← Book details Rufaffen Sirri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 80

Sashe 29

Rufaffen Sirri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*WANAN NOVEL DIN NA KUDI NE NA HADA KU DA FIYAYYEN HALLITA ANNABI MUHAMMAD SALLAHU ALAIHI WA SALAM KARKU MIN SHARING NOVEL IDAN BANA KALLON KI ALLAH YANA KALLON KI KUDIN KARATU KIKA BIYA BANA MALLAKA BA IDAN KIKA FITAR NA BAR KI DA ALLAH GA MAI BUKATA SAI TA BIYA 500 ZUWA WANAN ACCT DIN 2029764071 FIRST BANK NAFISA NUHU KO KATIN MTN TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08068484400 SAI A TURO DA SHAIDAR BIYA TA WANAN LAYIN 08033719070 KO WANAN LAYIN 08033719070 MUTANEN NIGER KUMA SU NEMI WANAN LAMBAR +227 96 82 89 84*

*PAGE 19*

"Ina zata je ita da bata gani dama nasan saboda ita Sajeeda ke ta wanan kukan"

"Sai a yanzu na gane Ashe a zuci nayi maganar ba'a fili ba"

Har ga Allah so nake kawai na tonawa Abban Nusrah asiri amma sai bakina ya gaza bani hadin kai,sai maganar zuci nake.

Yaya Abu kuwa masifa kawai take Abban Nusrah shi ma ya ringa bambamin fada Yana "Ina zata je ita da bata gani,wanan wane irin masifa ne wlh na fara gajiya da halin yarinya nan Yaya Abu"

"Dan ruko nada wahalar sha'ani idan ba iskanci ba Ina zata je ita da ba gani take ba,iyayin Sajeeda ma ya ja mata da ta dage zata rik'e ta gashi nan ma dangin mahaifinta sun manta da ita

Cewar Yaya Abu,

nidai kuka kawai nake kamar yadda Nusrah ke magana cikin kuka tana "ya akayi wai Yesmeen ta daina gani,wai me ke faruwa ne,?Annur ko wata biyu bai yi da kurmancewa ba yanzu Kuma Yesmeen ce ta daina gani innalillahi wa Inna ilaihi rajiun"

"Nima na fara tsoro ta Aunty Sajeeda yanzu ba wanan ba fita zamu yi muje mu nemo Yesmeen bamu ga ta zama ba"

Daga Haka su Saifullahi suka yi waje.

Abban Nusrah kuwa ya juya ya nufi d'akin sa Yana masifa

Yaya Abu kuwa cewa take "Sajeeda kinsan Allah ki tattara yarinya nan ki maidata wajen dangin ubanta tun kafin ta jawo Miki wani masifar,Yar iska yarinya tun jiya take daga Mana hankali idan ba iskanci ba Ina zata je ita da ba gani take ba,yanzu idan mota ya bugeta fa"

Ni dai shiru nayi ban magana ba dan ban ji hankali na ya tashi ba tunda nasan Yesmeen na gani, tsorana daya bansan hannun wa zata fada ba yesmeen bata jin magana ita bata san ma gudun da tayi ne zai saka Abban Nusrah ya zargi ko fada min tayi ba,Ina tsoron ma ya cutar da ita,dan daga labarin da ta bani,Yana sanin duk halin da take ciki tunda kila ta hanyar tsafi yake gane wa,Ina tsoron ya gano ma karyar makanta tayi, Yesmeen bata yi tunani ba,sai a yanzu duk nagane akwai dalilin daya saka naji bana iya dogon Addu'a daga lokacin da na fara munanan mafarki da naso taimaka wa kaina da Addu'a shine ya yi abinda Ina fara wa zan ji bacci ya d'aukeni.

Kabiru

Yana shigewa daki yaji zufa na keto masa ba dai Yesmeen ta tona sirrinsa ga Sajeeda ba tunda Yaya Abu tace tunda ya fita suka shige d'aki Suka ringa juyo kukan Sajeedan,ba dai Yesmeen karyar makanta ta Masa ta mishi shigo shigo ba zurfi ba,amma idan har ta tona masa asiri baya Jin Sajeeda zata iya hakuri bata tunkare shi da maganar ba dan yasan halin Sajeeda,ji yayi gabadaya kansa ya kulle zuciyarsa cike da fargaba jiki na rawa ya d'auki wayar sa ya hau neman lambar shugaban su sai da ya masa Kira biyar ana shidda ya d'auki wayar.

Kabiru yayi kasa da murya Yana "Shugaba ka taimaka ka duba min yarinya nan idan har dagaske ta makance ka Kuma duba mun ko ta fadawa matata sirrina dan Ina zargin Kamar ta fadawa matata shi yasa ta gudu,dan idan har bata gani ba abinda zai saka ta gudu a taimaka min Dan Allah a Kuma Kara min aiki akan matata Ina gudun tonan asirina"

"Ina wani aiki yanzu Zan duba ma karfe daya na dare"

Da haka suka yi sallama ya ajiye wayar Yana goge zufar dake ta keto masa har rigar jikin sa ta jike da gumi taya zai yarda asirin sa ya tonu a yanzu da ko fara morar kudin sa baiyi ba.

Muryar Abu da ya jiyo cikin bambamin masifa tana "Dan ubanki Ina Kika je ke da bakya gani"?

Da sauri yayi waje a daidai lokacin da Yaya Abu ta kwashe Yesmeen da idonta ke kallon sama mari , Saifullahi kuwa na rike da ita,

Sajeeda kuwa ta mik'e tana "Dan Allah Yaya Abu ki rabu da ita ba gani take ba"

"Tasan da bata gani ta fita dan uban ta kiga yadda ta daga mana hankali gidan uban wa zata je da ta fitan da yanzu mota ta kade ta fa"?

"Saifullahi a Ina kuka ganta"?

Abban Nusrah yace fuskarsa a mugun hade

Saifullahi ya fara magana Yana " a wajen shagon dake kasan layin nan muka hangota tana bin bango wai auduga taje siya"

"Haba Yesmeen akan me zaki fita bayan kinsan larurar ki kinsan yadda kika daga Mana hankali kuwa ?yanzu da mota ta bige ki fa"?

Cewar Sajeeeda tana zubda kwalla kasan zuciyarta Kuma tana Jin dadin da ba guduwa Yesmeen tayi ba

Kabiru kuwa cikin wani irin bacin rai ya fara magana Yana " Yaya abu na gaji da zaman yarinya nan a gidanan idan ban da tashin hankali ba abinda take jefani,dan haka Zan tattara ta na maida ta wajen ubanta bazai Yu Ina zaman zamana tazo ta jawo min magana ba"

"Kayi daidai da kaina Zan maidata wajen ubanta Dan daga jiya zuwa yau nasan jinin Sajeeda ya hau ya Kai sau Dubu haka kurum ana zaune kalau"

"Wallahi ba inda zata je idan har Yesmeen barin gidanan za tayi wallahi sai da mu bar gidan a tare

"Aikuwa maida ta za'ayi tun jiya take saka ki kuka,banda iskanci wa ta gayawa tana bukatar auduga Yesmeen yarinya ce ita"

Wani irin bakin ciki da takaicin Yaya Abu ne ya rufe Sajeeda duk da tana iya k'ok'arin ta wajen danne zuciyarta taga bata mata wani abu taji a ranta kamar Raina ta tayi saboda tazo wajenta ganin yadda ta hakikance tana sai an maida Yesmeen yasa ta fara magana cikin bacin rai tana "Yaya abu ba inda Yesmeen za taje,Yesmeen Yata ce kema yarki ce banga dalilin zaa ce zaa koreta ba,mai tayi?laifine dan an tausayawa halin da take ciki,tashi daya Muka wayi gari ta daina gani, iya wanan bai Isa yasa a tausaya mata ba sai ace zaa koreta,yau kina tunanin da Nuratu na rayye zata ji dadin irin yadda kike yiwa yarta ?karki manta fa baa san ranta ta mutu ta barta ba yau da bana rayye ke mai rik'e Yesmeen ce ban taba zaton haka daga wajenki ba"

"Ikon Allah Wani Abu akace zaa yiwa Yesmeen din kike zuba wanan dogon bayani,kina magana kamar ni na kashe Nuratu,kina tunanin idan Nusrah ce zata ringa daga miki hankali haka,yarinya tun jiya ta Hana mu sukuni,kike ta zuba dogon bayani kinsan da mota ta kadeta da ta fita dinan dangin babanta ba yarda zasu yi ba karshenta sai sun kulle ki"

"Ai na ma gama magana Yaya Abu Ni ke auren Sajeeda ba ita ke Aurena ba bata isa ta juya ni ba a karkashin ikona take da yardata ta rik'e Yesmeen a yanzu Kuma nace ta maida Yesmeen wajen mahaifin ta tunda Yana rayye ba mutuwa yayi ba a goben Nan Zan maidata"

Tunda ya fara magana wani irin Abu naji ya tsaya min a zuciya,wutar kiyayarsa ruruwa kawai yake a raina ji nake kamar na samo wuka nayi ta yanyanka shi yanzu alwashin da nake Sha ma bazai ci kudin nan ba yadda yake san yaga ya kasheni sai dai mu tafi tare bana Masa fatan Rahamar Allah daga Rana irin ta yau har zuwa karshen numfashina addu'oi masifa da balai Zan ta Masa,tunda har dani zai yi kudi,ba abinda zai hana naso ganin bayan sa.

Ganin Yana k'ok'arin barin palon Yana ta sheka rantsuwa yasa na fara magana cikin bacin rai Ina Jin ruwanan na zubo min Mai doyi

"Wallahi ba inda zata je Abban Nusrah idan har ka dage ka gaji da rukonta sai ka sallameni nima na tafi,haka kawai ba abinda ta maka zaka koreta,baka tashi korarta ba sai da ta daina gani,mai zaka cewa mahaifinta ya makantar Mata da ido,a haka na d'auko ta,har yanzu baka ji a jikinka mutane zasu fara zargin akwai wani abu dake faruwa a gidan ka ba kasa da wata biyar ka Zama hamshakin mai kudi,Dan cikin ka ya kurmance yanzu itama Yesmeen ta makance kila nan gaba ma mutuwa za'ayi,duk wani abu na faruwa da dalili banda na gidanan,Koda kaddara Allah ya Aiko akan ce ga dalili kafin aukuwar kaddarar amma na gidanmu daban ne Annur daga kwanciya bacci ya tashi ya daina magana Yesmeen daga kunna fitila ta daina gani,sai nayi magana ace ba haka ba idan har ka shirya korar Yesmeen ka dawo mata da ganin ta sai ta bar gidanan"

"Yaya Abu Kinga yadda ta juya zancen nan ko,banda Sajeeda bata da ilimi bata san yadda Allah ke juye lamarin sa dare daya ba,a cikin awa daya idan Allah ya so azurta bawan sa a yanzu Allah zaiyi silar da zai yi arziki,yanzu Mai ya hada kurmancewar Annur da makancewar Yesmeen da arzikin da Allah yamin yanzu ace matata ke min wanan zargin idan wani taji yana so ya zargeni ita ba mai hanawa bane,wanan wane irin abu ne,yanzu ba abin zargi a wajen ki sai ni kenan Shekara ashirin da uku muna tare ace baki san halina ba?baki San abinda zan yi da Wanda bazan iya ba mai kike nufi duk da kalmomin nan da kikayi da mutane zasu fara zargina"?

Kallona kawai yake Yana hucci cikin bacin rai
Chapter 29 · 0% Book details