Sashe 36
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na furta yayin da nake tashi na fice daga cikin falon ina goge fuskana da hawaye ya damalmala mini shi. Ƙarar rufe ƙofar da ta yi shi ya sanya Saif buɗe lumshashshun idanunsa yana bin ƙofar da kallo daidai sa'ilin da wayarsa ta soma ruri. Sunan Sultan ya bayyana cikin screen ɗin wayar. Sai da ƙiran ya kusa tsinkewa kana ya ɗaga bai sanya a kunnensa ba maimakon hakan sai ya sanya ta a amsa-kuwwa.
"Saif".
"Ina jinka".
"Ya jikin nakan? Wallahi hankalina ya tashi sosai da na ji halin da kake ciki". Sai da ya cije naman leɓansa kafin ya ba shi da faɗin"da sauƙi fa yanzu yadda nake ji na ma zan iya wasan polo da ingarman doki, sa boda ƙarfin da nake ji a jikina".
Murmusawa Sultan ya yi kafin ya ce"daman har yanzu ka na fama da wannan lalular Saif? Na yi tunanin zuwa lokacin abubuwan sun yi sauƙi ba kamar da ba".
"Babu abin da ya sauya daga abin da ka sa ni Sultan". Shuru ya biyo bayan zancen Saif na ƙarshe. Sai can ya ce"wace ce yarinyar da ta ɗauki wayarka muka yi waya da ita? Don na san gidanku babu ɗiya mace".
A dake ya furta"ni ma ban san ta ba".
"Mu bar maganar wasa mana Saif, wace ce?".
"Ka riga da ba wa kanka amsa tun da tun farkon zancenka kai ma ka ce gidanmu babu É—iya mace".
Dariya sosai Sultan ya yi sai da ya tsagaita ya furta"any way ko ma dai wace ce, tabbas ta shiga cikin firgici ganin halin da kake ciki ka ji yadda take kuka kuwa tsakanin da Allah. Tambaya kuwa ta yi min ya kai sau ashirin akan za ka tashi kuwa? Na ce da ita in sha Allah, ba don ta zo akan lokaci ba Saif wataƙila da yanzu wani labarin ake yi ba wannan ba. Ko wace ce wannan yarinyar haƙiƙa ta ceto rayuwarka kuma ta ba da gagarumar gudummawa wajen tabbatar da numfashin da kake yi yanzu a cikin duniya, ka gode mata don ta cancanci hakan sosai".
Kit! Saif ya datse ƙiran ba tare ya ba wa Sultani damar amayar da sauran zancen da suke cikin bakisa ba. Ya zame daga zaunen da yake ya kwanta akan bayansa yana jan bargon ya lulluɓe rabin jikinsa, numfashi mai zafi ya furta daga bakinsa yana ɗan lumshe idanunsa sa boda ciwon kan da yake ji yana damun sa kaɗan kaɗan.
Ya daɗe kwance a wajen yana saƙa da warwara cikin ransa kafin ya tashi ya haura sama zuwa cikin ɗakinsa, wanka ya yi ya ɗauro alwala ya fito ya sanya farar doguwar jallabiya da aka yi wa ado da zare launin ruwan zuma mai ƙyalli da ɗaukar ido, ƙaramar hula ya sanya a kansa ya shimfiɗa sallaya ya gabatar da sallan zuhur tare na sallan asr yana iddarwa ya ɗauko alƙur'ani ya soma karantawa.
Dole ne ya tursasa masa rufe alƙur'anin ya ajiye a gefe sa boda rawar da jikinsa yake yi tamkar mazari. Ya kunna ƙira'an Sheikh Ahmad Suleiman a cikin wayarsa ya ajiye, a nan kan sallayan ya kwanta take wani bacci mai nauyin gaske ya yi awon gaba da shi ba tare da ya shirya wa hakan ba.
Tun da na fito daga sashinsa na nufi hanyar gate ina tafiya a hankali tamkar babu laka a jikina, ina dab da fita na tsinkayo muryar Baba Mai gadi.
"Ƴar nan lafiya kuwa na ga kamar kuka kike yi?". Na yi saurin goge fuskana da ban san lokacin da wasu sabbin hawayen suka fito ba, na waigo tare da duƙawa na gaishe shi, ya amsa yana bi na da kallon tuhumar son gano abin da yake faruwa da ni. Ya zauna akan bencin da yake wajen ni ma na je na zauna.
"Ko dai cikin gidan ne babu lafiya? Don É—azu na ga Saifullahi ya fito daga cikin gidan ya nufi sashinsa cikin wani irin yanayi, wanda har ina tsoron har hakan ya tasar masa da ciwon da yake damunsa".
Na sauri na ce"wani irin ciwo ke nan Baba?". Ya yi ɗan jim kafin can ya ce"tun yana ƙarami yake fama da wani irin ciwo ga shi nan dai kamar aikin aljanu ko iskokai. A duk lokacin da ransa ya ɓaci ko kuma ya yi cacar baki da wani ke wani lokacin ma ko dogon zancen ya yi sai ki ga kawai ya yanke jiki ya faɗi jikinsa ya sanƙare haka zai koma ba shi da maraba da gawar da rai ya yi bankwana da gangar jikinsa, sai ta yi masa karatun alƙur'ani kafin yake dawowa daidai kuma da zaran ya tashi zai koma kamar ba shi ba".
Æoyayyan ajiyan zuciya na sauÆ™e ina jin Æ™aran da Æ™irjina yake yi tamkar zai faso allon Æ™irjin ya fito waje ya taka rawar disko. Sai da na harhaÉ—o kalaman kafin na yi nasarar cewa"Allah ya na shi lafiya, Baba bari na je gida na dawo".
"Amin ya Allah, to Æ´ar nan a gaishe da mutanan gidan".
"Za su ji in sha Allah". Na amsa da shi yayin da nake tashi daga kan bencin, tafiya kawai nake yi ba tare da na san inda nake cilla ƙafafuna ba ina tafe ina tunani tare da nazarin kalaman Baba mai gadi. Saura ƙiris wani mai napep ya kwashe ni Allah a rufa asiri, ai kuwa ya fito ya balbale ni da bala'i da masifa tamkar zai yi aron baki da ƙyar ya haƙura ya ja napep ɗinsa ya tafi bayan ya gama wurwurga mini ashariya tamkar ya hana jini da dangin maguzawa. Sai yamma lilis na iso gida lokacin ko wacce budurwar dake cikin gidan ta ci ƙwaras tana ƙoƙarin fice wa wajen harkanta. Gidan ya yi shuru sosai ina shigowa na kai duba na ƙofar ɗakin Hajiya Babba na ga ƙofar ɗakin a rufe an buga masa kwaɗo. Na lura cikin kwanakin nan ba na ganin La'aniyatu a cikin gidan nan kuma na rasa wanda zan tambaya.
Har na ɗauki hanyar ɗakinmu sai kuma na fasa don har cikin raina ba na ƙaunar haɗa ido da Sha'awanatu don har yanzu ban huce daga abin da ya faru ba. Ganin ƙofar ɗakin Zinariya a buɗe ya ba ni ƙwarin gwiwar faɗa wa cikin ɗakin.
Na iske ta tana kwance akan katifarta tana bacci na zauna a gefen tana dukan ƙafarta har sai da ta shi, ganin ni ce ya hana ta ƙarisa ashariyar da ta danno.
"Au wai ke ce?".
"Da waye kike yi tunani?". Ba ta amsa mini ba har sai da ta tashi ta zauna ta ce"kin dawo daga aikin wahalar ke nan?". Na yi murmushi har sai da haƙwarana suka bayyana"aikin rufa wa kai asiri dai ko?". Ta taɓe baki ba tare da ta ce da ni ko kanzil ba sai ma sauya akalar zancen da ta yi
"Ki na da lokaci ki raka ni kasuwa?".
"Duk a cikin shirin tarban Yallaɓai ɗin ne?". Ta yi fari da idonta"ƙwarai kuwa". Na gyaɗa kaina"Allah ya bar ƙauna Madam ta gaban goshin Saddam". Caraf bakina ya yi furucin ba tare ta yi shawari da zuciyata ba.
"Saddam kuma? Ina kika san sunansa?".
Cike da dabara na wayince"kar ki daina basirar duk wata macen da kika ga ni a cikin harkan bariki".
[12/9, 6:43 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________________
Page 6ï¸âƒ£5ï¸âƒ£
Tun da na yi zancen take bi na da kallo da mamakin zancen ya tilasta mata wartsakewa daga baccin da take yi. Ta rarumo hannuna ta riƙe gam"sanar da ni inda kika san sunansa don Allah". Na saki wani shu'umin murmushin gefen baki kafin na furta"ki fa kwantar da hankalinki na canza ne kawai. Sai kuma aka yi dace sunan ya zo daidai". Ta yi jim tana ta bi na da kallo kafin can ta ce"kin tabbata?".
Na yi fari da idona kafin na amsa mata da faɗin"ki yarda da ni wallahi ki ji rantsuwar ɗan musulmi ke nan ko? Ban taɓa ganin sa to ina ma za mu haɗu da shi mutumin da kika ce ba ya cikin ƙasar nan".
Da alama ta sama nutsuwa da kalaman da na furzar don ina jin sautin sauƙar numfashin da ta sauƙe.
"Na yarda da ke".
"To ba ta labarin abin da ake shiryawa yallaɓai ɗin namun?". Washe baki ta yi tamkar gonar auduga don na ga alamar tamkar babu maganar da yake sanya ta cikin tsananin farin ciki kamar batun Saddan da ta yi masa laƙabi da Oganta.
"So nake yi na je na sayo abubuwan gyaran jiki da kayan ƙamshi. Don so nake yi na shirya kaina kafin mu haɗu da shi, ina so wannan haɗuwar tamun ta zama abar tunawa a gare shi ta yadda ban bar shi masa tabon a cikin kwayansa".
Sai da na musguta kafin na ce"irin wannan kulawan da kuke ba wa junanku to me ye zai hana ku auri junanku?".
Ta taɓe baki"ai aure lokaci ne kuma ni ban shirya yin aure a wannan shekarun nawan ba. Kin gan ni nan sai na gama cin duniyarta da tsinken sakacen sannan na yi aure, mu yi rayuwar farin ciki da shi mu farantawa juna rai da zaran mun yi aure duk wannan soyayyar neman ta za mu yi mu rasa, duk marmarin junan da muke yi za mu koma jin haushin juna. Kin ga zaman auren nan zaman takura ne da rashin samun cikakken ƴancin kai mussamman aure a yanki arewacin ƙasar nan da za su san darajar mace ba sun mayar da matayensu tamkar bayin da ba su da ƴancin kansu, komai sai an ba ki izini za ki yi shi".
"To ai wannan abubuwan da kika lissafo ba ɗabi'ar ba ce, koyar wa addini ne cewar miji yana gaba da matarsa. Kuma ko fita za ki yi ƙofar gida sai da iznininsa".
Taɓe bakinta ta yi tana gyara ƙarin gashin doki da yake kanta kana ta ce"yanzu dai me ye kike so ki ce da ni?".
"Ku yi aure ya fi wannan rayuwar da kuke ciki. Ku ma kanki sai kun fi girmamawa da mutunta junanku".
"Saif".
"Ina jinka".
"Ya jikin nakan? Wallahi hankalina ya tashi sosai da na ji halin da kake ciki". Sai da ya cije naman leɓansa kafin ya ba shi da faɗin"da sauƙi fa yanzu yadda nake ji na ma zan iya wasan polo da ingarman doki, sa boda ƙarfin da nake ji a jikina".
Murmusawa Sultan ya yi kafin ya ce"daman har yanzu ka na fama da wannan lalular Saif? Na yi tunanin zuwa lokacin abubuwan sun yi sauƙi ba kamar da ba".
"Babu abin da ya sauya daga abin da ka sa ni Sultan". Shuru ya biyo bayan zancen Saif na ƙarshe. Sai can ya ce"wace ce yarinyar da ta ɗauki wayarka muka yi waya da ita? Don na san gidanku babu ɗiya mace".
A dake ya furta"ni ma ban san ta ba".
"Mu bar maganar wasa mana Saif, wace ce?".
"Ka riga da ba wa kanka amsa tun da tun farkon zancenka kai ma ka ce gidanmu babu É—iya mace".
Dariya sosai Sultan ya yi sai da ya tsagaita ya furta"any way ko ma dai wace ce, tabbas ta shiga cikin firgici ganin halin da kake ciki ka ji yadda take kuka kuwa tsakanin da Allah. Tambaya kuwa ta yi min ya kai sau ashirin akan za ka tashi kuwa? Na ce da ita in sha Allah, ba don ta zo akan lokaci ba Saif wataƙila da yanzu wani labarin ake yi ba wannan ba. Ko wace ce wannan yarinyar haƙiƙa ta ceto rayuwarka kuma ta ba da gagarumar gudummawa wajen tabbatar da numfashin da kake yi yanzu a cikin duniya, ka gode mata don ta cancanci hakan sosai".
Kit! Saif ya datse ƙiran ba tare ya ba wa Sultani damar amayar da sauran zancen da suke cikin bakisa ba. Ya zame daga zaunen da yake ya kwanta akan bayansa yana jan bargon ya lulluɓe rabin jikinsa, numfashi mai zafi ya furta daga bakinsa yana ɗan lumshe idanunsa sa boda ciwon kan da yake ji yana damun sa kaɗan kaɗan.
Ya daɗe kwance a wajen yana saƙa da warwara cikin ransa kafin ya tashi ya haura sama zuwa cikin ɗakinsa, wanka ya yi ya ɗauro alwala ya fito ya sanya farar doguwar jallabiya da aka yi wa ado da zare launin ruwan zuma mai ƙyalli da ɗaukar ido, ƙaramar hula ya sanya a kansa ya shimfiɗa sallaya ya gabatar da sallan zuhur tare na sallan asr yana iddarwa ya ɗauko alƙur'ani ya soma karantawa.
Dole ne ya tursasa masa rufe alƙur'anin ya ajiye a gefe sa boda rawar da jikinsa yake yi tamkar mazari. Ya kunna ƙira'an Sheikh Ahmad Suleiman a cikin wayarsa ya ajiye, a nan kan sallayan ya kwanta take wani bacci mai nauyin gaske ya yi awon gaba da shi ba tare da ya shirya wa hakan ba.
Tun da na fito daga sashinsa na nufi hanyar gate ina tafiya a hankali tamkar babu laka a jikina, ina dab da fita na tsinkayo muryar Baba Mai gadi.
"Ƴar nan lafiya kuwa na ga kamar kuka kike yi?". Na yi saurin goge fuskana da ban san lokacin da wasu sabbin hawayen suka fito ba, na waigo tare da duƙawa na gaishe shi, ya amsa yana bi na da kallon tuhumar son gano abin da yake faruwa da ni. Ya zauna akan bencin da yake wajen ni ma na je na zauna.
"Ko dai cikin gidan ne babu lafiya? Don É—azu na ga Saifullahi ya fito daga cikin gidan ya nufi sashinsa cikin wani irin yanayi, wanda har ina tsoron har hakan ya tasar masa da ciwon da yake damunsa".
Na sauri na ce"wani irin ciwo ke nan Baba?". Ya yi ɗan jim kafin can ya ce"tun yana ƙarami yake fama da wani irin ciwo ga shi nan dai kamar aikin aljanu ko iskokai. A duk lokacin da ransa ya ɓaci ko kuma ya yi cacar baki da wani ke wani lokacin ma ko dogon zancen ya yi sai ki ga kawai ya yanke jiki ya faɗi jikinsa ya sanƙare haka zai koma ba shi da maraba da gawar da rai ya yi bankwana da gangar jikinsa, sai ta yi masa karatun alƙur'ani kafin yake dawowa daidai kuma da zaran ya tashi zai koma kamar ba shi ba".
Æoyayyan ajiyan zuciya na sauÆ™e ina jin Æ™aran da Æ™irjina yake yi tamkar zai faso allon Æ™irjin ya fito waje ya taka rawar disko. Sai da na harhaÉ—o kalaman kafin na yi nasarar cewa"Allah ya na shi lafiya, Baba bari na je gida na dawo".
"Amin ya Allah, to Æ´ar nan a gaishe da mutanan gidan".
"Za su ji in sha Allah". Na amsa da shi yayin da nake tashi daga kan bencin, tafiya kawai nake yi ba tare da na san inda nake cilla ƙafafuna ba ina tafe ina tunani tare da nazarin kalaman Baba mai gadi. Saura ƙiris wani mai napep ya kwashe ni Allah a rufa asiri, ai kuwa ya fito ya balbale ni da bala'i da masifa tamkar zai yi aron baki da ƙyar ya haƙura ya ja napep ɗinsa ya tafi bayan ya gama wurwurga mini ashariya tamkar ya hana jini da dangin maguzawa. Sai yamma lilis na iso gida lokacin ko wacce budurwar dake cikin gidan ta ci ƙwaras tana ƙoƙarin fice wa wajen harkanta. Gidan ya yi shuru sosai ina shigowa na kai duba na ƙofar ɗakin Hajiya Babba na ga ƙofar ɗakin a rufe an buga masa kwaɗo. Na lura cikin kwanakin nan ba na ganin La'aniyatu a cikin gidan nan kuma na rasa wanda zan tambaya.
Har na ɗauki hanyar ɗakinmu sai kuma na fasa don har cikin raina ba na ƙaunar haɗa ido da Sha'awanatu don har yanzu ban huce daga abin da ya faru ba. Ganin ƙofar ɗakin Zinariya a buɗe ya ba ni ƙwarin gwiwar faɗa wa cikin ɗakin.
Na iske ta tana kwance akan katifarta tana bacci na zauna a gefen tana dukan ƙafarta har sai da ta shi, ganin ni ce ya hana ta ƙarisa ashariyar da ta danno.
"Au wai ke ce?".
"Da waye kike yi tunani?". Ba ta amsa mini ba har sai da ta tashi ta zauna ta ce"kin dawo daga aikin wahalar ke nan?". Na yi murmushi har sai da haƙwarana suka bayyana"aikin rufa wa kai asiri dai ko?". Ta taɓe baki ba tare da ta ce da ni ko kanzil ba sai ma sauya akalar zancen da ta yi
"Ki na da lokaci ki raka ni kasuwa?".
"Duk a cikin shirin tarban Yallaɓai ɗin ne?". Ta yi fari da idonta"ƙwarai kuwa". Na gyaɗa kaina"Allah ya bar ƙauna Madam ta gaban goshin Saddam". Caraf bakina ya yi furucin ba tare ta yi shawari da zuciyata ba.
"Saddam kuma? Ina kika san sunansa?".
Cike da dabara na wayince"kar ki daina basirar duk wata macen da kika ga ni a cikin harkan bariki".
[12/9, 6:43 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
___________________________________________
Page 6ï¸âƒ£5ï¸âƒ£
Tun da na yi zancen take bi na da kallo da mamakin zancen ya tilasta mata wartsakewa daga baccin da take yi. Ta rarumo hannuna ta riƙe gam"sanar da ni inda kika san sunansa don Allah". Na saki wani shu'umin murmushin gefen baki kafin na furta"ki fa kwantar da hankalinki na canza ne kawai. Sai kuma aka yi dace sunan ya zo daidai". Ta yi jim tana ta bi na da kallo kafin can ta ce"kin tabbata?".
Na yi fari da idona kafin na amsa mata da faɗin"ki yarda da ni wallahi ki ji rantsuwar ɗan musulmi ke nan ko? Ban taɓa ganin sa to ina ma za mu haɗu da shi mutumin da kika ce ba ya cikin ƙasar nan".
Da alama ta sama nutsuwa da kalaman da na furzar don ina jin sautin sauƙar numfashin da ta sauƙe.
"Na yarda da ke".
"To ba ta labarin abin da ake shiryawa yallaɓai ɗin namun?". Washe baki ta yi tamkar gonar auduga don na ga alamar tamkar babu maganar da yake sanya ta cikin tsananin farin ciki kamar batun Saddan da ta yi masa laƙabi da Oganta.
"So nake yi na je na sayo abubuwan gyaran jiki da kayan ƙamshi. Don so nake yi na shirya kaina kafin mu haɗu da shi, ina so wannan haɗuwar tamun ta zama abar tunawa a gare shi ta yadda ban bar shi masa tabon a cikin kwayansa".
Sai da na musguta kafin na ce"irin wannan kulawan da kuke ba wa junanku to me ye zai hana ku auri junanku?".
Ta taɓe baki"ai aure lokaci ne kuma ni ban shirya yin aure a wannan shekarun nawan ba. Kin gan ni nan sai na gama cin duniyarta da tsinken sakacen sannan na yi aure, mu yi rayuwar farin ciki da shi mu farantawa juna rai da zaran mun yi aure duk wannan soyayyar neman ta za mu yi mu rasa, duk marmarin junan da muke yi za mu koma jin haushin juna. Kin ga zaman auren nan zaman takura ne da rashin samun cikakken ƴancin kai mussamman aure a yanki arewacin ƙasar nan da za su san darajar mace ba sun mayar da matayensu tamkar bayin da ba su da ƴancin kansu, komai sai an ba ki izini za ki yi shi".
"To ai wannan abubuwan da kika lissafo ba ɗabi'ar ba ce, koyar wa addini ne cewar miji yana gaba da matarsa. Kuma ko fita za ki yi ƙofar gida sai da iznininsa".
Taɓe bakinta ta yi tana gyara ƙarin gashin doki da yake kanta kana ta ce"yanzu dai me ye kike so ki ce da ni?".
"Ku yi aure ya fi wannan rayuwar da kuke ciki. Ku ma kanki sai kun fi girmamawa da mutunta junanku".