Sashe 18
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Anty Altine don Allah ina ba damuwa zan yi amfani da alƙur'anin nan". Ta ɗago ido ta yi mini wani banzan kallo kafin ta ce"ai ba a kaina kika gan shi, da za ki ce sai kin jira na sauƙe kafin ki yi amfani da shi". Ban ce da ita komai ba na tashi na ɗauko alƙur'nin na soma karanta suratul Maryam cikin nutsuwa da fitar da haƙƙin ko wani harafi ɗaya bayan ɗaya.
"Malama ki rage muryarki don bacci nake so na yi". Na yi mata wani kallo ta wutsiyar idona na ci gaba da karatun da nake yi ba tare da na bi ta kanta ba. Ban yi aune ba kawai na ji an zagbaw mini wani gigitaccen mari a kuncina babu shiri na dafe kuncina tare da ɗago idanuna na sauƙe shi akan fuskar Altine da take tsaye a kaina ta riƙe ƙugu tana huci tamkar saniyar da take shirin kai bugu.
"Me ye na yi miki da za ki mare ni?".
"Bari ki ji in gaya miki wani abun da ba ki sani ba shi ne duk wata ƴar aikin da aka kawo cikin gidan nan dole ta bi umarnina. Sannan wajibi ne a gare ta ta yi mini biyayya don a gaba nake da ita. Na lura tun ranar ki ta farko kanki yana rawa ki na ta wani ƙoƙarin shige wa jikin Hajiya da wani kinibibin jan su Aryan a jikinki, to billahillazi tun wuri gwara ki kama kanki kafin na haɗa miki sharri da tuggun da ba za ki iya fitar da kanki ba". Na ji zuciyata tana wani irin harzuƙa ta zo mini har wuya tabbas na yi sanyi don da zamani da nake gida ne ba ta isa ta ɗaga mini ƴatsa ban karya shi ba duk da kuwa ina da haƙuri matuƙa da kai zuciya nisa.
Tsam na miƙe jikina har wani rawa yake yi kamar mazari haƙwarana suna karabɗiya da juna suna ba da wani sautin ɗas ɗas. Ta matso dab da ni ta ce"ko za ki rama ne na ga kin miƙe ina wani jijjiga?". Ta saki wani bushashshiyar dariyar da ba ta da haɗi da nishaɗi, jin daɗi ko kuma walwala kana na furta"ai ko dukana kika yi da itacen bishiya ba zan rama ba Anty, sa boda na ƙoshi da tarbiyya kuma an koyar da ni yadda zan girmama na gaba da ni ko da kuwa da sankan ɗaya ya riga ni zuwa duniya balle ke da kin kusa haifa ta. Bari na je na duba Hajiya ko sun gama na tattare kwanukan". Da alama ba ta ji daɗin zancena na ƙarshe ba don sakeke ta yi tana bi na da kallo tamkar ta sama majigi har na fice daga cikin ɗakin ba ta ce da ni komai ba.
Da sallama na ƙariso ciki falon na ga har sun gama cin abincin sun koma kan kujeru sun zauna, na tsuguna na yi wa Hajiya sannu da hutawa kana na isa wajen dinning table ɗin na tattare kwanunkan na kai kicin na wanke su tas na mayar da su majiyarsu.
Ina kicin ɗin Ayan ya shigo wai na zo in ji Umminsu, muka fito tare da shi na zauna a ƙasa cikin girmama wa na ce"Hajiya ga ni".
"Jiya Saif ya kai ki gidan nakun?". Ƙirjina ya buga da ƙarfi na ɗago ido ina satan kallonsa na ga shi kam ko a jikinsa wai an muntsini kakkarauna yana zaune yana latsa wayar da yake hannunsa.
Sai da na daidaita nutsuwata kafin na iya furta"e Hajiya ya kai ni". Ta mayar da dubanta gare shi"ka ga gidan na sun?".
Ba tare da ya É—ago kansa ba ya ce"e Hajiya Antynmu ko yanzu ma in ki na so zan iya kai ki".
"To alhamdulillah tun da ka ga gidan, ka ba ta makullin sashinka ta share maka kafin ka fita. Don ni yau sai around 5:pm zan fita". Sai a lokacin ya ɗago kansa daga latsa wayar da yake yi"Anty ni fa sashina a gyare yake. Ke ma kin san ko wata macen ba za ta nuna min tsafta ba balle kuma wannan". Ta murmusa kafin ta ce"ai duk tsaftan namiji Saif a bayan mace yale komai ƙanƙantan ta kuwa. Ka ba ta makullan kawai ta je ta gyara maka, kar wani gyara ka iya kai da yaushe ma ka zauna a cikin gidan". Kamar na yi magana na ce ta ita ta bar shi kawai tun da ba ya so sai kuma na yi shuru.
Muryarsa a cushe ya ce"a buÉ—e yake".
"To Amatullah tashi ki je sashin nasan ma a buɗe yake, ki gyara masa shi tsaf irin gyaran da shi da kanki sai ya sa an nemo ki gobe. Idan hakan ya faru kuma ni da kaina zan tsaya miki ki gara shi kamar ƙwallon ƙafa kafin ki je ki ƙara gyara masa".
"To Hajiya". Na amsa da shi a taƙaice jikina gabaɗaya ya mutu murus, na tashi na fita zuwa sashin nasan ƙirjina yana tsananta bugu kamar zai fito waje. Sai da na isa ƙofar sashin na ja dogon numfashi na fesar kafin na turo ƙofar na shiga ciki na tsaya ina ƙarewa zubi da tsarin falon kallo. Ba shi da girma sosai don bai kai na Hajiya Muhibbat ba ya tsaru sosai da dukkan abubuwan more rayuwa da ƙawata waje, komai na falon fari ne tun daga kan labulaye, kujeru, tayis da kuma kafet ɗin hatta abin da aka ɗaura tv a kai fari ne. Na cire hijabina na ɗaura a ƙuguna na soma tattare takardun da na gani a barbaze akan kujerar kan teburin kofi ne da goran ruwan da aka sha ba a ɗauke ba.
Na tattare takardun na kimtsa su na saka a cikin jakar da na gani a gefe, na ɗauke kofi da goran ruwan na shiga ɗaya daga cikin ƙofofi biyu da na gani. Ƙofan farko da na shiga na ga kicin ne na ajiye kofi da goran, kicin babu ƙazanta a cikinsa amma komai a birkice yake komai ba ya muhallinsa.
Ban san sa'ilin da na saki tsakin takaici ba ina kwakwayon muryarsa na ce"ni ko'ina a sashina a gyare ya ke ko wata macen ba za ta nuna mini tsafta ba". Na tattare kicin ɗin na share kana yi mopping na fito na shiga ɗayan ƙofan ɗaki ne mai ɗauke da kayan ɗaki tsaf sai dai da alama ba wanda yake kwana a cikinsa saboda yadda ya yi ƙora na karkaɗe na sauya zanin gadon na shiga banɗaki na wanke na fito na hau benin ya sada ni da wani ɗan madaidaicin falo nan komai a gyare yake sai ɗan abin da ba za a rasa ba, na kashe tvn da na gani a kunne kana na rufe tagogin da suke buɗe.
Ƙofa ɗaya na gani na shiga na tarar da ɗakin kwana ne shi ma komai na cikinsa launin fari ne hatta zanin dake kan gadon.
Sauya zanin gadon na fara yi na gyara gaban madubin da komai ya ke warwartse kana na wanke banɗaki. Na hango wani air freshener akan dirowar da ke jikin gadon na je da nufin ɗauka na feshe ɗakin da shi, sai dai mummunan ganin da na yi ya tursasa mini tsayawa cak na kasa motsawa na tsawon wasu dakiƙu.
Jikina yana rawa tamkar mazari na kai hannu na ɗauko hoton da na gani ajiye a saman dirowar ina ƙara ware idanuna akan sa. In dai ba idanuna ba ne suka sama matsala tabbas hoton Muhammad Taufik da Saif na gani tare cikin shiga irin ɗaya kowa hannunsa riƙe da sallaya da alama masallaci za su je, ko kuma ranar bikin salla aka yi hoton. Duk su biyun fuskokinsu yana ɗauke da maɗaukakin annurin.
"Muhammad Taufik".
Na furta cikin rawan jiki da na murya yayin da wasu hawaye suke gangarowa daga idanuna suna wanke mini fuskana. Jin an turo ƙofan ɗakin an buɗe ya sani na firgita da har ban san lokacin da hoton ya zame daga hannuna zuwa ƙasa ba, gilashin dake jiki ya yi kwasa-kwasa. Runtse idanuna na yi ina kai hannayena dukka biyu na toshe kunnuwana da ƙaran fashewan gilashin da ya gigita ni har ya na barazanar juyar mini da ƙaramar curin ƙwaƙwalwata.
"Me ye kike yi a nan?".
Na yi muryarsa tamkar daga sama ban iya cewa da shi komai har ya iso inda nake tsaye daidai lokacin da nake buÉ—e lumshashshun idanuna har na gama buÉ—e su tar akan gilashin da ya tarwatse a wajen.
Ina ɗago kaina muka haɗa ido da shi ya yi mini wani matsaiyacin kallo kafin ya tsuguna ya ɗauki frame ɗin bai ce da ni komai ba ya fita daga cikin ɗakin. Wani kuka ne mai ƙarfi ya kuɓuce mini na sulale ƙasa na yi zaman dirshan ina jin yadda dunduniyar ƙafana ya cashi gilashin yana fitar da jini amma ban damu ba na ci gaba da kukan da nake, tare da jefa wa kaina jerin gwanon tambayoyin da na gaza cimma amshoshinsu.
Me ye alaƙar Saif da Muhammad Taukif da har na ga hotonsu tare? Shin da gaske yadda kunnuwana suka ji yo mini shi ne baƙon da zai zo cikin gidan nan da yammacin gobe?. Tagwayen ajiyan zuciya mai ƙarfi na ja na fesar kafin na yi ƙarfin halin tashi tsaye ina ɗan ɗingisa ƙafata na ɗauko tsintsiya na share wajen na fesa air freshener ɗin da na yi niyya kana na ja ƙofar ɗakin na fito. Babu kowa a falon saman amma an kunna sautin karatun alƙur'ani cikin wata muryar da na kasa tuna inda na taɓa jin ta, na sauƙo ƙasa na iske shi zaune a falon ƙasa yana zaune ya yi shuru kamar wanda yake nazarin wani abu. Na zo na durƙusa a gabansa.
"Na ga ma duk wani gyaran da ya dace na yi. Shi ne na ce bari na tamnaya inda akwai abin da kake so a yi maka".
"Malama ki rage muryarki don bacci nake so na yi". Na yi mata wani kallo ta wutsiyar idona na ci gaba da karatun da nake yi ba tare da na bi ta kanta ba. Ban yi aune ba kawai na ji an zagbaw mini wani gigitaccen mari a kuncina babu shiri na dafe kuncina tare da ɗago idanuna na sauƙe shi akan fuskar Altine da take tsaye a kaina ta riƙe ƙugu tana huci tamkar saniyar da take shirin kai bugu.
"Me ye na yi miki da za ki mare ni?".
"Bari ki ji in gaya miki wani abun da ba ki sani ba shi ne duk wata ƴar aikin da aka kawo cikin gidan nan dole ta bi umarnina. Sannan wajibi ne a gare ta ta yi mini biyayya don a gaba nake da ita. Na lura tun ranar ki ta farko kanki yana rawa ki na ta wani ƙoƙarin shige wa jikin Hajiya da wani kinibibin jan su Aryan a jikinki, to billahillazi tun wuri gwara ki kama kanki kafin na haɗa miki sharri da tuggun da ba za ki iya fitar da kanki ba". Na ji zuciyata tana wani irin harzuƙa ta zo mini har wuya tabbas na yi sanyi don da zamani da nake gida ne ba ta isa ta ɗaga mini ƴatsa ban karya shi ba duk da kuwa ina da haƙuri matuƙa da kai zuciya nisa.
Tsam na miƙe jikina har wani rawa yake yi kamar mazari haƙwarana suna karabɗiya da juna suna ba da wani sautin ɗas ɗas. Ta matso dab da ni ta ce"ko za ki rama ne na ga kin miƙe ina wani jijjiga?". Ta saki wani bushashshiyar dariyar da ba ta da haɗi da nishaɗi, jin daɗi ko kuma walwala kana na furta"ai ko dukana kika yi da itacen bishiya ba zan rama ba Anty, sa boda na ƙoshi da tarbiyya kuma an koyar da ni yadda zan girmama na gaba da ni ko da kuwa da sankan ɗaya ya riga ni zuwa duniya balle ke da kin kusa haifa ta. Bari na je na duba Hajiya ko sun gama na tattare kwanukan". Da alama ba ta ji daɗin zancena na ƙarshe ba don sakeke ta yi tana bi na da kallo tamkar ta sama majigi har na fice daga cikin ɗakin ba ta ce da ni komai ba.
Da sallama na ƙariso ciki falon na ga har sun gama cin abincin sun koma kan kujeru sun zauna, na tsuguna na yi wa Hajiya sannu da hutawa kana na isa wajen dinning table ɗin na tattare kwanunkan na kai kicin na wanke su tas na mayar da su majiyarsu.
Ina kicin ɗin Ayan ya shigo wai na zo in ji Umminsu, muka fito tare da shi na zauna a ƙasa cikin girmama wa na ce"Hajiya ga ni".
"Jiya Saif ya kai ki gidan nakun?". Ƙirjina ya buga da ƙarfi na ɗago ido ina satan kallonsa na ga shi kam ko a jikinsa wai an muntsini kakkarauna yana zaune yana latsa wayar da yake hannunsa.
Sai da na daidaita nutsuwata kafin na iya furta"e Hajiya ya kai ni". Ta mayar da dubanta gare shi"ka ga gidan na sun?".
Ba tare da ya É—ago kansa ba ya ce"e Hajiya Antynmu ko yanzu ma in ki na so zan iya kai ki".
"To alhamdulillah tun da ka ga gidan, ka ba ta makullin sashinka ta share maka kafin ka fita. Don ni yau sai around 5:pm zan fita". Sai a lokacin ya ɗago kansa daga latsa wayar da yake yi"Anty ni fa sashina a gyare yake. Ke ma kin san ko wata macen ba za ta nuna min tsafta ba balle kuma wannan". Ta murmusa kafin ta ce"ai duk tsaftan namiji Saif a bayan mace yale komai ƙanƙantan ta kuwa. Ka ba ta makullan kawai ta je ta gyara maka, kar wani gyara ka iya kai da yaushe ma ka zauna a cikin gidan". Kamar na yi magana na ce ta ita ta bar shi kawai tun da ba ya so sai kuma na yi shuru.
Muryarsa a cushe ya ce"a buÉ—e yake".
"To Amatullah tashi ki je sashin nasan ma a buɗe yake, ki gyara masa shi tsaf irin gyaran da shi da kanki sai ya sa an nemo ki gobe. Idan hakan ya faru kuma ni da kaina zan tsaya miki ki gara shi kamar ƙwallon ƙafa kafin ki je ki ƙara gyara masa".
"To Hajiya". Na amsa da shi a taƙaice jikina gabaɗaya ya mutu murus, na tashi na fita zuwa sashin nasan ƙirjina yana tsananta bugu kamar zai fito waje. Sai da na isa ƙofar sashin na ja dogon numfashi na fesar kafin na turo ƙofar na shiga ciki na tsaya ina ƙarewa zubi da tsarin falon kallo. Ba shi da girma sosai don bai kai na Hajiya Muhibbat ba ya tsaru sosai da dukkan abubuwan more rayuwa da ƙawata waje, komai na falon fari ne tun daga kan labulaye, kujeru, tayis da kuma kafet ɗin hatta abin da aka ɗaura tv a kai fari ne. Na cire hijabina na ɗaura a ƙuguna na soma tattare takardun da na gani a barbaze akan kujerar kan teburin kofi ne da goran ruwan da aka sha ba a ɗauke ba.
Na tattare takardun na kimtsa su na saka a cikin jakar da na gani a gefe, na ɗauke kofi da goran ruwan na shiga ɗaya daga cikin ƙofofi biyu da na gani. Ƙofan farko da na shiga na ga kicin ne na ajiye kofi da goran, kicin babu ƙazanta a cikinsa amma komai a birkice yake komai ba ya muhallinsa.
Ban san sa'ilin da na saki tsakin takaici ba ina kwakwayon muryarsa na ce"ni ko'ina a sashina a gyare ya ke ko wata macen ba za ta nuna mini tsafta ba". Na tattare kicin ɗin na share kana yi mopping na fito na shiga ɗayan ƙofan ɗaki ne mai ɗauke da kayan ɗaki tsaf sai dai da alama ba wanda yake kwana a cikinsa saboda yadda ya yi ƙora na karkaɗe na sauya zanin gadon na shiga banɗaki na wanke na fito na hau benin ya sada ni da wani ɗan madaidaicin falo nan komai a gyare yake sai ɗan abin da ba za a rasa ba, na kashe tvn da na gani a kunne kana na rufe tagogin da suke buɗe.
Ƙofa ɗaya na gani na shiga na tarar da ɗakin kwana ne shi ma komai na cikinsa launin fari ne hatta zanin dake kan gadon.
Sauya zanin gadon na fara yi na gyara gaban madubin da komai ya ke warwartse kana na wanke banɗaki. Na hango wani air freshener akan dirowar da ke jikin gadon na je da nufin ɗauka na feshe ɗakin da shi, sai dai mummunan ganin da na yi ya tursasa mini tsayawa cak na kasa motsawa na tsawon wasu dakiƙu.
Jikina yana rawa tamkar mazari na kai hannu na ɗauko hoton da na gani ajiye a saman dirowar ina ƙara ware idanuna akan sa. In dai ba idanuna ba ne suka sama matsala tabbas hoton Muhammad Taufik da Saif na gani tare cikin shiga irin ɗaya kowa hannunsa riƙe da sallaya da alama masallaci za su je, ko kuma ranar bikin salla aka yi hoton. Duk su biyun fuskokinsu yana ɗauke da maɗaukakin annurin.
"Muhammad Taufik".
Na furta cikin rawan jiki da na murya yayin da wasu hawaye suke gangarowa daga idanuna suna wanke mini fuskana. Jin an turo ƙofan ɗakin an buɗe ya sani na firgita da har ban san lokacin da hoton ya zame daga hannuna zuwa ƙasa ba, gilashin dake jiki ya yi kwasa-kwasa. Runtse idanuna na yi ina kai hannayena dukka biyu na toshe kunnuwana da ƙaran fashewan gilashin da ya gigita ni har ya na barazanar juyar mini da ƙaramar curin ƙwaƙwalwata.
"Me ye kike yi a nan?".
Na yi muryarsa tamkar daga sama ban iya cewa da shi komai har ya iso inda nake tsaye daidai lokacin da nake buÉ—e lumshashshun idanuna har na gama buÉ—e su tar akan gilashin da ya tarwatse a wajen.
Ina ɗago kaina muka haɗa ido da shi ya yi mini wani matsaiyacin kallo kafin ya tsuguna ya ɗauki frame ɗin bai ce da ni komai ba ya fita daga cikin ɗakin. Wani kuka ne mai ƙarfi ya kuɓuce mini na sulale ƙasa na yi zaman dirshan ina jin yadda dunduniyar ƙafana ya cashi gilashin yana fitar da jini amma ban damu ba na ci gaba da kukan da nake, tare da jefa wa kaina jerin gwanon tambayoyin da na gaza cimma amshoshinsu.
Me ye alaƙar Saif da Muhammad Taukif da har na ga hotonsu tare? Shin da gaske yadda kunnuwana suka ji yo mini shi ne baƙon da zai zo cikin gidan nan da yammacin gobe?. Tagwayen ajiyan zuciya mai ƙarfi na ja na fesar kafin na yi ƙarfin halin tashi tsaye ina ɗan ɗingisa ƙafata na ɗauko tsintsiya na share wajen na fesa air freshener ɗin da na yi niyya kana na ja ƙofar ɗakin na fito. Babu kowa a falon saman amma an kunna sautin karatun alƙur'ani cikin wata muryar da na kasa tuna inda na taɓa jin ta, na sauƙo ƙasa na iske shi zaune a falon ƙasa yana zaune ya yi shuru kamar wanda yake nazarin wani abu. Na zo na durƙusa a gabansa.
"Na ga ma duk wani gyaran da ya dace na yi. Shi ne na ce bari na tamnaya inda akwai abin da kake so a yi maka".