← Book details Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 72

Sashe 60

Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Na ji zan tafi amma don Allah ki ba ni ko da mintuna goma daga cikin lokacinki, ki saurare ni ki ji bayanin da zan yi miki. Ban zo wajen da nufin yaudara ko cutar da ke ba hasalima....".
Na datse numfashinsa"ba zan taɓa sonka ba Saifullah, me yasa ba ka duba matsayina da na ka ba da suka yi hannun riga. Ƙwarya ta bi ƙwarya idan ta bi alwashi ai fashe wa za ta yi".
"Na ji na yarda ba za ki so ni, amma ni dai ki ba ni dama ki saurare ni".
Hannayena na saka na toshe kunnuwana da shi yayin da hawaye suke zuba daga idanuna kamar bakin indararo, ganin ba zan iya jimirin sauraron zantukansa da suke barazanar raba ni da nutsuwata ba, hakan ya tilasta mini juya wa na shige cikin gida da gudu.
Na ci karo da Anty Sawwama ta na fito wa daga banɗakin ina jin ta tana tambayata ko lafiya na shigo gida da kuka, amma ban iya amsa mata ba. Kai tsaye ɗakin kwanana na nufa na kwanta ina kuka, babu irin tambayoyin da ba ta yi mini ba amma na dage ina ce mata babu komai ba don ta yarda ba haka ta haƙura ta ƙyale ni.

Daren ranar ban iya runtsa wa sai da dare ta raba cikin baccin na ji ana ƙiran sunana na tashi na zauna ina ƙara kasa kunne na ji dai tabbas sunana ake ƙira a tsakar gidan. Zumbur na yi na miƙe ina murtsike idanuna na buɗe ƙofar ɗakin na fito waje inda nake jin sautin ƙiran yana tashi.
Ina fito wa na ga tsakar gidan ya yi haske sosai tamkar ba dare ba, na kai dubana inda nake ji sautin yana tashi idanuna suka sauƙa akan fuskan Hajiya Babba. Take ilahirin jikina ya soma rawa tamkar ana jona mini wutan lantarki na nuna da yar manuniyar yatsana bakina ya na rawa na ce"Hajiya Babba ke ce ki ka biyo ni nan?". Lu na ji na yi baya na zube a ƙasa yayin da kaina ya bugu da dutse, tun idanuna suna gano mini fuskarta dishi-dishi har sai da suka rufe gabaɗaya, daga lokacin ban ƙara sanin inda kaina yake ba balle fahimtar abubuwan da suke wanzuwa.
[12/24, 3:41 PM] Maimunatu Iyam🥰: *DAFIN HARSHE*

©️ Maimuna Tijjani Iyam

___________________________________

Page 7️⃣8️⃣

A hankali na soma buɗe idanuna da suka yi mini nauyin gaske kaina ya yi dum tamkar wacce aka yi wa ajiya dutse, hankalina yana dawowa jikina abin da ya faru ya dawo mini cikin kwanyata tiryan-tiryan, take na zabure ina rafka salati tare da runtse idanuna da matuƙar ƙarfi ina ta batutuwa mara sa kan gado.
"Hajiya Babba me ye na yi miki za ki biyo ni har cikin gidan nan? A zamana da ke ko da wasa ban cutar da ke ba don Allah ke ma kar ki cutar da ni ko da kwantankwacin misƙala zarratin ne". Ji da na yi an dafo kafaɗana shi ya dawo da ni cikin hyayancina na buɗe runtsatstsun idanuna na kafe Anty Sawwama da su da take zaune kusa da ni, ganinta kusa da ni ya sani ƙanƙame ta a jikina tsaf ina zubar da hawaye tamkar an kunna burɗaɗɗan fanfo.
"Uwata ki nutsu ki kwantar da hankali, babu wani abun da zai faru face alkhairi da iznin Allah. Babu wanda ya isa ya cutar da ke duk abin da kika ga ya faru da ke to daman haka Allah ya ƙaddara zai faru". Luf na yi a jikinta ina mayar da numfashi tamkar wacce ta yi wani gagarumin aikin wahala, mun daɗe a haka kafin ta ɗago ni daga cikinta ta tambaye ni abin da yake faru na kwashe komai na sanar da ita, haƙiƙa na hangi tashin hankali da tsoro kwance a cikin ƙwayan idanunta sai dai ta dannan duk yanayin da take ciki.

A cikin daren ta ƙira Yaya Alhassan ya zo ta sanar da shi komai, ina kwance na ɗaura kaina akan cinyarta yayin da na lumshe idanuna tamkar mai bacci sai dai a farke nake don ina sauraron dukkan abin da suke tattaunawa.
Cike da tarin damuwan da yake tattare da furucin bakinta Anty Sawwama take faÉ—in"tsoro É—aya kar wannan matar ta sabauta yarinyar nan, ina tsoron har ta juya mata hankalinta ko ma ta raba ta da shi gabaÉ—aya, don irin waÉ—annan matan ababen tsoro ne".
"Umma in sha Allah babu abin da ta isa ta yi wa Amatullah, gobe idan Allah ya kai mu zan je har can garin Jafarin mu yi ta ni da ita, in ta kama ma har ƴan sanda zan saka cikin lamarin". Anty Sawwama ta yi hanzarin taran numfashinsa"kar ka sake ka aikata wannan kuskuren Alhassan. Wani hujja kake da shi da za ka je har cikin gidan ka tunkare ta da wannan zancen? Ka san girman irin wannan lamarin kuwa? Hmm! Addu'a ita kaɗai ce mafita a gare mu". Shuru Yaya Alhassan ya yi har ta kai aya bai ce komai ba sai can ya ce"to yanzu Umma mene ne abin yi? Me ya kamata mu yi?". Ta saki sakakken ajiyar zuciyan da har sai da na ji sautin fitarsa kafin ta sama damar furta abin da yake kwance a ƙasan ranta.

"Ina tunanin idan Allah ya kai mu gobe mu ƙira Malamai su zo, a kewaye mana ƙur'ani a cikin gidan nan, sannan mu riƙi addu'o'i da azkar don shi ne kawai mafita".

Cike da gamsuwa ya ce"in sha Allah yadda kika ce Umma hakan za a yi, bari na je na kwanta Allah ya tashe mu lafiya".
"Amin". Ta amsa da shi da hakan ya ba shi damar tashi ya fita, ni kam dole ta sanya Anty Sawwama kwanan a nan tare da ni sa boda yadda duk bayan mintuna nake firgita har sai an riƙe ni. Washe gari da sassafe Yaya Alhassan ya nemo Malamai suka zo suka yi sauƙan alƙur'ani a cikin domin kariya da kuma fin ƙarfin duk wani aljanni ko iska har ma da wani mai mungun nufi, da mummunan ƙuduri. Kwana biyu na jera a jere ba na samun bacci duk da kuwa yadda aka zage da addu'a da roƙon Allah, Yaya Alhassan har yanka ya sa aka yi mini kafi lamarin ya lafa sai dai cikin ɗan kwanaki na rame sosai na fita daga cikin hayyacina.

A ranar wani labara ina kwance a ɗaki ina karanta littafin ƁOYAYYEN MANUFA, labarin zazzafan soyayyar Aishatu da Abdulhamid da ya karo da ƙaddarar da ta yi silar tarwatsa dukkan gini da tubalin da suka gina soyyayarsu a kai, Amir ya shigo ya kawo mini sabuwan waya ƙarama har da layi a cikinta, ya kuma shaida mini cewar Yaya Alhassan ne ya ce ya kawo min don ba son ina amfani da wannan wayar da na zo na ita ya kuma ce ma na ba ta ita. Ban yi musu ba na tashi na ɗauka wayar daman ko layi babu a cikin ta, memory ne kuma shi ma tunin na cire sa tun lokacin da Yaya Alhassan ya umarce ni da na goge wannan sautin muryar, na naɗe sa a cikin takarda na sanya a cikin jaka yayin na ɓoye sa a can ƙasan kayana.
Tare da shi muka fito falo ta juya wayar a hannuna yayin da nake ba shi saƙon godiya ya isarwa Yaya Alhassan kafin ya dawo gidan na yi masa na mussamman, turus muka yi ganin baƙi a cikin falon tare da Anty Sawwama. Muhammad Taufik ne tare da Saifullah da suke gaishe da Anty Sawwama ciki girmamawa ta na amsawa fuskarta kamar gonar auduga. Juya ciki na yi don ko mayafi babu a jikina na fito na zauna a bakin katifa yayin da na faɗa cakwakiyar tunanin dalilin zuwan su gidan a wannan lokacin.

Ban yi nisa cikin tunanin ba Amir ya É—ago labulen É—akin fuskarsa a sake ya ce"ki fito ku gaisa".
Na murtuƙe fuskana"Mu gaisa kuma Yaya Amir? Ni fa ina tunanin lokaci ya yi da za du dakatar da mutanen nan daga zuwa cikin gidan nan". Jijjiga kansa ya yi yana ɗan murmushi ya ce"yanzu dai ki yi haƙuri ki fito ku gaisa". Ya na dasa aya a zancen ya saki labulen ya juya ya fita, ina ta ƙunƙunai na ɗauko hijabi na saka na fito falon lokacin da na fito na iske Anty Sawwama ma ta tashi daga cikin falon. Can gefe na zauna kaina a ƙasa na gaishe su suka haɗa baki wajen amsawa kafin shuru ya biyo bayan zancena na ƙarshe. Har sai da na ƙosa da zaman kafin na tsinkayo muryar Muhammad Taufik yana faɗin"Amatullah mun zo gaisuwa ne tare da neman iri, na san ba ki manta zancen da Saifullah ya zo miki da shi ba kwanakin baya ya sanar da ni cewar har yanzu ba ki ba shi amsa ba hasalima ba ki saurare shi ba. Ina mai tabbatar miki da cewar Saif mutumin kirki ne duk inda ake neman mutum na ƙwara to ya kai wannan matakin a iya tsawon zamana da shi ban taɓa jin ya buɗe baki ya furta yana son wata mace har ya yi burin aurenta ba sai ke, ke ce mace ta farko a cikin labarin rayuwarsa ke ce mace ta farko da ta fara karya alƙadarinsa. Don Allah ki ba shi dama ko da sau ɗaya ne ki ba shi damar ya yi yaƙi domin tabbatar miki da ƙarfin soyyaya da ƙaunar da yake gwada miki". Tun da ya soma zancen nake kallonsa da wutsiyar idanuna ina jin wani abu yana tasowa tun daga cikin zuciyata yana tokare mini ƙirjina.

Take! Ranar kuwa fara ganin lokacin zan tafi islamiyya ya soma dawo mini cikin kwanyata, na yi saurin tare da hawayen da suke shirin ɓalle mini.
"Mun yi tunanin ko akwai wanda kike magana da shi ko kuma an riga da an yi miki miji shi yasa ba ki saurare shi, amma yanzu da muka zuwa Anty da maganan ta tabbatar babu ko ɗaya, kuma ta ba shi damar ya nema amincewanki idan har kin amince shi kenan". Ban san dalili ba haka kawai tun ya ci gaba da maganan na ji hawayen da nake ta ƙoƙarin riƙe wa sun ɓalle suka fara kwaranya.
Chapter 60 · 0% Book details