Sashe 52
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Mu gama cin abincin sai mu yi magana".
Ban iya ce mata komai ba illa jinjina kaina da na yi, haka aka ci gaba da cin abincin sai dai ni kam ina ci ne kawai ba wai don ina jin ɗanɗanon abincin a bisa harshena ba, haka nan ba don ina son cin abincin haka na ci gaba da tuttura abin cin har muka gama ci. Muka tattare wajen tare da Anty Zulaihatu muka wanke kwanukan, na dawo na zauna a ɗaki ina ta tsammanin ko Anty Sawwama za ta aiko a ƙira ni ta ba ni damar fayyace musu komai amma ba ta yi hakan ba, haka muka kwana ba tare da wani ya ce mini ci kanki ba na yanki dare na yi kuka mai tsanani har sai da na ji numfashina yana cushewa waje guda kafin na tsagaita, na tashi na fita na ɗauro alwala na zo na fuskanci alƙibla na tada kabbara. Raka'a biyu na yi a fashe wa Ubangiji da kuka a cikin sujjadata na ƙarshe.
Daren ranar ban iya runtsawa ba hakan ya sa ni washe gari na tashi da wani irin matsanancin zazzaɓi mai dafa jiki. Ina kwance a ɗakin Umar ya shigo ya iske ni a haka ya ruga ya je ya sanar da Anty Sawwama ta zo ta ɗago ni ta ji jikina ya ɗauki zafi gau. Ta sa Umar ya riƙa Yaya Alhassan ya zo shi ta ce ya kai ni asibiti yayin da ta umarce Anty Zulaihatu ta raka ni sa boda a gidan ta kwana, don a daren jiya na ji tana waya da mijinta yana shaida mata yau zai dawo daga tafiyar da ya yi.
Hijabina na saka na tashi tsaye yayin da Anty Zulaihatu ta riƙe mini hannuna sa boda yadda jiri yake ta faman kai ni ƙasa.
"Alhassan idan kun je ayi mata dukkanin gwaje-gwajen da suka kamata". Ciken rashin fahimtar inda zantukan natan suka nufo ya ce"wasu irin gwaje-gwaje ke nan Umma? Na yi tunanin ai zazzaɓi ne kawai".
"A yi mata gwajin dukkanin cututtuka ciki har da na cuta mai karya garkuwan jiki da kuma gwajin ciki".
Take na ji ƙirjina ya buga kwatankwacin irin bugun da maƙeri yake yi wa ƙarfi da dukkan ƙarfinsa. Kalaman Anty Sawwama suka karyar mini da zuciya tare da haifar da wasi-wasi a cikin zuciyata, mamaki ya cika mini raina sai dai na gaza juyowa na kalle ta kamar yadda na kasa ɗaga ƙafana na bar wajen. Sai da Anty Zulaihatu ta ja hannuna muka bar wajen kafin na dawo cikin hayyacina haka muka fita muka nema adaidaita muka shiga zuwa asibitin.
Mu na zuwa aka ƙarbe ni aka yi mini duk wasu gwaje-gwajen da suka dace ciki kuwa har ta waɗanda Anty Sawwama ta lissafa. Tunin magunguna aka rubuta mini cikin har da ƙarin ruwa sun so su ba ni gado Yaya Alhassan ya ce su rubuta mini magani kawai. Haka muka saya magungunan jimgim muka koma gida a yadda muka iske Anty Sawwama ta na ta faman safa da marwa a tsakar gidan ya tabbatar mini da cewar duk da muka fita daga cikin gidan ruhinta bai huta ba hakan nan zuciyanta bai daina saƙa mata abubuwa ba. Sai da muka shiga cikin falo muka zauna sannan Yaya Alhassan ya tabbatar mata da cewar babu ciki a jikina kuma likitoci sun tabbatar da cewar ko cutar sanyi ba na ɗauke da ita balle cuta mai karya garkuwa jiki watau siga.
Silalewa daga kan kujerar da take Anty Sawwama ta yi ta yi sujudul shukur tana gode wa Ubangijnta Sarkin da bai haifa ba kuma ba a haife shi ba. Ta daÉ—e kafin ta É—ago ta koma mazauninta ta yi alama da idon akan na zo kusa da ita na zauna.
Kamar yadda ta buƙata haka na yi na je kusa da ita na zauna na sadda kaina ƙasa yayin da ta riƙo hannayena ta sanya cikin nata ta na murzawa a hankali ta ce"Uwata ɗago idanunki ki kalle ni" a hankali na ɗago idona ina kallon fuskarta da ta washe da annuri.
"Ba wai ina tantama akan tarbiyyanki ba ne amma shin da gaske ne tun da kika saka ƙafa kika fita daga cikin gidan nan ba ki aika wani abun ashsha ba, balle kuma wanda Allah ya haramta aikata sa?". Hawaye suna gudun famfalaƙi a bisa kuncina na furta"wallahi Anty ban aika ko ɗaya daga ciki ba, na kiyaye mutunci da kuma kimar kaina". Daga haka na zarce da ba su lamarin duk abin da ya wakana tun daga ranar farko da na sa ƙafata na fita daga cikin gidan har zuwa lokacin da muka yi ido huɗu da Yaya Alhassan da Amir a ɗakin Hajiya, sai dai na ɓoyeH musu haƙiƙanin gaskiyan abin da ya kai ni otel a cikin wannan daren. Haƙiƙa na ga zallan tausayawa kwance a cikin idanunsu yayin da Anty Zulaihatu da Umar suka zubar mini da hawaye tausayi sosai, Amir da Yaya Alhassan kuwa duk jikkunansu ya yi sanyi ƙalau tamkar kazar da aka jefa da ruwan gishiri. Anty Sawwama kuwa baƙinta ya ƙi rufewa sai godiya take ta faman jeranta wa Allah na yi ta ƙara gode masa, tare da addu'ar Allah ya ba ta ikon kulawa da rayuwata daga yanzu har zuwa fitar numfashinta na ƙarshe.
"Ga Amatullah nan na ba ku amanarta da ragamar kula da ita duk wani a cikin ku da yake son faranta min, to ya faranta mata. Haka zalika duk wani da yake
son ganin ɓacin raina to ya musguna mat yy yh h yh hmy a, ko bayan raina ban yarda ku wulaƙanta ba ko kuma ku bari ta yi kukan maraincin mahaifinta". Jikinmu gabaɗaya ya kuma yin sanyi na kwantar da kaina a bisa cinyar Anty Sawwama ina faɗin"Anty ina Ummata tun da na zo babu wanda ya yi mini maganarta, ina so na je na gan ta ita ma na nema yafiyarta".
"Ummanki tana nan Amatullah. Kuma sa boda ita ne ma ya sa muka saya kai da fata wajen ganin mun dawo da ke gida". Babu shiri na ɗago kaina ina kallonta"sa boda ita kuma? Wani abun ne ya faru da ita?". Ganin yadda na birkice ya sanya ta sanyaya muryarta tana faɗin"ki kwantar da hankalinki babu abin da ya faru da ita. Za kuma ki je ki gan ta a yau ba sai gobe ba". Kaina kawai na yi ƙarfin halin gyaɗa mata don jikina ya gama ba ni tabbacin cewa akwai wani abu a ƙasa.
Muna yin sallan asubahi ko abincin ban tsaya ci ba muka nufi gidan ni da Anty Zulaihatu har izuwa lokacin ƙirjina bai daina harbawa haka yana dakan lugudan-lugudan tara-tara. Muna sauƙa a ƙofan gidan na ji wasu tulin hawaye sun ciko mini idanuna rayuwata ta baya ya soma dawo mjni cikin kwanyata, yayin da wani haske ya ratsa idanuna tamkar majigin da yake hasko mini jiya ta zuwa yau. Babu abin da na fi tuna illa lokacin zaman makokin Abba yadda aka cika a ƙofar gidan. Sai da ta riƙo hannuna muka shiga cikin gidan yayin da yaran gidan da na maƙwabta suna cika a kaina suka mamaye ni kowa burinsa ya ɗaura hannunsa a jikina don kawai ya tabbatar da cewa ni ɗin ce na dawo ba wata ba.
Muna shiga filin tsakar gidan da Umman Amira na fara cin karo ta saki kwanon wainar da yake hannunta ya faɗi ƙasa.
"Amatullah ke ce? Jama'a ku fito ku fito ga Amatullahi ta dawo gida. Allah alhamdulillah". Ta yi zancen cikin ɗaga murya yayin da take rugowa da gudu ta zo ta ƙanƙame ni ƙam a jikinta. Kamar an kaɗa ƙararrawa haka ragowar matan gidan suka soma fitowa ƙwansu da ƙwarƙwatansu.
"Allah buwayi gagara misali. Amatullah ke ce tsaye a gabanmu? Ko da yake daman masu iya magana ai sun ce giji lahira ce". Maman Adnan da na gan ta da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe a jikinta, kaina kawai na jinjina cikin ƙarfin hali na kallo Umman Amira na ce"ina Ummata take?".
Ta yi mini nuni da hanyar ɗakinmu"tana cikin ɗakin". Da gudu na nufi ɗakin ina ƙwalla mata ƙira cikin muryata da ta gama dushashewa sa boda kukan da na ɗauki tsawon lokaci ina yin sa, turus na yi na tsaya lokacin da na yi ido huɗu da ita yashe a falon a bisa kan tabarma na bi ta da kallon tsaf yayin da ƙirjina yake buga wa kamar zai bayyano waje.
Daga ita sai zani ɗaurin ƙirji a jikinta sai kuma wani ɗan ƙyallen da ta lulluɓe kanta da shi, ƙafafunta na yi da kallo da wani wari da ɗoyi yake tashi daga gare su, ƙafarta ɗaya na ga an yanke har zuwa gwiwar ƙafar yayin da ɗayar kuma ta kumbura ta yi tsimtim kamar za ta fashe.
"Um-um-um-umma ke ce haka me ye ya same ƙafafunki?". Na furta zancen cikin tsintsinkewar zance numfashina yana sama yana ƙasa tamkar ceron da yake bugan sa a cikin turmi. Ta kasa cewa da ni komai illa kallon da ta kafe ni da shi hawaye suna tsiyaya a bisa baƙin fuskarta da ta yi duhun gaske tamkar bayan tukunya, ta ƙanjame kamar mai cutar ƙanjamau duk ta lalace kamar kamun mayu. Na duƙufa a gefenta ina kuka yayin da ita ma take taya ni babu ji babu gani kamar waɗannan aka yi wa mutuwar ƙare dangi.
[12/20, 1:48 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page 7ï¸âƒ£4ï¸âƒ£
Ban iya ce mata komai ba illa jinjina kaina da na yi, haka aka ci gaba da cin abincin sai dai ni kam ina ci ne kawai ba wai don ina jin ɗanɗanon abincin a bisa harshena ba, haka nan ba don ina son cin abincin haka na ci gaba da tuttura abin cin har muka gama ci. Muka tattare wajen tare da Anty Zulaihatu muka wanke kwanukan, na dawo na zauna a ɗaki ina ta tsammanin ko Anty Sawwama za ta aiko a ƙira ni ta ba ni damar fayyace musu komai amma ba ta yi hakan ba, haka muka kwana ba tare da wani ya ce mini ci kanki ba na yanki dare na yi kuka mai tsanani har sai da na ji numfashina yana cushewa waje guda kafin na tsagaita, na tashi na fita na ɗauro alwala na zo na fuskanci alƙibla na tada kabbara. Raka'a biyu na yi a fashe wa Ubangiji da kuka a cikin sujjadata na ƙarshe.
Daren ranar ban iya runtsawa ba hakan ya sa ni washe gari na tashi da wani irin matsanancin zazzaɓi mai dafa jiki. Ina kwance a ɗakin Umar ya shigo ya iske ni a haka ya ruga ya je ya sanar da Anty Sawwama ta zo ta ɗago ni ta ji jikina ya ɗauki zafi gau. Ta sa Umar ya riƙa Yaya Alhassan ya zo shi ta ce ya kai ni asibiti yayin da ta umarce Anty Zulaihatu ta raka ni sa boda a gidan ta kwana, don a daren jiya na ji tana waya da mijinta yana shaida mata yau zai dawo daga tafiyar da ya yi.
Hijabina na saka na tashi tsaye yayin da Anty Zulaihatu ta riƙe mini hannuna sa boda yadda jiri yake ta faman kai ni ƙasa.
"Alhassan idan kun je ayi mata dukkanin gwaje-gwajen da suka kamata". Ciken rashin fahimtar inda zantukan natan suka nufo ya ce"wasu irin gwaje-gwaje ke nan Umma? Na yi tunanin ai zazzaɓi ne kawai".
"A yi mata gwajin dukkanin cututtuka ciki har da na cuta mai karya garkuwan jiki da kuma gwajin ciki".
Take na ji ƙirjina ya buga kwatankwacin irin bugun da maƙeri yake yi wa ƙarfi da dukkan ƙarfinsa. Kalaman Anty Sawwama suka karyar mini da zuciya tare da haifar da wasi-wasi a cikin zuciyata, mamaki ya cika mini raina sai dai na gaza juyowa na kalle ta kamar yadda na kasa ɗaga ƙafana na bar wajen. Sai da Anty Zulaihatu ta ja hannuna muka bar wajen kafin na dawo cikin hayyacina haka muka fita muka nema adaidaita muka shiga zuwa asibitin.
Mu na zuwa aka ƙarbe ni aka yi mini duk wasu gwaje-gwajen da suka dace ciki kuwa har ta waɗanda Anty Sawwama ta lissafa. Tunin magunguna aka rubuta mini cikin har da ƙarin ruwa sun so su ba ni gado Yaya Alhassan ya ce su rubuta mini magani kawai. Haka muka saya magungunan jimgim muka koma gida a yadda muka iske Anty Sawwama ta na ta faman safa da marwa a tsakar gidan ya tabbatar mini da cewar duk da muka fita daga cikin gidan ruhinta bai huta ba hakan nan zuciyanta bai daina saƙa mata abubuwa ba. Sai da muka shiga cikin falo muka zauna sannan Yaya Alhassan ya tabbatar mata da cewar babu ciki a jikina kuma likitoci sun tabbatar da cewar ko cutar sanyi ba na ɗauke da ita balle cuta mai karya garkuwa jiki watau siga.
Silalewa daga kan kujerar da take Anty Sawwama ta yi ta yi sujudul shukur tana gode wa Ubangijnta Sarkin da bai haifa ba kuma ba a haife shi ba. Ta daÉ—e kafin ta É—ago ta koma mazauninta ta yi alama da idon akan na zo kusa da ita na zauna.
Kamar yadda ta buƙata haka na yi na je kusa da ita na zauna na sadda kaina ƙasa yayin da ta riƙo hannayena ta sanya cikin nata ta na murzawa a hankali ta ce"Uwata ɗago idanunki ki kalle ni" a hankali na ɗago idona ina kallon fuskarta da ta washe da annuri.
"Ba wai ina tantama akan tarbiyyanki ba ne amma shin da gaske ne tun da kika saka ƙafa kika fita daga cikin gidan nan ba ki aika wani abun ashsha ba, balle kuma wanda Allah ya haramta aikata sa?". Hawaye suna gudun famfalaƙi a bisa kuncina na furta"wallahi Anty ban aika ko ɗaya daga ciki ba, na kiyaye mutunci da kuma kimar kaina". Daga haka na zarce da ba su lamarin duk abin da ya wakana tun daga ranar farko da na sa ƙafata na fita daga cikin gidan har zuwa lokacin da muka yi ido huɗu da Yaya Alhassan da Amir a ɗakin Hajiya, sai dai na ɓoyeH musu haƙiƙanin gaskiyan abin da ya kai ni otel a cikin wannan daren. Haƙiƙa na ga zallan tausayawa kwance a cikin idanunsu yayin da Anty Zulaihatu da Umar suka zubar mini da hawaye tausayi sosai, Amir da Yaya Alhassan kuwa duk jikkunansu ya yi sanyi ƙalau tamkar kazar da aka jefa da ruwan gishiri. Anty Sawwama kuwa baƙinta ya ƙi rufewa sai godiya take ta faman jeranta wa Allah na yi ta ƙara gode masa, tare da addu'ar Allah ya ba ta ikon kulawa da rayuwata daga yanzu har zuwa fitar numfashinta na ƙarshe.
"Ga Amatullah nan na ba ku amanarta da ragamar kula da ita duk wani a cikin ku da yake son faranta min, to ya faranta mata. Haka zalika duk wani da yake
son ganin ɓacin raina to ya musguna mat yy yh h yh hmy a, ko bayan raina ban yarda ku wulaƙanta ba ko kuma ku bari ta yi kukan maraincin mahaifinta". Jikinmu gabaɗaya ya kuma yin sanyi na kwantar da kaina a bisa cinyar Anty Sawwama ina faɗin"Anty ina Ummata tun da na zo babu wanda ya yi mini maganarta, ina so na je na gan ta ita ma na nema yafiyarta".
"Ummanki tana nan Amatullah. Kuma sa boda ita ne ma ya sa muka saya kai da fata wajen ganin mun dawo da ke gida". Babu shiri na ɗago kaina ina kallonta"sa boda ita kuma? Wani abun ne ya faru da ita?". Ganin yadda na birkice ya sanya ta sanyaya muryarta tana faɗin"ki kwantar da hankalinki babu abin da ya faru da ita. Za kuma ki je ki gan ta a yau ba sai gobe ba". Kaina kawai na yi ƙarfin halin gyaɗa mata don jikina ya gama ba ni tabbacin cewa akwai wani abu a ƙasa.
Muna yin sallan asubahi ko abincin ban tsaya ci ba muka nufi gidan ni da Anty Zulaihatu har izuwa lokacin ƙirjina bai daina harbawa haka yana dakan lugudan-lugudan tara-tara. Muna sauƙa a ƙofan gidan na ji wasu tulin hawaye sun ciko mini idanuna rayuwata ta baya ya soma dawo mjni cikin kwanyata, yayin da wani haske ya ratsa idanuna tamkar majigin da yake hasko mini jiya ta zuwa yau. Babu abin da na fi tuna illa lokacin zaman makokin Abba yadda aka cika a ƙofar gidan. Sai da ta riƙo hannuna muka shiga cikin gidan yayin da yaran gidan da na maƙwabta suna cika a kaina suka mamaye ni kowa burinsa ya ɗaura hannunsa a jikina don kawai ya tabbatar da cewa ni ɗin ce na dawo ba wata ba.
Muna shiga filin tsakar gidan da Umman Amira na fara cin karo ta saki kwanon wainar da yake hannunta ya faɗi ƙasa.
"Amatullah ke ce? Jama'a ku fito ku fito ga Amatullahi ta dawo gida. Allah alhamdulillah". Ta yi zancen cikin ɗaga murya yayin da take rugowa da gudu ta zo ta ƙanƙame ni ƙam a jikinta. Kamar an kaɗa ƙararrawa haka ragowar matan gidan suka soma fitowa ƙwansu da ƙwarƙwatansu.
"Allah buwayi gagara misali. Amatullah ke ce tsaye a gabanmu? Ko da yake daman masu iya magana ai sun ce giji lahira ce". Maman Adnan da na gan ta da tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe a jikinta, kaina kawai na jinjina cikin ƙarfin hali na kallo Umman Amira na ce"ina Ummata take?".
Ta yi mini nuni da hanyar ɗakinmu"tana cikin ɗakin". Da gudu na nufi ɗakin ina ƙwalla mata ƙira cikin muryata da ta gama dushashewa sa boda kukan da na ɗauki tsawon lokaci ina yin sa, turus na yi na tsaya lokacin da na yi ido huɗu da ita yashe a falon a bisa kan tabarma na bi ta da kallon tsaf yayin da ƙirjina yake buga wa kamar zai bayyano waje.
Daga ita sai zani ɗaurin ƙirji a jikinta sai kuma wani ɗan ƙyallen da ta lulluɓe kanta da shi, ƙafafunta na yi da kallo da wani wari da ɗoyi yake tashi daga gare su, ƙafarta ɗaya na ga an yanke har zuwa gwiwar ƙafar yayin da ɗayar kuma ta kumbura ta yi tsimtim kamar za ta fashe.
"Um-um-um-umma ke ce haka me ye ya same ƙafafunki?". Na furta zancen cikin tsintsinkewar zance numfashina yana sama yana ƙasa tamkar ceron da yake bugan sa a cikin turmi. Ta kasa cewa da ni komai illa kallon da ta kafe ni da shi hawaye suna tsiyaya a bisa baƙin fuskarta da ta yi duhun gaske tamkar bayan tukunya, ta ƙanjame kamar mai cutar ƙanjamau duk ta lalace kamar kamun mayu. Na duƙufa a gefenta ina kuka yayin da ita ma take taya ni babu ji babu gani kamar waɗannan aka yi wa mutuwar ƙare dangi.
[12/20, 1:48 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________
Page 7ï¸âƒ£4ï¸âƒ£