Sashe 42
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da ya yarce hawaye da suke tsare-tsare a kuncina kana na ce"e Baba duk abin da ka ji haka yake, zaman kaina nake yi a garin nan sannan a cikin gidan karuwai nake rayuwata". Ina gama faɗin haka na fice daga cikin gida fita irin wacce ba na fatan ko a cikin mafarki na dawo, fita irin wacce babu waiwaye har abada balle dawowa. Fita ita wacce take datse ko wani irin alaƙa da mu'amalar da aka ƙulla komai ƙarko da daɗewansa.
Sai da na yi nisa na nema ƙasan wani bishiya na zauna na ci kuka na yi kuka na zubda ƙwalla tamkar raina zai fita. Komai ya fita daga cikin kaina na rasa inda zan nufa na ji daɗi da sanyi a cikin raina. Duniyar da abubuwan da suke cikinta gabaɗayansu suka daina burge ni balle su ba ni sha'awa. Ba don ilmin addini da nake da shi wanda ya yi matuƙar tasiri a gare ni har yake bayyana kansa cikin aikina ba, da kuma hukunci da azabar da na san Ubangiji ya tanada ga duk Bawan da ya kashe kansa ba da babu abin da hana ni shan guba ko kuma na rataye kaina, na huta ba.
Zafin ranar da yake duka na shi ya tursasa mini tashi daga wajen ba domin na gaji da kukan da nake yi É—in ba. A tashi na ci gaba da tafiya ina tafe ina haÉ—a hanya tamkar Æ´ar mayen ta sha abubuwan gusar da hankali ta bugu ta yi tatil.
Ikon Allah ne kawai ya kawo ni gida ba domin na san inda kaina yake ba, balle ina nake cilla ƙafata a buɗe na tarar da ƙofar ɗakin da hakan ya tabbatar mini da cewar Sha'awanatu tana ciki, ina shiga na gan ta zaune tana latsa waya ta kuna kiɗa tamkar za ta ɗaga ɗakin, mu na haɗa ido da ita ta kashe kiɗa ta soma bi na da kallo har na je kwanta akan tabarmata. Na dafe kaina ina ta murtsukuku sa boda tsananin azabar ciwon kan da ya rufe ni lokaci guda ko buɗe idona ba na ƙaunar yi balle na ga haske, ina jin Sha'awanatu na tambayata ko lafiya na yi banza da ita ba tare da na tanka mata ba har ta yi ta gaji ta koma ta ci gaba da harkokinta.
A daddafe na fito na yi alwala na koma ciki na gabatar da sallan zuhur ina shafa addu'ar da na yi na tsinkayo muryar Zinariya ta na faman ɗura ashariya a tsakar gidan, wanda ban zan da wanda take yi ba. Na yi wuf na tashi na fito daidai lokacin da ta buɗe ƙofar ɗakinta ta shiga na bi bayanta, ta waigo tana kallona.
"Har kin dawo ke nan yau da wuri haka?". Maimakon na ba ta amsa sai kawai na tuntsire da kuka har jikina yana rawa. Ta saki ledodin siyayyar da ta yi a kasuwa suka faɗi ƙasa ta riƙo hannuna muka zauna.
"Kukan me ye kike yi Amatullah? Sanar da ni abin da yake faruwa?".
Ban yi ƙasa a gwiwa ba na kwashe duk abin da ya faru na sanar da ita. Sai dai ban fayyace mata cewar Hajiya Muhibbat ita ce matar Saddam wanda take yi wa take da Oganta ba.
"Kan bala'i bura uban can. Yau ina ga ni wani zallan rainin wayo da ɗiban albarka. Kuma ke sai kika tsaya kika zuba musu ido su na jifanki da waɗannan kalaman? Ai fito na fito za ki yi da su ki nuna musu ainihin kalar taki salon barikin. Na rantse sai na dira a cikin gidan matar nan tamkar sauƙar aradu na yi wasan kura da ita sai na nuna mata cewar lalle da ruwa ake dafa shayi kuma bakin rijiya bai kasance wajen wasan makaho ba, tashi mu je ki kai ni gidan". Ta yi zancen yayin da take miƙe wa tsaye.
"A'a Zinariya ba za a yi haka na ƙudurce a cikin raina cewar ba zan ƙara wuce wa ko da ta ƙofar gidan ba ne balle na shiga cikinsa. Na ri ga na yi musu bayannin komai".
A kufule ta ce"waya gaya miki yanzu bayani yana tasiri ga mutane? Ai duk yadda kika ƙware wajen iya tsara kalaman da gogewarki wajen furta su daki-daki, wasu mutanen ba sa fahimta sai kin haɗa musu da akuyanci a cikin lamarin. Ki yi wa girman Allah ki tashi mu je gidan matar nan na ƙaddamar mata".
Na tashi tsayi na riƙo hannunta"don Allah ki taushi zuciyarki ki yayyafa mata ruwan sanyi, mu bar maganar nan ta wuce. Na sanar da ke kawai don na ji sanyi a ciki raina ba don wani abun ba". Ba ta ce da ni komai ba illa zare hannunta da ta yi daga cikin na wa ta koma mazauninta ta zauna, ta yi ƙwafa kana ta ce"billahillazi don kawai zan yi tafiya ne shi yasa zan lafa bayan hakan ban dalilin da za ki ce kin bar wannan maganar ba".
Na sauƙe tagwayen ajiyar zuciya tare da faɗin"gobe za ki tafi Abujan ko?".
"Da sassafe ma kuma Ogana kuma jibi da yamma zai diro najeriya, a ƙalla za mu iya yin sati guda tare".
Na waro idanuna waje"kika ce hutun ƙarshen mako kawai za ku yi tare ki dawo?".
Ta yi fari da idanunta"e amma yanzu lissafin ta sauya kai tsaye ba zan iya ce miki ga ranar dawowa ta ba, sai dai ranar da Allah ya nufa kawai za ki ganni. Zan bar miki makulin ɗakina akwai ragowar kayan abinci ki yi amfani da su. Sannan don Allah ina son kafin na dawo ki sauya daga wannan Amatullah ɗin da take zaune a gabana yanzu, ina son duk wanda ya ɗaga miki ƴatsa ki tabbatar kafin ya sauƙe ta kin karya ɗan tsayan, kin ga harkar bariki fa babu wanda zai zo don ya taimake, ya kawo miki agaji ko kuma ya ƙwata miki haƙƙinki. Yaƙi ne da babu wanda zai tallafa miki ke za ki tashi ki yi wa kanki yaƙin neman ƴancin kai".
"In sha Allah ba zan dawwama a haka ba ni ma, dole akwai lokaci ya na zuwa wanda zan sauya".
Ta murmusawa"yauwa Æ´ar gari yanzu na ji batu". Daga haka ta É—auki ledodin siyayyar da ta yi ta soma nuna mini, magungunan mata ne da na matsi birjik iya ganin mai gani. Daga na turare sai na tsuguna da na sha da kuma na ci da kaza. Ta sayo mini wasu dogayen riguna da mayafai ta ba ni, bakina har kunne na din ga doka mata godiya tamkar zan yi aron baki.
A nan ɗakinta na yi sallan isha'i muka ci abinci, ita take gulmata mini cewar Hajiya Babba ta tura La'aniyatu can ƙasar nijer wajen wata aminiyarta don a ba ta horo a kuma koyar da ita kwasa-kwasan bariki don a cewarta so take yi ta gaje ta ta ɗaura daga inda ta ja birki. Ba kaɗan ba lamarin ya taɓa ni tausayin La'aniyatu ya mamaye zuciyata ni shaida ce akan cewar ba ta ƙaunar irin rayuwar da mahaifiyata take yi, balle daidai da rana guda ta ji sha'awarsa a cikin ranta.
Ba ni na baro ɗakin Zinariya ba sai ƙarfe sha ɗaya dare, lokacin ta gama haɗa kayanta tsaf domin tafiyar gobe. Ta rako ni har ƙofar ɗakinmu muka yi sallama don ta tabbatar mini da cewar ƙarfe ukun dare za a zo ɗaukarta za su wuce garin Kano inda daga nan za ta kai jirgin safe da zai tashi daga cikin filin tashin jiragen sama na cikin jihar Kano zuwa garin Abuja, ta ɗauki makulin ɗakin ta damƙa mini na yi mata fatan sauƙa lafiya kana na shige ɗakin.
Washe gari da ƙyar na tashi sa boda daren jiya ban iya runtsawa da wuri, a makare na gabatar da sallan asubahi na zauna inda na yi sallan na yi shuru ina tunanin ta yadda ta fara gudanar da rayuwata a wannan gaɓar, sai dai kamar yadda Zinariya ta faɗa ne dole na tashi na yi yaƙin nema wa kaina ƴancin kai. Haka kuwa haka ba ta cika sati guda da tafiya ba sai da na zama babu wanda bai
sanni ba a kaf cikin gidan, hatta baƙin da suke zuwa san sunana ko da kuwa ba su taɓa ganin fuskata ba.
Na yi ƙaurin suna fiye da tunanin mai tunani ta yadda duk wani rashin mutunci da tijara na san farillai da sunnoninsu, har na kai munzalin da babu wanda yake rayuwa a cikin gidan da za a ƙira sunana ba tare da ya sha jinin jikinsa. Babu wanda ya isa ya nuna mini ɗan ƴatsa rashin mutuncin da nake yi ina sa yaƙinin ko Zinariya ce ta dawo ba za ta yi rabinsa.
Faɗa da jagwal babu wanda ba na shiga, rigima kuwa ko ba da ni ake yi ba zan shiga na amshe balle kuma da ni ake yi. Yo wani ma ya yi rawa balle ɗan makiɗi. Duk tijara da kwashe-kwashen Aminu sai da ya zubar da makamansa ya duƙa a gabana ya sara mini.
Har na kai lokacin da duk sa'ilin da aka kawo wata sabuwar yarinyar cikin gida waje na ake fara kawo ta na yi mata darasi. Sai dai duk barikin da nake bugawa babu wani na mijin da nake sake wa fuska balle na ba shi gangar jikina, haka nan duk shagalata ba na wasa da addini ko kaɗan du abin nake yi kuma a duk inda nake da na ji an yi ƙiran sallan zan bar abin da nake yi salla, haka nan azumin Litinin da alhamis ba ya taɓa wuce ni. Hakan nan ba a yin cikakkun kwanaki goma sha biyar ba tare da na sauƙe alƙur'ani ba, sadaka kuwa sai dai in ban sama taro da sisi ba.
Wasa-wasa sai da Zinariya ta ci satikai biyar cur ba ta dawo ba, tun abin ba ya damu na har ya soma damuna. A duk lokacin da zan ce Aminu ya ƙira mini layinta a kashe yake lamarin ya yi matuƙar ɗaga mini hankali da jefa ni cikin cakwakiyar tunanin an ya kuwa lafiya?.
[12/14, 12:30 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________________
Page 6ï¸âƒ£9ï¸âƒ£
Sai da na yi nisa na nema ƙasan wani bishiya na zauna na ci kuka na yi kuka na zubda ƙwalla tamkar raina zai fita. Komai ya fita daga cikin kaina na rasa inda zan nufa na ji daɗi da sanyi a cikin raina. Duniyar da abubuwan da suke cikinta gabaɗayansu suka daina burge ni balle su ba ni sha'awa. Ba don ilmin addini da nake da shi wanda ya yi matuƙar tasiri a gare ni har yake bayyana kansa cikin aikina ba, da kuma hukunci da azabar da na san Ubangiji ya tanada ga duk Bawan da ya kashe kansa ba da babu abin da hana ni shan guba ko kuma na rataye kaina, na huta ba.
Zafin ranar da yake duka na shi ya tursasa mini tashi daga wajen ba domin na gaji da kukan da nake yi É—in ba. A tashi na ci gaba da tafiya ina tafe ina haÉ—a hanya tamkar Æ´ar mayen ta sha abubuwan gusar da hankali ta bugu ta yi tatil.
Ikon Allah ne kawai ya kawo ni gida ba domin na san inda kaina yake ba, balle ina nake cilla ƙafata a buɗe na tarar da ƙofar ɗakin da hakan ya tabbatar mini da cewar Sha'awanatu tana ciki, ina shiga na gan ta zaune tana latsa waya ta kuna kiɗa tamkar za ta ɗaga ɗakin, mu na haɗa ido da ita ta kashe kiɗa ta soma bi na da kallo har na je kwanta akan tabarmata. Na dafe kaina ina ta murtsukuku sa boda tsananin azabar ciwon kan da ya rufe ni lokaci guda ko buɗe idona ba na ƙaunar yi balle na ga haske, ina jin Sha'awanatu na tambayata ko lafiya na yi banza da ita ba tare da na tanka mata ba har ta yi ta gaji ta koma ta ci gaba da harkokinta.
A daddafe na fito na yi alwala na koma ciki na gabatar da sallan zuhur ina shafa addu'ar da na yi na tsinkayo muryar Zinariya ta na faman ɗura ashariya a tsakar gidan, wanda ban zan da wanda take yi ba. Na yi wuf na tashi na fito daidai lokacin da ta buɗe ƙofar ɗakinta ta shiga na bi bayanta, ta waigo tana kallona.
"Har kin dawo ke nan yau da wuri haka?". Maimakon na ba ta amsa sai kawai na tuntsire da kuka har jikina yana rawa. Ta saki ledodin siyayyar da ta yi a kasuwa suka faɗi ƙasa ta riƙo hannuna muka zauna.
"Kukan me ye kike yi Amatullah? Sanar da ni abin da yake faruwa?".
Ban yi ƙasa a gwiwa ba na kwashe duk abin da ya faru na sanar da ita. Sai dai ban fayyace mata cewar Hajiya Muhibbat ita ce matar Saddam wanda take yi wa take da Oganta ba.
"Kan bala'i bura uban can. Yau ina ga ni wani zallan rainin wayo da ɗiban albarka. Kuma ke sai kika tsaya kika zuba musu ido su na jifanki da waɗannan kalaman? Ai fito na fito za ki yi da su ki nuna musu ainihin kalar taki salon barikin. Na rantse sai na dira a cikin gidan matar nan tamkar sauƙar aradu na yi wasan kura da ita sai na nuna mata cewar lalle da ruwa ake dafa shayi kuma bakin rijiya bai kasance wajen wasan makaho ba, tashi mu je ki kai ni gidan". Ta yi zancen yayin da take miƙe wa tsaye.
"A'a Zinariya ba za a yi haka na ƙudurce a cikin raina cewar ba zan ƙara wuce wa ko da ta ƙofar gidan ba ne balle na shiga cikinsa. Na ri ga na yi musu bayannin komai".
A kufule ta ce"waya gaya miki yanzu bayani yana tasiri ga mutane? Ai duk yadda kika ƙware wajen iya tsara kalaman da gogewarki wajen furta su daki-daki, wasu mutanen ba sa fahimta sai kin haɗa musu da akuyanci a cikin lamarin. Ki yi wa girman Allah ki tashi mu je gidan matar nan na ƙaddamar mata".
Na tashi tsayi na riƙo hannunta"don Allah ki taushi zuciyarki ki yayyafa mata ruwan sanyi, mu bar maganar nan ta wuce. Na sanar da ke kawai don na ji sanyi a ciki raina ba don wani abun ba". Ba ta ce da ni komai ba illa zare hannunta da ta yi daga cikin na wa ta koma mazauninta ta zauna, ta yi ƙwafa kana ta ce"billahillazi don kawai zan yi tafiya ne shi yasa zan lafa bayan hakan ban dalilin da za ki ce kin bar wannan maganar ba".
Na sauƙe tagwayen ajiyar zuciya tare da faɗin"gobe za ki tafi Abujan ko?".
"Da sassafe ma kuma Ogana kuma jibi da yamma zai diro najeriya, a ƙalla za mu iya yin sati guda tare".
Na waro idanuna waje"kika ce hutun ƙarshen mako kawai za ku yi tare ki dawo?".
Ta yi fari da idanunta"e amma yanzu lissafin ta sauya kai tsaye ba zan iya ce miki ga ranar dawowa ta ba, sai dai ranar da Allah ya nufa kawai za ki ganni. Zan bar miki makulin ɗakina akwai ragowar kayan abinci ki yi amfani da su. Sannan don Allah ina son kafin na dawo ki sauya daga wannan Amatullah ɗin da take zaune a gabana yanzu, ina son duk wanda ya ɗaga miki ƴatsa ki tabbatar kafin ya sauƙe ta kin karya ɗan tsayan, kin ga harkar bariki fa babu wanda zai zo don ya taimake, ya kawo miki agaji ko kuma ya ƙwata miki haƙƙinki. Yaƙi ne da babu wanda zai tallafa miki ke za ki tashi ki yi wa kanki yaƙin neman ƴancin kai".
"In sha Allah ba zan dawwama a haka ba ni ma, dole akwai lokaci ya na zuwa wanda zan sauya".
Ta murmusawa"yauwa Æ´ar gari yanzu na ji batu". Daga haka ta É—auki ledodin siyayyar da ta yi ta soma nuna mini, magungunan mata ne da na matsi birjik iya ganin mai gani. Daga na turare sai na tsuguna da na sha da kuma na ci da kaza. Ta sayo mini wasu dogayen riguna da mayafai ta ba ni, bakina har kunne na din ga doka mata godiya tamkar zan yi aron baki.
A nan ɗakinta na yi sallan isha'i muka ci abinci, ita take gulmata mini cewar Hajiya Babba ta tura La'aniyatu can ƙasar nijer wajen wata aminiyarta don a ba ta horo a kuma koyar da ita kwasa-kwasan bariki don a cewarta so take yi ta gaje ta ta ɗaura daga inda ta ja birki. Ba kaɗan ba lamarin ya taɓa ni tausayin La'aniyatu ya mamaye zuciyata ni shaida ce akan cewar ba ta ƙaunar irin rayuwar da mahaifiyata take yi, balle daidai da rana guda ta ji sha'awarsa a cikin ranta.
Ba ni na baro ɗakin Zinariya ba sai ƙarfe sha ɗaya dare, lokacin ta gama haɗa kayanta tsaf domin tafiyar gobe. Ta rako ni har ƙofar ɗakinmu muka yi sallama don ta tabbatar mini da cewar ƙarfe ukun dare za a zo ɗaukarta za su wuce garin Kano inda daga nan za ta kai jirgin safe da zai tashi daga cikin filin tashin jiragen sama na cikin jihar Kano zuwa garin Abuja, ta ɗauki makulin ɗakin ta damƙa mini na yi mata fatan sauƙa lafiya kana na shige ɗakin.
Washe gari da ƙyar na tashi sa boda daren jiya ban iya runtsawa da wuri, a makare na gabatar da sallan asubahi na zauna inda na yi sallan na yi shuru ina tunanin ta yadda ta fara gudanar da rayuwata a wannan gaɓar, sai dai kamar yadda Zinariya ta faɗa ne dole na tashi na yi yaƙin nema wa kaina ƴancin kai. Haka kuwa haka ba ta cika sati guda da tafiya ba sai da na zama babu wanda bai
sanni ba a kaf cikin gidan, hatta baƙin da suke zuwa san sunana ko da kuwa ba su taɓa ganin fuskata ba.
Na yi ƙaurin suna fiye da tunanin mai tunani ta yadda duk wani rashin mutunci da tijara na san farillai da sunnoninsu, har na kai munzalin da babu wanda yake rayuwa a cikin gidan da za a ƙira sunana ba tare da ya sha jinin jikinsa. Babu wanda ya isa ya nuna mini ɗan ƴatsa rashin mutuncin da nake yi ina sa yaƙinin ko Zinariya ce ta dawo ba za ta yi rabinsa.
Faɗa da jagwal babu wanda ba na shiga, rigima kuwa ko ba da ni ake yi ba zan shiga na amshe balle kuma da ni ake yi. Yo wani ma ya yi rawa balle ɗan makiɗi. Duk tijara da kwashe-kwashen Aminu sai da ya zubar da makamansa ya duƙa a gabana ya sara mini.
Har na kai lokacin da duk sa'ilin da aka kawo wata sabuwar yarinyar cikin gida waje na ake fara kawo ta na yi mata darasi. Sai dai duk barikin da nake bugawa babu wani na mijin da nake sake wa fuska balle na ba shi gangar jikina, haka nan duk shagalata ba na wasa da addini ko kaɗan du abin nake yi kuma a duk inda nake da na ji an yi ƙiran sallan zan bar abin da nake yi salla, haka nan azumin Litinin da alhamis ba ya taɓa wuce ni. Hakan nan ba a yin cikakkun kwanaki goma sha biyar ba tare da na sauƙe alƙur'ani ba, sadaka kuwa sai dai in ban sama taro da sisi ba.
Wasa-wasa sai da Zinariya ta ci satikai biyar cur ba ta dawo ba, tun abin ba ya damu na har ya soma damuna. A duk lokacin da zan ce Aminu ya ƙira mini layinta a kashe yake lamarin ya yi matuƙar ɗaga mini hankali da jefa ni cikin cakwakiyar tunanin an ya kuwa lafiya?.
[12/14, 12:30 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________________
Page 6ï¸âƒ£9ï¸âƒ£