Sashe 66
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya ɗago kai ya na kallona kafin ya ce"ke kuma me ye kin wani tsare ni da idanuna kamar za ki cinye ni? Mai sunan tsofaffi kawai". Murmusawa na yi kafin na furta"za ka ji da shi dai, ai sai an kula kare sannan yake haushi". Dariya ya ƙyalƙyale da shi tare da faɗin"yanzu ni ne karen ke nan? Ai wallahi in da ni kare ne da tunin na daɗe da cinye namanki har na taune ƙasussuwanki yarinya". Dariya na aka mai sauti ina jijjiga kaina na juya na fice daga cikin ɗakin na koma ɗakina, karatun Alkur'ani na ɗan yi kafin na fito na haɗa girkin rana. Haka na wuni cikin tsammanin ganin ƙiran Saif ya sanar da ni yadda ake ciki amma shuru tamkar an shuka dusa har na kwanta ƙiransa bai shigo cikin wayata. Ni kuma ina kunyar ƙiransa haka na daure safiya ta yi ko ƙaran shigowar saƙon kamfanin layin MTN na ji ya shigo cikin wayata sai na yi zumbur na tashi na duba ko zan ci karo da saƙon Saif amma wayam, haka na ƙarar da wunin wannan ranar komai cikin sanyin jiki nake aiwatar da shi tamkar majinyaciya. Har dare ta yi bai ƙira ni ba muna tsaka da cin abinci na ji wayata ta yi ruri na kusa bazama da sauti na je na ɗauko ta da yake ajiye a saman firijin da yake cikin falon
Ina duba wa na ga baƙuwar lamba ce take na ji raina ya ɓaci don ba wannan nake tsammani ba, ban yi ƙasa a gwiwa ba na katse ƙiran tare da ajiye wayar na dawo na zauna ina zama wani ƙiran ya ƙara shigowa a karo na biyu na yi biris da shi tamkar ban ji ba.
"Wai ba wayanki ake ƙira ba ne Amatullah?". Yaya Alhassan ya jefa mini tambaya cikin kakkauran murya.
"Baƙuwar lamba ce ban san wanda yake ƙira ba".
"Ɗauko min wayar na gani". Ya furta cikin ba da umarni, hakan ya tilasta mini tashi na je na ɗauko wayar na miƙa masa daidai sa'ilin da wani ƙiran yake ƙara
shigowa a karo na barkatai. Ya É—aga tare da sanya ta a amsa-kuwwa aka yi sallama ya amsa.
"Mansur ne mijin Amira". Aka furta daga ɗayan ɓangaren sai a lokacin da na ji muryarsa na tuna cewar lokacin da na je gidansu ta amshi lambana a fefa da nufin idan Mansur ya dawo za ta ƙira ni da wayarsa. Miƙo mini wayar da Yaya Alhassan ya yi bayan sun gama gaisa wa da Mansur shi ya dawo da ni cikin hayyacina daga karatun wasiƙan jakin da na faɗa. Na amsa wayar muka gaisa da shi kafin ya miƙa wa Amira ita muka gaisa.
"Ya na ji muryarki haka ba ki da lafiya ne ko kuma dai akwai wani abun da yake damunki?". Sai da na saci kallon Anty Sawwama kafin na mai da wa Amira amsar tambayar da ta yi mini.
"Lafiya ƙalau me kika ji da ya sa ki faɗin haka?".
"Haba! Amatullah ki na nufin ban san halinki ba ne ko kuma mene ne?". Da hanzari na taka mata burki ganin ta na ƙoƙarin wuce mini zani a cikin tsakiyar kasuwa.
"Mu na cin abincin bari inna gama zan ƙara ƙira". Ina gama maganan na katse ƙiran tare da ajiye wayan, na ci gaba da cin abincin sai dai duk a tsarge nake. Har muka gama cin abincin ban ɗago kaina ba muna gama wa na tattare kwanukan na je na wanke su kaina a ƙasa na zo na wuce zuwa ɗaki sai da na yi shirin kwanciya sannan na danna wa Amira ƙira, bugun farko ta ɗaga.
"Wai Amatullah ki na lafiya ƙalau kuwa? Na ji a jikina akwai matsala ga shi kwanakin sai mafarkinki nake yi da zaran na kwanta bacci wannan ya ƙara tabbatar min da cewar akwai wani damuwa. Don Allah mene ne yake faruwa?". Maimakon na ba ta amsa sai kawai na fashe da kukan da ya yi matuƙar gigita mata tunaninta ta din ga jeranta mini tambayo ɗaya bayan ɗaya.
"Subhanallahi! Hashashen zuciyata ya tabbata ke nan wai me yake faruwa ne sanar da ni idan akwai wani matsalan?".
"Amira ina cikin matsala shi kenan na jefa kaina da wanda bai ji ba bai gani ba cikin matsalar da ni na yi silar ruruwanta".
"Wani irin matsala ke nan?".
Take na kwashe komai na yadda muka yi da Saif har da alƙawarin da na yi masa da kuma yadda ya daina ƙira na na tsawon kwanaki biyu, sannan na ƙara da faɗin"jikina ya na ba ni tabbas akwai wani matsalan tun da har na ji shi shuru na tsawon wannan lokacin, sai dai ban san abin da yake faruwa. Idan ma matsalar ce ba na fatan ta shafi kowa mussamman Saifullah da shi ne mutum na farko da ya fara ba n goyon baya kuma ya tsaya mini tsayin daka wajen ganin na cika wannan burin da ya daɗe a cikin rai. Daman sai da Yaya Alhassan ya gargaɗe ni amma na ƙi amfani da abin da ya faɗa mini har umartana ya yi akan na karya memory ɗin amma na yi kunnen uwar shegu".
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Amatullah me yasa za ki aikata haka? Me yasa ke ba kya jin magana ne sannan ki na da kafiya akan abu. Na yi tunanin kin daɗe da mance wa da babin wannan mutumin a cikin rayuwarki ashe har yanzu ki na nan akan bakanki. Me yasa kike ƙoƙarin butulcewa rahamar da Ubangiji ya yi miki? Kike ta ƙoƙarin ganin kin bankaɗo sirrinki da Ubangiji ya lulluɓe ta a idon duniya?. Allah ya rufa miki asiri ya ceto ki daga rayuwar halakan da kika faɗa ya karkarto da hankalinki zuwa gida ki ka dawo rayuwa cikin ƴan uwanki, su ka rufa miki asiri suka yi miki gata suka ɗauke dukkan ɗawainiyyarki ta hanyar killace ki a cikin gida suna wadata ki da dukkanin abin buƙatun rayuwa. Daga ƙarshe Allah ya ɗaga kimarki ta hanyar yi miki tagomashi da samun mijin da yake shirye ya aure ki, duk wannan tarin ni'iman da Ubangiji ya lulluɓe ki da ita amma kike ƙoƙarin butulcewa". Izuwa yanzu kuka nake yi sosai wiwi don jikina ya gama mutuwa murus na kuma tabbatar wa cewar matsala ce ta hana Saifullah ƙira na ya sanar da ni halin da ake ciki.
Sai da ta sallawantar da wasu mintuna kafin ta furta"yanzu dai ki yi haƙuri ki kwantar da hankali, ki yi addu'a Allah ya sa komai lafiya kuma shi ma yana cikin ƙoshin lafiya. Idan kin ga abun ya ci tura to ina mai ba ki shawara da ke ki ɗaga waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki domin hakan ba laifi ba ne, masu iya magana su na cewa gaida mai gaishe ka ko da kuwa ba zai amsa ba". Sai da na zurfar da zafafan iska daga bakina kafin na ce da ita"na ƙira shi kuma?".
Ta katse ni"to hakan laifi ne ko kuma haramun ne aikata hakan? Kin ga wannan jan ajin babu inda zai kai ki sai dai ya sauƙe ki a tashar nadama. Ki ɗauki waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki alama ce ta nuna kin damu dashi, ko ke da nan ki na tunanin shi da yake ɗaga waya kullu yaumin ya ƙira ki shi bai san ciwon kansa da darajan kansa ba ne?". Luƙus jikina ya yi sanyi ƙalau har na kasa motsa wa daga inda nake zaune.
"In sha Allah inna ga shurun ya yi yawa zan ƙira shi". Ban ƙari sa zancen ba ta katse mini hanzari"kamar ya ya? Ai yanzu ya kamata ki ƙira shi son samu m, mu na gama wayar nan ki ƙira shi".
"Ki na ganin hakan ne mafita?". A kufule ta ce"ban sa ni ba, tun da ke nan zama kika yi kika miƙe ƙafa ki na jiran ƙiransa, to sai ki yi ta jira daga nan har zuwa ranar da mahadi zai bayyana". Ta gama furzar da zancen kit ta katse ƙiran ta bar ni da sauƙe tagwayen ajiyan zuciya tamkar wacce ta yi wani gagarumin aikin ƙarfi. Rumgume wayar na yi a ƙirjina tare da lumshe idanuna da ruwan hawaye yake zuba daga cikinsu ina yin zantukan na Amira suna yi mini amsa-kuwwa a cikin na'urar naɗan sautina tamkar a lokacin take furta mini su daki-daki.
Wani sashin zuciyata ta gaskata abun da Amira ta ce da ni, don haka na ɗauki wayar na lalumo lambarsa na dannan masa ƙira sai dai ƙiran ba ya tafiya, a jere a jere sai da na yi masa ƙira uku amma duk ba ya tafiya. Dole ƙanwar na ƙi na haƙura na ajiye wayar na kwanta ina ta fama da tunani kala daban-daban bacci sai da ya cika cikakken ɓarawo kafin ya iya ɗauka na sai da na makara tashi sallan asubahi, ko da na iddar da sallan sai da na ƙara gwada layin Saif amma har yanzu ba ya tafi, ganin tunanin yana neman ya yi rikita mini kwanyata ya sanya ni ɗauko alƙur'ani na buɗe na soma karanta ban gushe ina yi ba har sai da na ji zuciyata ta sama nutsuwa wani sanyi ya ziyarci sashin ruhina. Ko da na gama karatun zama na yi a wajen na zabga wani uban tagumi.
Ban san lokacin da Yaya Alhassan ya shigo cikin É—akin ba har sai da saurin muryarsa ta ratsa dodon kunnuwana.
"Tunanin me ye kike yi haka?". Na yi figigi na dawo cikin hayyacina"na'am ka ce me ye?". Ya kafe ni da ido kafin ya furta"tunanin me ye kike yi?".
Na sadda kaina ƙasa"babu komai".
"Koma dai mene ne tabbas kawai abin da yake damun ki, ki yi ƙoƙarin yaƙar duk damuwar da yake damunki a cikin ranki".
"In sha Allah Yaya na gode sosai".
Ina duba wa na ga baƙuwar lamba ce take na ji raina ya ɓaci don ba wannan nake tsammani ba, ban yi ƙasa a gwiwa ba na katse ƙiran tare da ajiye wayar na dawo na zauna ina zama wani ƙiran ya ƙara shigowa a karo na biyu na yi biris da shi tamkar ban ji ba.
"Wai ba wayanki ake ƙira ba ne Amatullah?". Yaya Alhassan ya jefa mini tambaya cikin kakkauran murya.
"Baƙuwar lamba ce ban san wanda yake ƙira ba".
"Ɗauko min wayar na gani". Ya furta cikin ba da umarni, hakan ya tilasta mini tashi na je na ɗauko wayar na miƙa masa daidai sa'ilin da wani ƙiran yake ƙara
shigowa a karo na barkatai. Ya É—aga tare da sanya ta a amsa-kuwwa aka yi sallama ya amsa.
"Mansur ne mijin Amira". Aka furta daga ɗayan ɓangaren sai a lokacin da na ji muryarsa na tuna cewar lokacin da na je gidansu ta amshi lambana a fefa da nufin idan Mansur ya dawo za ta ƙira ni da wayarsa. Miƙo mini wayar da Yaya Alhassan ya yi bayan sun gama gaisa wa da Mansur shi ya dawo da ni cikin hayyacina daga karatun wasiƙan jakin da na faɗa. Na amsa wayar muka gaisa da shi kafin ya miƙa wa Amira ita muka gaisa.
"Ya na ji muryarki haka ba ki da lafiya ne ko kuma dai akwai wani abun da yake damunki?". Sai da na saci kallon Anty Sawwama kafin na mai da wa Amira amsar tambayar da ta yi mini.
"Lafiya ƙalau me kika ji da ya sa ki faɗin haka?".
"Haba! Amatullah ki na nufin ban san halinki ba ne ko kuma mene ne?". Da hanzari na taka mata burki ganin ta na ƙoƙarin wuce mini zani a cikin tsakiyar kasuwa.
"Mu na cin abincin bari inna gama zan ƙara ƙira". Ina gama maganan na katse ƙiran tare da ajiye wayan, na ci gaba da cin abincin sai dai duk a tsarge nake. Har muka gama cin abincin ban ɗago kaina ba muna gama wa na tattare kwanukan na je na wanke su kaina a ƙasa na zo na wuce zuwa ɗaki sai da na yi shirin kwanciya sannan na danna wa Amira ƙira, bugun farko ta ɗaga.
"Wai Amatullah ki na lafiya ƙalau kuwa? Na ji a jikina akwai matsala ga shi kwanakin sai mafarkinki nake yi da zaran na kwanta bacci wannan ya ƙara tabbatar min da cewar akwai wani damuwa. Don Allah mene ne yake faruwa?". Maimakon na ba ta amsa sai kawai na fashe da kukan da ya yi matuƙar gigita mata tunaninta ta din ga jeranta mini tambayo ɗaya bayan ɗaya.
"Subhanallahi! Hashashen zuciyata ya tabbata ke nan wai me yake faruwa ne sanar da ni idan akwai wani matsalan?".
"Amira ina cikin matsala shi kenan na jefa kaina da wanda bai ji ba bai gani ba cikin matsalar da ni na yi silar ruruwanta".
"Wani irin matsala ke nan?".
Take na kwashe komai na yadda muka yi da Saif har da alƙawarin da na yi masa da kuma yadda ya daina ƙira na na tsawon kwanaki biyu, sannan na ƙara da faɗin"jikina ya na ba ni tabbas akwai wani matsalan tun da har na ji shi shuru na tsawon wannan lokacin, sai dai ban san abin da yake faruwa. Idan ma matsalar ce ba na fatan ta shafi kowa mussamman Saifullah da shi ne mutum na farko da ya fara ba n goyon baya kuma ya tsaya mini tsayin daka wajen ganin na cika wannan burin da ya daɗe a cikin rai. Daman sai da Yaya Alhassan ya gargaɗe ni amma na ƙi amfani da abin da ya faɗa mini har umartana ya yi akan na karya memory ɗin amma na yi kunnen uwar shegu".
"Innalillahi wa inna ilahirin raji'un! Amatullah me yasa za ki aikata haka? Me yasa ke ba kya jin magana ne sannan ki na da kafiya akan abu. Na yi tunanin kin daɗe da mance wa da babin wannan mutumin a cikin rayuwarki ashe har yanzu ki na nan akan bakanki. Me yasa kike ƙoƙarin butulcewa rahamar da Ubangiji ya yi miki? Kike ta ƙoƙarin ganin kin bankaɗo sirrinki da Ubangiji ya lulluɓe ta a idon duniya?. Allah ya rufa miki asiri ya ceto ki daga rayuwar halakan da kika faɗa ya karkarto da hankalinki zuwa gida ki ka dawo rayuwa cikin ƴan uwanki, su ka rufa miki asiri suka yi miki gata suka ɗauke dukkan ɗawainiyyarki ta hanyar killace ki a cikin gida suna wadata ki da dukkanin abin buƙatun rayuwa. Daga ƙarshe Allah ya ɗaga kimarki ta hanyar yi miki tagomashi da samun mijin da yake shirye ya aure ki, duk wannan tarin ni'iman da Ubangiji ya lulluɓe ki da ita amma kike ƙoƙarin butulcewa". Izuwa yanzu kuka nake yi sosai wiwi don jikina ya gama mutuwa murus na kuma tabbatar wa cewar matsala ce ta hana Saifullah ƙira na ya sanar da ni halin da ake ciki.
Sai da ta sallawantar da wasu mintuna kafin ta furta"yanzu dai ki yi haƙuri ki kwantar da hankali, ki yi addu'a Allah ya sa komai lafiya kuma shi ma yana cikin ƙoshin lafiya. Idan kin ga abun ya ci tura to ina mai ba ki shawara da ke ki ɗaga waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki domin hakan ba laifi ba ne, masu iya magana su na cewa gaida mai gaishe ka ko da kuwa ba zai amsa ba". Sai da na zurfar da zafafan iska daga bakina kafin na ce da ita"na ƙira shi kuma?".
Ta katse ni"to hakan laifi ne ko kuma haramun ne aikata hakan? Kin ga wannan jan ajin babu inda zai kai ki sai dai ya sauƙe ki a tashar nadama. Ki ɗauki waya ki ƙira shi ki ji halin da ake ciki alama ce ta nuna kin damu dashi, ko ke da nan ki na tunanin shi da yake ɗaga waya kullu yaumin ya ƙira ki shi bai san ciwon kansa da darajan kansa ba ne?". Luƙus jikina ya yi sanyi ƙalau har na kasa motsa wa daga inda nake zaune.
"In sha Allah inna ga shurun ya yi yawa zan ƙira shi". Ban ƙari sa zancen ba ta katse mini hanzari"kamar ya ya? Ai yanzu ya kamata ki ƙira shi son samu m, mu na gama wayar nan ki ƙira shi".
"Ki na ganin hakan ne mafita?". A kufule ta ce"ban sa ni ba, tun da ke nan zama kika yi kika miƙe ƙafa ki na jiran ƙiransa, to sai ki yi ta jira daga nan har zuwa ranar da mahadi zai bayyana". Ta gama furzar da zancen kit ta katse ƙiran ta bar ni da sauƙe tagwayen ajiyan zuciya tamkar wacce ta yi wani gagarumin aikin ƙarfi. Rumgume wayar na yi a ƙirjina tare da lumshe idanuna da ruwan hawaye yake zuba daga cikinsu ina yin zantukan na Amira suna yi mini amsa-kuwwa a cikin na'urar naɗan sautina tamkar a lokacin take furta mini su daki-daki.
Wani sashin zuciyata ta gaskata abun da Amira ta ce da ni, don haka na ɗauki wayar na lalumo lambarsa na dannan masa ƙira sai dai ƙiran ba ya tafiya, a jere a jere sai da na yi masa ƙira uku amma duk ba ya tafiya. Dole ƙanwar na ƙi na haƙura na ajiye wayar na kwanta ina ta fama da tunani kala daban-daban bacci sai da ya cika cikakken ɓarawo kafin ya iya ɗauka na sai da na makara tashi sallan asubahi, ko da na iddar da sallan sai da na ƙara gwada layin Saif amma har yanzu ba ya tafi, ganin tunanin yana neman ya yi rikita mini kwanyata ya sanya ni ɗauko alƙur'ani na buɗe na soma karanta ban gushe ina yi ba har sai da na ji zuciyata ta sama nutsuwa wani sanyi ya ziyarci sashin ruhina. Ko da na gama karatun zama na yi a wajen na zabga wani uban tagumi.
Ban san lokacin da Yaya Alhassan ya shigo cikin É—akin ba har sai da saurin muryarsa ta ratsa dodon kunnuwana.
"Tunanin me ye kike yi haka?". Na yi figigi na dawo cikin hayyacina"na'am ka ce me ye?". Ya kafe ni da ido kafin ya furta"tunanin me ye kike yi?".
Na sadda kaina ƙasa"babu komai".
"Koma dai mene ne tabbas kawai abin da yake damun ki, ki yi ƙoƙarin yaƙar duk damuwar da yake damunki a cikin ranki".
"In sha Allah Yaya na gode sosai".