Sashe 25
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka kawai na wayi gari ina ji na cikin wani irin karsashi a jikina, wanda na danganta hakan da karatun alƙur'anin da na yi ta yi bayan na yi sallan asubahi. Na tisa haddan da yake kaina sosai har sai da na ji wani nutsuwa ya lulluɓe mini rai da ruhina. Sai da na ɗebo ruwa na yi wanka na mayar da kayan da yake jikina na duba ko'ina na rasa abin da zan tauna a cikin ɗakin, na gama cinye duk siyayyar da Hajiya Muhibbat ta yi mini kat. Numfashi na ja na fesar kafin na yi shirin tafiya wajen aikin zan fita na ji sautin da ya tirsasa mini tsayawa.
"Madam fita za ki yi ne?".
Na waigo na yi mata kallo guda tana kwance akan katifarta da ban ma san sa'ilin da ta dawo ba daren jiya sai wayen gari na yi na gan ta cikin É—akin.
"E ko na tsaya za ki aike ni ne?".
"To ikon Allah wai na zaune ya faɗi. Abin ai bai kai haka ba, dama na ga muna zaune a ɗaki ɗaya ne akwai haƙƙin maƙwabta a kanmu ai ko?". Na bi ta da wani kallo don har yanzu ban manta zafafan kalaman da ta yaɓa mini ba ranar farko da ta zo cikin ɗakin.
"Tambaya kike yi ko neman sani?".
"Duk wanda kika ɗauka daga cikin biyun daidai ne". Ban amsa mata ba na ja tsaki na fice daga cikin ɗakin ina jin haushin abin da ta yi mini har yanzu a cikin raina. Ina fitowa na yi kiciɓus da zinariya tana ƙoƙarin shiga ɗakin na ƙirƙiri murmushin dole na aza a bisa fuskana.
"Barka da safiya ranki ya daÉ—e".
"Ai ke ce ranki ya daɗe, dama na zo na ƙara duba jikin nakin ne. Ban saman shigowa ba".
"Ai na je na iske ki na waya sai kuma daga nan ban dawo ba. Na gode sosai Allah ya saka da alkhairi....". Kafin na rufe bakina na ji ta rumgume ni tsam a jikinta kafin na yi aune na ji hannayenta a gadon bayana tana shafa wa har zuwa ƙunguna. Jikina na mutu murus na kasa cewa da ita komai kamar yadda na gaza hana ta yawo da hannunta da take yi a cikin jikina.
"Bari na bar ki haka tun da na ga kamar fita za ki yi ko?".
Zallar ruwan mamakin da ta shayar da ni ya hana ni amsa mata cikin kalmomin da bakin kan iya furta wa illa gyaÉ—a mata kaina da na yi.
"To sai kin dawo idan kin dawo sai ki shigo mu yi hira". Na kuma gyaɗa mata kaina a karo na biyu ta sakar mini wani shu'umin murmushin yayin da take ɗaukar hanyar koma wa cikin ɗakinta. Na fita da kallo ƙirjina yana buga wa tamkar zai faso allon ƙirjina ya bayyano waje ya taka rawar disko, na daɗe tsaye a wajen kafin na ja sanƙararrun ƙafafuna da nake jin su tamkar ba za jikin gangar jikina na fice daga cikin gidan.
Ina tafiya ina tunani har na isa ƙofar gidan ina jin wani masifaffen yunwa hancin cikina sai kuka suke yi da neman agaji, na ƙwanƙwasa gate ɗin Baba mai gadi ya fito ya buɗe mini na durƙusa har ƙasa na gaishe shi ya amsa mini fuskarsa tamkar gonar auguda.
"Kin iso ko?". Na gyaÉ—a masa kaina alamar e.
"To madalla Allah ya taimaka ya yi jagora".
"Amin ya Allah". Na amsa da shi yayin da nake shiga cikin gidan ina shiga na hango motoci guda uku a cikin parking space, ɗayan Kam ko a ina na ganta zan gane ta don motar Hajiya Muhibbat ce. Ɗayan kuma motar Saif ne ɗayar ce baƙuwa amma tabbas a gare ni ba baƙuwa ba ce don ba yau ne rana ta farko da na fara ganinta ba. Ƙirjina ya harba da ƙarfin Rabbussamawati da hakan ya tilasta mini runtse idanuna Ina karanton a'uziya a cikin raina.
"Ƴarta lafiya kuma na ga kin tsaya a nan, ba ki shiga cikin gidan ba?".
"Baba wannan motar baƙo aka yi a cikin gidan nan?".
Ya washe bakinsa kafin ya amsa mini cikin faɗin"wannan motar baƙon Saifullahi ne, da ya zo da yammacin jiya. Yaron kirki ne matuƙa ga girmama manya gami da tsantsan tarbiyya daɗin daɗawa kuma ga nutsuwa da kawaici".
"Tabbas ya cika mutumin kirki tun da har ya sama yabo daga bakin uba na gari kamar ka".
Ya washe bakinsa tamkar wanda aka yi wa wani babban kyauta"duk inda ake neman yaron kirki wannan baƙon ya zarce duk tunanin mai tunani. Ni ɗin nan idan ya zo cikin gidan na irin girman da yake ba ni na daman ne, in ya shigo ya ganni ina wani aikin kuwa sai ya karɓa ya yi min babu ruwansa da matsayinsa, matakin karatunsa ko kuma azurkinsa".
Na riƙe haɓata"dole na zo a ba ni labarin wannan baƙo".
"Ai kuwa za ki sha labari, don duk suna makaranta a nan gidan yake hutunsa har sai sun koma".
"In sha Allah zan zo na sha labari". Daga haka na bar wajen na ƙarisa shiga cikin gidan, na tsaya a ƙofar falo ina ta zabga sallama har baki uku ba a amsa ba sai a na huɗun Ayan ya buɗe ƙofar ya fito, na fafaɗaɗa fara'ar fuskarta kafin na ce da shi"ina kwana".
Ya tsaya ya yi sakeke yana kallona kafin can ya ce"ki shigo Ummin tana ciki". Murmushi na sakar masa na riƙo hannunsa muka shiga cikin falon.
Na tsuguna har ƙasa na gaishe da Hajiya Muhibbat da na iske zaune a falon tana danna wayarta, yayin da Aryan take zaune a kusa da ita yana wasa da motar da yake hannunsa.
"Lafiya ƙalau kin tashi lafiya?".
"Lafiya alhamdulillah ranki ya daÉ—e".
"Lafiya jiya kika tafi babu sanarwa sai aikowa na yi a ƙira ki aka ce ba kya nan?".
"Hajiya ba na jin daÉ—i ne shi yasa na tafi, amma tuba nake yi".
"Ba damuwa Allah ya ƙara sauƙi. Ki shiga kicin ku ci gaba da aikin don yau mu na da baƙo na musamman a cikin gidan nan". Kaina kawai na gyaɗa mata na tashi na yi hanyar kicin ɗin na tarar da Altine a tsaya ta juya wa ƙofa baya tana waya. Na yi gyaran murya da hakan ya ankarar da ita wanzuwa ta a cikin kicin ɗin, a firgice ta waigo tana datse ƙiran.
"Ke kuma me ye kike yi a nan? Yaushe kika shigo?".
Ruɗewan da ta yi lokaci guda shi ya fi komai ba ni mamaki, sai na ƙariso cikin kicin ɗin kafin na ce"yanzu na shigo na tarar ki na waya. Ina kwana mun tashi lafiya?".
"Lafiya". Ta amsa mini a daƙile tamkar wacce aka yi wa dole, ba ta ƙara bi ta kaina ba ta ci gaba da abin da take yi. Dankalin turawa take soya wa da ƙwai gefe guda kuma tana haɗa dafa shayi da ya sha kayan yaji dangin su citta da kananfari ƙamshi ya buɗe ko'ina.
Ina ta tsaye ba ta ce da ni ga abun da zan yi ba har sai da na ji ƙafafuna sun gaji sun yi sanyi ƙalau. Sai da na tabbatar da cewa ba ta tanka mini na half ƙafafuna na isa wajen da ake ajiye kayan abinci na ɗebo fulawa zan tankaɗe ta dakatar da ni"me ye haka kike ƙokarin aikata wa?". Ba tare da na kalle ta ba na amsa da faɗin"wainar fulawa zan soya".
"Wainar fulawa kuma?". Ta maimaita cikin isa da taƙama kafin ta zarce da cewa"wani irin wainar fulawa kuma? Bayan ga abincin karin kumallo nan ina girka wa ko ba kya gani ne?". Ban ce da ita uffan ba hakan bai hana ta ci gaba da maganar ba tamkar mai amayar da wuta.
"Babu wani wainar fulawan da za a yi a cikin gidan nan tun da ga abinci nan na girka. Duk wanda ba zai ci ba sai ya wuni da yunwa ai yunwa ba uwar kowa ba ce kuma ba a fushi da abinci ko ka yi ma kai ne a wahala".
"Ai na ji Hajiya ta ce akwai babban baƙo a cikin gidan kuma ta ba da lasisin a girka duk abin da ya kamata don a faranta masa. Laifi ne don na girka wannan?". Na ƙare zancen da alamar tambaya, lamarin da ya fusata ta ainun ta yi watsi wani kallo tamkar za ta kai mini bugu tana gallo mini harara kamar idanunta za su faɗo ƙasa.
"Sai kuma aka ce da ke baƙo irin baƙin da kika saba ji da gani ne ko? To wannan baƙon babban mutum ne da ya fito daga gidan manya, ina mai tabbatar miki da cewar ko kallon wainar fulawan nan ba zai yi ba balle ya sa shi akan harshensa".
"Sanin daga gidan da ya fito ne ya sa zan yi masa wainar fulawa, don ina da yaƙinin wannan dankali da shayin da kika yi abubuwa ne da kullum yake gani kuma yake cinsu. Amma ina da yaƙinin wannan wainar fulawan zai zama sabon abu a wajensa". Kafin na gama kammala zancen kawai na ga ta ɗaga hannu za ta zabga mini mari na yi hanzarin riƙe hannunta tare da jefa idanuna a cikin na ta.
"Kar ki kuskura ki yi gangancin É—aura hannunki a jikna da sunan mari. Don abin da zai bi yo bayan hakan daga ni har ke ba zai mana daÉ—i ba". Kafin ta ce wani abu Hajiya Muhibbat ta shigo cikin kicin É—in ta iske mu a haka.
"Me yake faruwa na gan ku kun tsaya cirko-cirko?".
"Babu komai Hajiya, da inna fere dankalin nan ne na kuskure hannuna shi ne take so ta É—auke min wajen".
Altine ta kora mata bayanin da ta ƙirƙire shi a take a wajen, ban ce da ita komai hasalima ko hannun ta ban yi ba.
"To Allah ya kiyaye gaba. Wannan fulawar fa?".
"Madam fita za ki yi ne?".
Na waigo na yi mata kallo guda tana kwance akan katifarta da ban ma san sa'ilin da ta dawo ba daren jiya sai wayen gari na yi na gan ta cikin É—akin.
"E ko na tsaya za ki aike ni ne?".
"To ikon Allah wai na zaune ya faɗi. Abin ai bai kai haka ba, dama na ga muna zaune a ɗaki ɗaya ne akwai haƙƙin maƙwabta a kanmu ai ko?". Na bi ta da wani kallo don har yanzu ban manta zafafan kalaman da ta yaɓa mini ba ranar farko da ta zo cikin ɗakin.
"Tambaya kike yi ko neman sani?".
"Duk wanda kika ɗauka daga cikin biyun daidai ne". Ban amsa mata ba na ja tsaki na fice daga cikin ɗakin ina jin haushin abin da ta yi mini har yanzu a cikin raina. Ina fitowa na yi kiciɓus da zinariya tana ƙoƙarin shiga ɗakin na ƙirƙiri murmushin dole na aza a bisa fuskana.
"Barka da safiya ranki ya daÉ—e".
"Ai ke ce ranki ya daɗe, dama na zo na ƙara duba jikin nakin ne. Ban saman shigowa ba".
"Ai na je na iske ki na waya sai kuma daga nan ban dawo ba. Na gode sosai Allah ya saka da alkhairi....". Kafin na rufe bakina na ji ta rumgume ni tsam a jikinta kafin na yi aune na ji hannayenta a gadon bayana tana shafa wa har zuwa ƙunguna. Jikina na mutu murus na kasa cewa da ita komai kamar yadda na gaza hana ta yawo da hannunta da take yi a cikin jikina.
"Bari na bar ki haka tun da na ga kamar fita za ki yi ko?".
Zallar ruwan mamakin da ta shayar da ni ya hana ni amsa mata cikin kalmomin da bakin kan iya furta wa illa gyaÉ—a mata kaina da na yi.
"To sai kin dawo idan kin dawo sai ki shigo mu yi hira". Na kuma gyaɗa mata kaina a karo na biyu ta sakar mini wani shu'umin murmushin yayin da take ɗaukar hanyar koma wa cikin ɗakinta. Na fita da kallo ƙirjina yana buga wa tamkar zai faso allon ƙirjina ya bayyano waje ya taka rawar disko, na daɗe tsaye a wajen kafin na ja sanƙararrun ƙafafuna da nake jin su tamkar ba za jikin gangar jikina na fice daga cikin gidan.
Ina tafiya ina tunani har na isa ƙofar gidan ina jin wani masifaffen yunwa hancin cikina sai kuka suke yi da neman agaji, na ƙwanƙwasa gate ɗin Baba mai gadi ya fito ya buɗe mini na durƙusa har ƙasa na gaishe shi ya amsa mini fuskarsa tamkar gonar auguda.
"Kin iso ko?". Na gyaÉ—a masa kaina alamar e.
"To madalla Allah ya taimaka ya yi jagora".
"Amin ya Allah". Na amsa da shi yayin da nake shiga cikin gidan ina shiga na hango motoci guda uku a cikin parking space, ɗayan Kam ko a ina na ganta zan gane ta don motar Hajiya Muhibbat ce. Ɗayan kuma motar Saif ne ɗayar ce baƙuwa amma tabbas a gare ni ba baƙuwa ba ce don ba yau ne rana ta farko da na fara ganinta ba. Ƙirjina ya harba da ƙarfin Rabbussamawati da hakan ya tilasta mini runtse idanuna Ina karanton a'uziya a cikin raina.
"Ƴarta lafiya kuma na ga kin tsaya a nan, ba ki shiga cikin gidan ba?".
"Baba wannan motar baƙo aka yi a cikin gidan nan?".
Ya washe bakinsa kafin ya amsa mini cikin faɗin"wannan motar baƙon Saifullahi ne, da ya zo da yammacin jiya. Yaron kirki ne matuƙa ga girmama manya gami da tsantsan tarbiyya daɗin daɗawa kuma ga nutsuwa da kawaici".
"Tabbas ya cika mutumin kirki tun da har ya sama yabo daga bakin uba na gari kamar ka".
Ya washe bakinsa tamkar wanda aka yi wa wani babban kyauta"duk inda ake neman yaron kirki wannan baƙon ya zarce duk tunanin mai tunani. Ni ɗin nan idan ya zo cikin gidan na irin girman da yake ba ni na daman ne, in ya shigo ya ganni ina wani aikin kuwa sai ya karɓa ya yi min babu ruwansa da matsayinsa, matakin karatunsa ko kuma azurkinsa".
Na riƙe haɓata"dole na zo a ba ni labarin wannan baƙo".
"Ai kuwa za ki sha labari, don duk suna makaranta a nan gidan yake hutunsa har sai sun koma".
"In sha Allah zan zo na sha labari". Daga haka na bar wajen na ƙarisa shiga cikin gidan, na tsaya a ƙofar falo ina ta zabga sallama har baki uku ba a amsa ba sai a na huɗun Ayan ya buɗe ƙofar ya fito, na fafaɗaɗa fara'ar fuskarta kafin na ce da shi"ina kwana".
Ya tsaya ya yi sakeke yana kallona kafin can ya ce"ki shigo Ummin tana ciki". Murmushi na sakar masa na riƙo hannunsa muka shiga cikin falon.
Na tsuguna har ƙasa na gaishe da Hajiya Muhibbat da na iske zaune a falon tana danna wayarta, yayin da Aryan take zaune a kusa da ita yana wasa da motar da yake hannunsa.
"Lafiya ƙalau kin tashi lafiya?".
"Lafiya alhamdulillah ranki ya daÉ—e".
"Lafiya jiya kika tafi babu sanarwa sai aikowa na yi a ƙira ki aka ce ba kya nan?".
"Hajiya ba na jin daÉ—i ne shi yasa na tafi, amma tuba nake yi".
"Ba damuwa Allah ya ƙara sauƙi. Ki shiga kicin ku ci gaba da aikin don yau mu na da baƙo na musamman a cikin gidan nan". Kaina kawai na gyaɗa mata na tashi na yi hanyar kicin ɗin na tarar da Altine a tsaya ta juya wa ƙofa baya tana waya. Na yi gyaran murya da hakan ya ankarar da ita wanzuwa ta a cikin kicin ɗin, a firgice ta waigo tana datse ƙiran.
"Ke kuma me ye kike yi a nan? Yaushe kika shigo?".
Ruɗewan da ta yi lokaci guda shi ya fi komai ba ni mamaki, sai na ƙariso cikin kicin ɗin kafin na ce"yanzu na shigo na tarar ki na waya. Ina kwana mun tashi lafiya?".
"Lafiya". Ta amsa mini a daƙile tamkar wacce aka yi wa dole, ba ta ƙara bi ta kaina ba ta ci gaba da abin da take yi. Dankalin turawa take soya wa da ƙwai gefe guda kuma tana haɗa dafa shayi da ya sha kayan yaji dangin su citta da kananfari ƙamshi ya buɗe ko'ina.
Ina ta tsaye ba ta ce da ni ga abun da zan yi ba har sai da na ji ƙafafuna sun gaji sun yi sanyi ƙalau. Sai da na tabbatar da cewa ba ta tanka mini na half ƙafafuna na isa wajen da ake ajiye kayan abinci na ɗebo fulawa zan tankaɗe ta dakatar da ni"me ye haka kike ƙokarin aikata wa?". Ba tare da na kalle ta ba na amsa da faɗin"wainar fulawa zan soya".
"Wainar fulawa kuma?". Ta maimaita cikin isa da taƙama kafin ta zarce da cewa"wani irin wainar fulawa kuma? Bayan ga abincin karin kumallo nan ina girka wa ko ba kya gani ne?". Ban ce da ita uffan ba hakan bai hana ta ci gaba da maganar ba tamkar mai amayar da wuta.
"Babu wani wainar fulawan da za a yi a cikin gidan nan tun da ga abinci nan na girka. Duk wanda ba zai ci ba sai ya wuni da yunwa ai yunwa ba uwar kowa ba ce kuma ba a fushi da abinci ko ka yi ma kai ne a wahala".
"Ai na ji Hajiya ta ce akwai babban baƙo a cikin gidan kuma ta ba da lasisin a girka duk abin da ya kamata don a faranta masa. Laifi ne don na girka wannan?". Na ƙare zancen da alamar tambaya, lamarin da ya fusata ta ainun ta yi watsi wani kallo tamkar za ta kai mini bugu tana gallo mini harara kamar idanunta za su faɗo ƙasa.
"Sai kuma aka ce da ke baƙo irin baƙin da kika saba ji da gani ne ko? To wannan baƙon babban mutum ne da ya fito daga gidan manya, ina mai tabbatar miki da cewar ko kallon wainar fulawan nan ba zai yi ba balle ya sa shi akan harshensa".
"Sanin daga gidan da ya fito ne ya sa zan yi masa wainar fulawa, don ina da yaƙinin wannan dankali da shayin da kika yi abubuwa ne da kullum yake gani kuma yake cinsu. Amma ina da yaƙinin wannan wainar fulawan zai zama sabon abu a wajensa". Kafin na gama kammala zancen kawai na ga ta ɗaga hannu za ta zabga mini mari na yi hanzarin riƙe hannunta tare da jefa idanuna a cikin na ta.
"Kar ki kuskura ki yi gangancin É—aura hannunki a jikna da sunan mari. Don abin da zai bi yo bayan hakan daga ni har ke ba zai mana daÉ—i ba". Kafin ta ce wani abu Hajiya Muhibbat ta shigo cikin kicin É—in ta iske mu a haka.
"Me yake faruwa na gan ku kun tsaya cirko-cirko?".
"Babu komai Hajiya, da inna fere dankalin nan ne na kuskure hannuna shi ne take so ta É—auke min wajen".
Altine ta kora mata bayanin da ta ƙirƙire shi a take a wajen, ban ce da ita komai hasalima ko hannun ta ban yi ba.
"To Allah ya kiyaye gaba. Wannan fulawar fa?".