiya Babba a yayin da ta yi ƙoƙarin sauya rayuwa, ta ce da ni har hauka sai da ta sa ta yi hauka tuburan har sai an ɗaure ta da mari don in ta bazama ta fice daga cikin gida to fa sai lokacin da Allah ya nufa. Da taimakon Allah da kuma addu'o'i ta sama sauƙi har hankalinta ya dawo jikinta.
Ranar wata juma'a mun dawo daga gidan Anty Sawwama da muka kai mata wuni, ina gaba Yaya Alhassan yana baya yayin da yake riƙe da Abul-khair a hannunsa, na zaro makullin daga cikin jakata na buɗe ƙofar falon muka shiga ciki a nan cikin falon muka yada zango. Na amshi Abul-khair da ya fara bacci na je na kwantar da shi kana na dawo.
Kusa da shi na zauna na tisa shi a gaba ina kallonsa har sai ya yi magana.
"Ke lafiyanki kuwa wannan kallon kamar za ki cinye ni?".
Taƙaitaccen murmushi na saka kafin na ce"kawai ina tunanin da wasu kalamai ya dace na gode wa Allah ne, bisa kyautar da ya yi mini da kuma ni'iman da ya lulluɓe rayuwata da ita".
"Ban gane ba".
"Yaya Alhassan ni da kai mun san cewa ban dace da kai ba, amma duk da hakan ka aure ni ka killace ni a cikin gidanka ka ba ni dukkan kulawan da ya dace. A zamanmu da kai kullum cikin neman sabon hanyan da za kyautata mini kake yi......". Ban ƙarisa ba ya ɗaura ɗan yatsansa a saman leɓena.
"Shit! Ba na son na ji wannan kalmar ta ƙara fito wa daga cikin bakinki. Bari na faɗa miki abin da ban taɓa faɗa miki ba, ni fa daman tun da ran Abba ina sonki a cikin zuciyata kawai na rasa ta yadda zan faɗa miki ne, ban san kuma yadda za ki fahimci maganar ba sa boda lokaci da yarinta a tattare da ke".
Hannunsa da yake saman leɓena na ture"wai daman tun lokacin kake so na?".
Ya ɗage mini giransa"ƙwara kuwa kawai ban faɗa miki ba, amma na san da na faɗa miki da yanzu mun haifi ƴaƴan ya kai dozin biyu". Babu shiri na kai masa duka a kafaɗarsa ya yi saurin zame wa.
"Dozin biyu sai ka ce ka sama akuya". Dariya ya ƙyalƙyale da shi sai da ya tsagaita kana ya ce"to me ye a ciki? Ai duk za mu iya kula da su. In kuma ba za ki iya haifa min ƴaƴa ba sai na je na auro wacce za ta iya". Harara na galla masa wanda ya ke yawan cewa a duk lokacin da na yi masa sai ya tsorita.
Zan yi magana ya katse ni"kin ga mayar da wuƙan wasa nake yi miki, Amatu ke ce wacce nake so kuma ba zan taɓa iya haɗa soyayyarki da na wata mace ba, ina fatan ki kasance matata har a cikin gidan aljanna". Ya ƙare zancen ya na jawo ni jikinsa ya rungume a ƙirjinsa, luf na kwantar da kaina tare da lumshe idanuna. Ya kawo bakinsa daidai kunnena kamar mai raɗa ya ce"Ina sonki matar Alhassan".
"Ina sonka mijin Amatullah".
A hankali ya ke shafa kaina kafin na ji ya É—auke ni cak ya wuce da ni cikin É—aki, na yi luf abina.
Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! A yau Allah ya ba ni ikon kammala wannan littafin mai suna DAFIN HARSHE . Ina roƙon Allah ya yafe mini kuskuren da na yi a cikinsa abubuwan alkhairin da na yi a ciki kuma Allah ya haɗa mu akan ladan. Ina godiya ga masoyana da suka yi jimirin bibibiyar littafin tun daga farko har ƙarshe ba tare da gajiya wa ba, ina godiya Allah ya bar ƙauna. Ga masu buƙatan littafaina, tambaya, ba da shawara ko wani gyara ƙofa a buɗe take, za a iya tuntuɓa ta ta wannan lambar kamar haka 07038908713.
Sai na ji ku.......