Sashe 7
Dafin Harshe Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Me yasa mutane ba su da tausayi ne? Me yasa masu kuɗi ba sa tausayi na ƙasa da su? Me yasa masu kuɗi ba sa tausayin masu rauni? Wani irin al'umma ce muke rayuwa a cikin da babu tausayi balle jin ƙai?. Kowa babu Allah a cikin zuciyarsa kowa saɓon Allah da kaucewa koyarwa Annabinmu Muhammadu kawai aka saka a gaba. Ta ina za a sama yadda ake so? Me yasa masifo da bala'i ba za su baibaiye al'umma ba?".
Shuru ya biyo bayan zancena na ƙarshe na tsawon mintuna kafin ta kawar da shi ta hanyar faɗin"wai me ya faru ne?". Na kwashe komai tiryan-tiryan na sanar da ita ta daɗe ba ta yi magana kafin can ta ce"kin ga hakan kaɗai ya isa ya tabbatar miki da cewar sauran matan da kika gani a cikin gidan nan su ma dole ce ya sanya su aikata abin da suke aikatawa na haramci ba wai don son zuciyoyinsu ba".
Na tashi na zaune"babu wani uzuri cikin aikata saɓon Allah. In sha Allah zan ci gaba da nema har na dace da na ƙwarai". Ta yunƙura za ta yi magana na dakatar da ita"ki taya ni da addu'a kawai". Ta ja numfashi ta fesar kafin ta ce"shikenan Allah ya sa ki dace".
"Amin". Na amsa da shi, ta tashi ta fita ta bar ni a cikin É—akin, na kwanta ina tunanin mafita ga bahaguwar rayuwata.
[12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
________________________________________
Page 4ï¸âƒ£5ï¸âƒ£
Tun da na shiga cikin ɗakin ban fito sai alwalan da na fito na yi na koma ciki na zauna, a nan na yi sallan zuhur, na yi asr har magrib. Yunwa ya dinga ƙwaƙulan kayan cikina na dafe cikina ta faman murtsukuku a wajen kamar zan mutu, ina mayar da wani irin numfashi da ƙarfi da ƙarfi da ƙyar na iya tashi na zauna ina salati tare da karanto dukkanin wani addu'ar da ya fara zuwa bakina.
Ganin yunwa yana neman raba ni da numfashina idanuna har wani dishi-dishi yake yi mini ga wani irin nauyin da kaina ya yi mini na bala'in gaske. Da rarrabe na fito ƙofar ɗaki na dinga warara amai tamkar zan amayar da dukkan kayan cikina sosai nake aman har jikina yana rawa kamar ana jona mini wutar lantarki.
"Sannu Amatullah ba ki da lafiya ne?". Na tsinkayo muryar La'aniyatu a bisa cikin kwanyata, na kasa ba ta amsa da kalmomin baki ila gyaɗa mata kaina da na yi alamar e ta taimaka mini na tashi tsaye sai dai ƙafafuna sun kasa ɗaukar nauyina.
Muka koma ciki na kwanta lamau kamar ruwa na kasa tashi balle na É—aga ko da Æ´atsan hannuna.
"Wai me yake damunki ne?". Na yi jarumtar faÉ—in"yunwa nake ji wallahi ji nake yi kamar numfashina zai tsaya cak".
"Bari na kawo miki abinci sai ki ci". Ta ƙare zancen tare da tashi ta fita babu jimawa ta kawo mini biredi da ruwan shayi da babu ko madara a cikinsa, na tashi jikina yana rawa na amsa na ɓula ledar na soma zuƙa ina turawa da biredin sai da na ci ya fi rabin biredin kana na ƙarisa zuƙe ruwan shayin na koma na kwanta ina mayar da numfarfashi.
"Sannu! Ya jikin na kin?".
"Yunwar ce fa kawai".
Cike da tausaya wa ta ce"ba ki ci abinci ba ne tun safe?". Hawaye suka ziraro mini daga gefe da gefen idanuna kana na ce"ban ci ba Aminun yau gabaɗaya bai shigo ba". Ta sauƙe numfashi mai ƙarfi da har sai da na jiyo sautin fitar sa"na ji fa Ummanta suna waya da shi yana cewa ya yi tafiya can wani gari, kuma ina tabbatar miki da cewar da wata matar zai dawo ya kawo ta cikin gidan nan".
"Yanzu haka zan zauna kenan babu ci babu sha har sai ya dawo daga tafiyar da ya yi ke nan?. Dole na tashi na nema yadda zan taimaki kaina, ki riƙe ni na tashi na zauna na yi salla".
Na wangale baki da ido tana duba na"salla kuma? Ba ki da lafiyan ma ba za ki huta ba? Ban taɓa ganin macen da take girmama ibada sama da ke ba. Tun da kika zo gidan nan ban taɓa ganin kin yi fashin salla ba". Cike da matsanancin mamaki nake bin ta da kallo na gaza cewa komai har ta gama zancen ta ƙare.
"Salla kam ai ko da lafiya ko akasin hakan dole ce akan dukkan wani musulmi mai hankali kuma balagagge. Matuƙar kana cikin hankalinka dole ka yi salla ka bautawa Ubangijinka".
Ta sauƙe numfashi kafin ta ce"tirƙashi! Ni dai na tashi ne kawai a matsayin musulma amma duk wasu abubuwan da suke cikin musulunci ban san su ba kuma ba na aikata su. Sallar ce kawai ita kuma bai fi a sati na yi sau biyu ba shi ma sai na ga dama, tun da nake Mahaifiyata ba ta taɓa nuna min cewa salla dole ne a kaina ba balle ta koyar da ni sauran wasu abubuwan addini".
"Ko ba ta koyar da ke ba ke ya dace ki tashi ki nema ilmi ki nema ilmin addininki domin inganta rayuwarki ta gidan duniya da kuma na lahira. Kin ga hatta wannan sunan da ake ƙiranki La'aniyatu ba shi da gurbi a cikin addinin musulunci, domin fassara Annabinmu ya koyar da mu cewa mu sanya wa ƴaƴanmu sunane masu kyau da ma'ana domin suna linzami shi yasa ake so a dinga sanya wa ƴaƴa sunayen salihan bayi, masu imani da zuciyar tausayi waɗanda suka yi wa addinin musluncin hidima da ƙarfinsu, lokacinsu da kuma dukiyansu".
"To me ye fassaran sunan nawan?".
"Kalmar La'aniyatu kalmar labarci ne da yake nufin tsinanniya ko kuma wani abun da aka kwashe masa albarka". Ta dafe ƙirji"tsinanniya kuma?". Na gyaɗa mata kaina"ƙwarai kuwa a duk lokacin da aka ƙira sunanki hakan na nufin ana ƙiran ki da tsinanniya ne". Ta yi shuru na lura gabaɗaya jikinta ya yi sanyi ƙalau tamkar kazar da aka jifa da ruwan gishiri, na dafa kafadunta cikin sigar ƙafafa gwiwa na ce"kar ki wani damu fa, ai har yanzu lokaci bai ƙure ba. Za ki iya sauya sunan zuwa duk sunan da kike so mai ma'ana da asali gami da tushe".
"Ba zan ma fara wannan garajen ba Amatullah, na san ma Ummata ba za ta taɓa barin na yi hakan ba. Tun da ƙaddarata ta faɗo a haka babu yanda zan yi face na rumgume ta yadda ta zo min".
Zan yi magana ta ɗaga mini hannu alamar ba ta son jin komai daga gare ni"Amatullah kar ki kawo min rikici da ruɗu a cikin rayuwata. Na yi kowa sanin wace ce Ummanta don ita ta haife ni hakan ba zai hana ta hukunta ni idan na bujire mata ba, ba abin wahala ba ne a wajen ta ta saka a haukata ni. Don haka maganin bari kar a fara Hausawa suka ce zaman lafiya ya fi zama ɗan sarki". Ina ƙare zancen ta tashi ta fita da sauri ba tare da ta ba ni damar cewa komai ba. Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya ina dafe jikin gini na tashi na fito na yi alwala na koma ciki na gabatar da sallan isha'i. Ina zaune a inda na yi sallan aka ɗago labulen ɗakin akan shigo.
Wata matasjiyar budurwa ce ta tsuke cikin shirgar ƙananan kaya dogon wandon da aka tsatstsaga gwiwansa sai kuma wata rigar da babu hannu a jikinta, ta tula uban gashin doki a kanta da ya sauƙo har bayan wuyanta tana taunar chewgum da yake ba da sautin ɗas ɗas.
"Ke ce Amatullah?".
Na gyaÉ—a kaina"e ni ce".
"To ki zo Hajiya Babba tana son ganawa da ke a cikin É—akinta".
"Na shiga uku! Allah ya sa ba wani laifin na yi ba". Na galla mini harara"wannan kuma idan kin je za ki ji ko ma me nene. Ni dai na isar da saƙo". Tana dire zancen ta juya ta fice ta bar ni cikin tarin zulumi da fargaban abin da zan je na tarar. Cikin mutuwar jiki na tashi na fito na nufi ɗakin Hajiya Babba na tsaya daga waje ina kwaɗa sallama sai da ta ba ni iznin shiga kana na shiga. Tana zaune akan kujera ta ɗaura ƙafarta ɗaya akan ɗaya na zauna a ƙasa tare da gaishe ta ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa.
"Hajiya sannu da hutawa, an ce wai ki na nema na". Na ajiye wayar da take latsa wa ta fuskanto ni da kyau tare da faɗin"kwananki nawa a cikin gidan nan?". Ƙirjina ya buga na shiga tsoron kar ta ce na haɗa nawa ya nawa na bar cikin gidan don na ga hakan ba wani abu ne mai wahala a wajenta ba. Kafin na ba ta amsa ta ci gaba da cewa"na lura har yanzu ba ki fara mu'amala da kowa ba balle har ki sama kuɗin da za ki dinga biyan kuɗin hayan ɗakinki. Sannan har zuwa wannan lokacin Aminu shi yake ɗaukan nauyin ci da shanki, shin dama ba ki shiryawa rayuwar bariki ba kika saka ƙafa kika fito daga gidanku? Ba ki tanadin guzurin irin rayuwar nan ba kika baro gaban iyayenki?".
Jikina gabaɗaya ya yi laushi na kasa cewa da ita komai illa sadda kaina ƙasa da na yi da hakan ya ba wa hawayen da nake dako damar tsiyaya. Muryata can ƙasan maƙoshina na furta"Hajiya in sha Allah zan nema sana'ar da zan din ga ɗaukar ɗawainiyyar kaina da shi kwanan nan".
"Wane irin sana'a kenan?".
"Kowani irin aiki idan zan samu na cikin gida, ko wankau ne ko kuma rauno....". Tun kafin na rufe bakina ta katse mini numfashina"wankau dai da na sani?". Na gyaɗa mata kaina alamar e da hakan ya ba ta damar zarce wa da faɗin"mace kamar ki ta tsaya tana yin wankau ai wannan abin a duba lamarin ne, yadda kike da dirin nan ga kuma kyawun sura da ko mace ƴar uwarki ce ta gan ki sai ta ƙara bin ki da kallo balle kuma ɗa namiji. Me ye zai hana ki yi amfani da damar da Allah ya ba ki wajen cin duniyarki da tsinken sakace".
"Ban gane abin da kike nufi ba?".
Shuru ya biyo bayan zancena na ƙarshe na tsawon mintuna kafin ta kawar da shi ta hanyar faɗin"wai me ya faru ne?". Na kwashe komai tiryan-tiryan na sanar da ita ta daɗe ba ta yi magana kafin can ta ce"kin ga hakan kaɗai ya isa ya tabbatar miki da cewar sauran matan da kika gani a cikin gidan nan su ma dole ce ya sanya su aikata abin da suke aikatawa na haramci ba wai don son zuciyoyinsu ba".
Na tashi na zaune"babu wani uzuri cikin aikata saɓon Allah. In sha Allah zan ci gaba da nema har na dace da na ƙwarai". Ta yunƙura za ta yi magana na dakatar da ita"ki taya ni da addu'a kawai". Ta ja numfashi ta fesar kafin ta ce"shikenan Allah ya sa ki dace".
"Amin". Na amsa da shi, ta tashi ta fita ta bar ni a cikin É—akin, na kwanta ina tunanin mafita ga bahaguwar rayuwata.
[12/3, 2:54 PM] Aeesher: *DAFIN HARSHE*
Â©ï¸ Maimuna Tijjani Iyam
________________________________________
Page 4ï¸âƒ£5ï¸âƒ£
Tun da na shiga cikin ɗakin ban fito sai alwalan da na fito na yi na koma ciki na zauna, a nan na yi sallan zuhur, na yi asr har magrib. Yunwa ya dinga ƙwaƙulan kayan cikina na dafe cikina ta faman murtsukuku a wajen kamar zan mutu, ina mayar da wani irin numfashi da ƙarfi da ƙarfi da ƙyar na iya tashi na zauna ina salati tare da karanto dukkanin wani addu'ar da ya fara zuwa bakina.
Ganin yunwa yana neman raba ni da numfashina idanuna har wani dishi-dishi yake yi mini ga wani irin nauyin da kaina ya yi mini na bala'in gaske. Da rarrabe na fito ƙofar ɗaki na dinga warara amai tamkar zan amayar da dukkan kayan cikina sosai nake aman har jikina yana rawa kamar ana jona mini wutar lantarki.
"Sannu Amatullah ba ki da lafiya ne?". Na tsinkayo muryar La'aniyatu a bisa cikin kwanyata, na kasa ba ta amsa da kalmomin baki ila gyaɗa mata kaina da na yi alamar e ta taimaka mini na tashi tsaye sai dai ƙafafuna sun kasa ɗaukar nauyina.
Muka koma ciki na kwanta lamau kamar ruwa na kasa tashi balle na É—aga ko da Æ´atsan hannuna.
"Wai me yake damunki ne?". Na yi jarumtar faÉ—in"yunwa nake ji wallahi ji nake yi kamar numfashina zai tsaya cak".
"Bari na kawo miki abinci sai ki ci". Ta ƙare zancen tare da tashi ta fita babu jimawa ta kawo mini biredi da ruwan shayi da babu ko madara a cikinsa, na tashi jikina yana rawa na amsa na ɓula ledar na soma zuƙa ina turawa da biredin sai da na ci ya fi rabin biredin kana na ƙarisa zuƙe ruwan shayin na koma na kwanta ina mayar da numfarfashi.
"Sannu! Ya jikin na kin?".
"Yunwar ce fa kawai".
Cike da tausaya wa ta ce"ba ki ci abinci ba ne tun safe?". Hawaye suka ziraro mini daga gefe da gefen idanuna kana na ce"ban ci ba Aminun yau gabaɗaya bai shigo ba". Ta sauƙe numfashi mai ƙarfi da har sai da na jiyo sautin fitar sa"na ji fa Ummanta suna waya da shi yana cewa ya yi tafiya can wani gari, kuma ina tabbatar miki da cewar da wata matar zai dawo ya kawo ta cikin gidan nan".
"Yanzu haka zan zauna kenan babu ci babu sha har sai ya dawo daga tafiyar da ya yi ke nan?. Dole na tashi na nema yadda zan taimaki kaina, ki riƙe ni na tashi na zauna na yi salla".
Na wangale baki da ido tana duba na"salla kuma? Ba ki da lafiyan ma ba za ki huta ba? Ban taɓa ganin macen da take girmama ibada sama da ke ba. Tun da kika zo gidan nan ban taɓa ganin kin yi fashin salla ba". Cike da matsanancin mamaki nake bin ta da kallo na gaza cewa komai har ta gama zancen ta ƙare.
"Salla kam ai ko da lafiya ko akasin hakan dole ce akan dukkan wani musulmi mai hankali kuma balagagge. Matuƙar kana cikin hankalinka dole ka yi salla ka bautawa Ubangijinka".
Ta sauƙe numfashi kafin ta ce"tirƙashi! Ni dai na tashi ne kawai a matsayin musulma amma duk wasu abubuwan da suke cikin musulunci ban san su ba kuma ba na aikata su. Sallar ce kawai ita kuma bai fi a sati na yi sau biyu ba shi ma sai na ga dama, tun da nake Mahaifiyata ba ta taɓa nuna min cewa salla dole ne a kaina ba balle ta koyar da ni sauran wasu abubuwan addini".
"Ko ba ta koyar da ke ba ke ya dace ki tashi ki nema ilmi ki nema ilmin addininki domin inganta rayuwarki ta gidan duniya da kuma na lahira. Kin ga hatta wannan sunan da ake ƙiranki La'aniyatu ba shi da gurbi a cikin addinin musulunci, domin fassara Annabinmu ya koyar da mu cewa mu sanya wa ƴaƴanmu sunane masu kyau da ma'ana domin suna linzami shi yasa ake so a dinga sanya wa ƴaƴa sunayen salihan bayi, masu imani da zuciyar tausayi waɗanda suka yi wa addinin musluncin hidima da ƙarfinsu, lokacinsu da kuma dukiyansu".
"To me ye fassaran sunan nawan?".
"Kalmar La'aniyatu kalmar labarci ne da yake nufin tsinanniya ko kuma wani abun da aka kwashe masa albarka". Ta dafe ƙirji"tsinanniya kuma?". Na gyaɗa mata kaina"ƙwarai kuwa a duk lokacin da aka ƙira sunanki hakan na nufin ana ƙiran ki da tsinanniya ne". Ta yi shuru na lura gabaɗaya jikinta ya yi sanyi ƙalau tamkar kazar da aka jifa da ruwan gishiri, na dafa kafadunta cikin sigar ƙafafa gwiwa na ce"kar ki wani damu fa, ai har yanzu lokaci bai ƙure ba. Za ki iya sauya sunan zuwa duk sunan da kike so mai ma'ana da asali gami da tushe".
"Ba zan ma fara wannan garajen ba Amatullah, na san ma Ummata ba za ta taɓa barin na yi hakan ba. Tun da ƙaddarata ta faɗo a haka babu yanda zan yi face na rumgume ta yadda ta zo min".
Zan yi magana ta ɗaga mini hannu alamar ba ta son jin komai daga gare ni"Amatullah kar ki kawo min rikici da ruɗu a cikin rayuwata. Na yi kowa sanin wace ce Ummanta don ita ta haife ni hakan ba zai hana ta hukunta ni idan na bujire mata ba, ba abin wahala ba ne a wajen ta ta saka a haukata ni. Don haka maganin bari kar a fara Hausawa suka ce zaman lafiya ya fi zama ɗan sarki". Ina ƙare zancen ta tashi ta fita da sauri ba tare da ta ba ni damar cewa komai ba. Na sauƙe ɓoyayyar ajiyar zuciya ina dafe jikin gini na tashi na fito na yi alwala na koma ciki na gabatar da sallan isha'i. Ina zaune a inda na yi sallan aka ɗago labulen ɗakin akan shigo.
Wata matasjiyar budurwa ce ta tsuke cikin shirgar ƙananan kaya dogon wandon da aka tsatstsaga gwiwansa sai kuma wata rigar da babu hannu a jikinta, ta tula uban gashin doki a kanta da ya sauƙo har bayan wuyanta tana taunar chewgum da yake ba da sautin ɗas ɗas.
"Ke ce Amatullah?".
Na gyaÉ—a kaina"e ni ce".
"To ki zo Hajiya Babba tana son ganawa da ke a cikin É—akinta".
"Na shiga uku! Allah ya sa ba wani laifin na yi ba". Na galla mini harara"wannan kuma idan kin je za ki ji ko ma me nene. Ni dai na isar da saƙo". Tana dire zancen ta juya ta fice ta bar ni cikin tarin zulumi da fargaban abin da zan je na tarar. Cikin mutuwar jiki na tashi na fito na nufi ɗakin Hajiya Babba na tsaya daga waje ina kwaɗa sallama sai da ta ba ni iznin shiga kana na shiga. Tana zaune akan kujera ta ɗaura ƙafarta ɗaya akan ɗaya na zauna a ƙasa tare da gaishe ta ta amsa fuskarta babu yabo babu fallasa.
"Hajiya sannu da hutawa, an ce wai ki na nema na". Na ajiye wayar da take latsa wa ta fuskanto ni da kyau tare da faɗin"kwananki nawa a cikin gidan nan?". Ƙirjina ya buga na shiga tsoron kar ta ce na haɗa nawa ya nawa na bar cikin gidan don na ga hakan ba wani abu ne mai wahala a wajenta ba. Kafin na ba ta amsa ta ci gaba da cewa"na lura har yanzu ba ki fara mu'amala da kowa ba balle har ki sama kuɗin da za ki dinga biyan kuɗin hayan ɗakinki. Sannan har zuwa wannan lokacin Aminu shi yake ɗaukan nauyin ci da shanki, shin dama ba ki shiryawa rayuwar bariki ba kika saka ƙafa kika fito daga gidanku? Ba ki tanadin guzurin irin rayuwar nan ba kika baro gaban iyayenki?".
Jikina gabaɗaya ya yi laushi na kasa cewa da ita komai illa sadda kaina ƙasa da na yi da hakan ya ba wa hawayen da nake dako damar tsiyaya. Muryata can ƙasan maƙoshina na furta"Hajiya in sha Allah zan nema sana'ar da zan din ga ɗaukar ɗawainiyyar kaina da shi kwanan nan".
"Wane irin sana'a kenan?".
"Kowani irin aiki idan zan samu na cikin gida, ko wankau ne ko kuma rauno....". Tun kafin na rufe bakina ta katse mini numfashina"wankau dai da na sani?". Na gyaɗa mata kaina alamar e da hakan ya ba ta damar zarce wa da faɗin"mace kamar ki ta tsaya tana yin wankau ai wannan abin a duba lamarin ne, yadda kike da dirin nan ga kuma kyawun sura da ko mace ƴar uwarki ce ta gan ki sai ta ƙara bin ki da kallo balle kuma ɗa namiji. Me ye zai hana ki yi amfani da damar da Allah ya ba ki wajen cin duniyarki da tsinken sakace".
"Ban gane abin da kike nufi ba?".