← Book details Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 92 OF 93

Sashe 92

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Na manta yanda yarda da kai take, zai dauki lokaci kafin ta dawo, ka tashi"

Bai musu ba ya samu ya mike, yanajin jikin shi a wani irin mace, alwalar yaje ya dauro shima yana fitowa

"Daada..."

Nur ta kira cike da alamun tambaya

"Masallaci zanje Nur, yanzun zan dawo kinji?"

Sai da ta daga mishi kai sannan ya kalli Bilal da idanuwan shi suke kan Nur din, kallonta yake yana rasa abinda yake ji akan ta, saboda kaunarta ko akwaita baisan inda ta labe ba, ciwon da samunta ya haifar mishi kawai yake ji, ciwon da bata da laifin shi, tabon da sukayi wa rayuwar ta yake gani a tare da yarinyar

"Ki yafe mun, ki yafe mun kafin mu tsaya dake a gaban Allah, wallahi bani da hujja"

Ya furta can kasan zuciyar shi, kafafuwan shi na daukar shi dakyar lokacin da suka fita masallaci, ga wani tsoro da yake ji har ran shi. Gidan bai sake rudewa ba sai bayan da suka dawo sallah, saboda lokacin duk yan gidan sun zo, da yake asabar ne, yawanci har masu auren idan basu zo da matan su ba suna zuwa su kadai, haka matan gidan ma, su Zubaida suna zuwa, kusan duk asabar din duniya da wahala kaga basu hadu a gidan ba, dan Rukayya sun dade akanta kafin ta dawo hayyacin ta, tana ganin Bilal din ta mike, sulalewa tayi gabaki daya, ga ciki da yake jikinta.

Gabaki daya Bilal a rude yake jin shi

"Kuyi hakuri, dan Allah kuyi hakuri"

Shine abinda yake furtawa yana sake maimaitawa yana wani irin kuka da daga baya su suka koma suna lallashin shi. Layla itama sai da Rayyan ya riketa, duk kuwa kunyar da daga ita har shi basu san suna da ita ba sai bayan auren su, dan kujera ma in suka zauna a cikin gidan ko babu kowa sai sun dan bada tazara a tsakanin su. Ranar kuwa da ya rike hannunta ta yana daura mata agogo sun zo gidan zasu tafi saboda tana rike da Nur, sai ta rike agogon a hannu, sai ga Abbu ya fito sakin agogon yayi har ya fashe, saboda kunyar da yaji, ita kanta Layla kasa hada idanuwa tayi da Abbun. Murmushi yayi kawai ya rabasu ya wuce.

Amman yau gaban kowa ya riketa har kitchen ya jata ya dibi ruwa ya bata

"Ki rufa mun asiri Layla, babyna a jikin ki, dan Allah ki natsu"

Yake fadi, amman bata san yanda zata fara natsuwa ba, sai da ya kamata yana riketa a jikin shi, tafi mintina goma kafin numfashin ta ya dai-daita, sannan ta iya raba jikinta dana Rayyan, suka samu suka baro kitchen din zuwa falo, kan kujera suka samu suka zauna. Banda ajiyar zuciya babu abinda take saukewa, ganin Bilal din ya nutsar da wani shimfidadden kalubale da take hangowa a gaba, ko ba komai tambayoyin da Nur zatayi mata wata rana ba ita kadai zata yiwa ba, yanzun addu'a takeyi Allah ya bama Bilal aron tsayin kwanaki tare da su, saboda ganin shi ya tuna mata akwai tambayoyin da koya Rayyan zai rike hannunta ba zai isa ba.

Sam Bilal da Rayyan basu samu wani lokaci su kadai ba sai da dare, sai bayan isha'i, sannan, kallon shi Bilal yake yi, amman maganganun Abbu suke dawo mishi

"Da yana nisa da iyayen shi haka Bilal?"

A idanuwan su yake ganin yanda bai kyauta ba, yayi tunanin su kafin ya tafi, amman tunanin kan shi yafi yawa, ba zai iya fuskantar su ba shisa ya zabi ya gudu. Amman gudun nashi bai canza komai ba, bai rage musu ciwo ba kamar yanda yayi tunani, asalima ya kara musu wani ciwon ne na daban

"Hamma kace wani abu"

Bilal ya bukata, saboda shirun yayi mishi yawa

"Me zance? Bani da wasu kalamai"

Numfasawa Bilal yayi

"Kace ka yafe mun"

Dan juyawa Rayyan yayi yana kallon shi, ba yafe mishi bane baiyi ba, ko da bai yafe mishi ba, dawowar da yayi ta wanke komai, amman ba zai fada mishi yaji ba dan yanzun, ya jira kamar yanda ya saka shi jiran shi duk tsayin shekarun nan.

"Da kana son ji da baka dade har haka ba"

Kai Bilal ya jinjina, yana son ji, zai jira duk lokacin da hakan zai dauka, zai jira, zai kuma nunama Rayyan din da gaske yakeyi ya dawo. Babu inda zaije, yana kallo Rayyan ya mike, Nur da tayi bacci akan kujera ya dauka yana sabata a kafadar shi kafin ya kalli Bilal

"Karka bar gidan nan, da gaske nakeyi Bilal, ko ina zakaje ka jira sai gobe idan Allah ya kaimu, ka jirani sai gobe mu tafi tare"

Kai Bilal din ya jinjina mishi kawai, yana hada idanuwa da shi, dan baisan kome Rayyan din yake nema a cikin idanuwan shi ba

"Ka rantse mun babu inda zakaje"

Saboda a tsorace yake, ji yake kamar kar su koma su kwana a gidan yasa ido akan Bilal din karya sake tafiya

"Ba inda zanje Hamma, babu inda zanje. Ka yarda dani, babu inda zani"

Numfashi Rayyan ya sauke yana wucewa ba dan zuciyar shi ta so ba. Bangaren Mami yaje yana yiwa Layla magana ta fito su tafi gida. Da yake Bilya ya dawo mishi da motar shi, ko kudin shima bai tura mishi ba saboda bashi da wadatacciyar natsuwa, sai dai inya isa gida tukunna sai ya samu yayi mishi transfer, kafin su karasa kira biyu yayi wa Bilal duk idan ya daga amsa daya yake bashi

"Ba inda zanje Hamma, ina nan"

Har sai da Layla ta dafa shi sannan ya sauke numfashi

"Ka yarda da shi ko yayane, babu inda zaije. Wannan karin ko da zaka rasa shi, rashin zaizo maka da tabbaci, ba zaka kwanta da rashin natsuwa ba saboda in shaa Allah"

Kai kawai ya iya dagawa Layla, saboda a zantukan akwai tunatarwa, dawowar Bilal baya nufin mutuwa idan ta tashi zata tsallake shi, a yanzun din ma zai iya sake rasa shi, amman duk firgicin da kalaman ta suka sake jefa shi sun zo mishi da wata natsuwa da ba zata misaltu ba, addu'a yakeyi ko da zai sake rasa Bilal din ya samu damar da ko bashi zai suturta gawar shi ba ya halarci jana'iza, ya ga ya binne shi, yayi mishi bankwana, sai ya dawo yayi jira hakurin da yake saukarwa kowanne bawa a yayin rashi, ya kuma shiryawa tashi mutuwar, tunda babu wanda zai tsallake, babu wanda zata bari, kowa cikar lokaci yake jira.

***

Hutun da baisan yana bukata ba shi yayi, satika biyun da basu dai-dai ta mishi komai ba, amman sun nutsar da rayuwar shi, sun dawo mishi da abinda ya rasa, sun dawo mishi da yan uwan shi. Duk da har yanzun Ayya bata daina kallon shi kamar zai sake tafiya ba. Ko sun gaisa da asuba idan takwas tayi bai sake fitowa ba sai ta kira wayar shi taji ko lafiya. Da yake satin farko yaci gaba da zuwa aiki dan karamcin da mai makarantar ya nuna mishi, sai ya tsaya har sati daya ya bashi damar neman replacement kafin ya dawo, sai lokacin sukaje da Rayyan ya tattara duka yan kayan shi da suke gidan da yake haya. Daman saura wata daya kudin shekarar ya kare, mukulli kawai ya kaiwa mai gidan.

Yau kam tsaye yake kofar gidan su Aisha yana neman kwarin gwiwar shiga cikin gidan. Dakyar ya iya kwankwasa maigadi ya bude mishi, kallon Bilal yakeyi yana mamakin inda ya shiga a duk tsayin shekarun, gaishe da shi Bilal yayi yana wucewa harabar gidan, zufa har cikin tafukan hannayen shi yake jinta. Ba tunaninta bane baiyi, sosai take fado mishi. Ko bayan ya dawo dinma tana ran shi, yana tunanin inda rayuwa ta kaita, kasa hakuri yayi yace ma Rayyan

"Aisha tayi aure na sani... Tayi aure yanzun"

Tafiyar shi ta saka ya rasa abubuwa da dama, bayajin wata zata so shi yanda Aisha taso shi. Ya rasa shekaru uku a tare da su, baiga auren da yawa daga cikin yan uwan shi ba, baya cikin hotunan su da rayuwar da sukayi a shekarun, ya kuma rasa Aisha, kai Rayyan ya girgiza mishi

"Bana so in maka magana baka shirya ba. In ba a watan nan tayi aure ba tana nan, naganta a gidan mai last month"

Dan ba zai manta bayan sun gaisa ba, shi duk daburcewa yayi da yaji ta tace, yana zaune cikin mota, ya juyo ya ganta

"Hamma"

Saukowa yayi, da suka gaisa saiya rasa abinda zaice mata, kamanninta suna nan, amman ba yarinyar da yasani bace, ba budurwar Bilal din shi da take yi musu girki bace a makaranta, wannan ta girma, ta zama cikakkiyar budurwa, idan sa'anni daya suke da Layla ba zata shige shekaru ashirin da biyar zuwa da shida ba yanzun. Ba kamar sanda ya santa tana sha wani abu ba. Haka kawai ya tsinci kan shi da son tambayar ko tayi aure, sai ya kasa, bakin shi yayi mishi nauyi, dan yana jiran Bilal ba shida tabbas din zai dawo, baiga dalilin da zaisa yayi mata tambayar ba, amman ga mamakin shi dariya tayi a nutse

"Banyi aure ba Hamma, ban dade da gama bautar kasa ba..."

Kai ya jinjina mata, labarin yayi mishi dadin ji, sallama sukayi da sakon ta na ya gaishe da Layla

"Ka dauki kafafuwan ka kaje kafin ka rasata gabaki daya"

Shine abinda Rayyan ya fada mishi

"Kana tunanin zata so ni har yanzun? Ni din bani da komai da zan bata, ga Nur kuma..."

Kallon shi Rayyan yayi

"Kana da zuciyar ka, ni bansan me zance maka ba, ban iya kalamai kamar Abbu ba, idan kana tunanin makaranta ne na fada maka ina sake tsayar maka duk shekara, zaka iya cigaba sanda ka shirya. Zaka iya fara zuwa kasuwa kasani in ka fadama Abbu, zaka samu sana'ar da zaka iya rike mata..."

Sauraren Rayyan yakeyi

"Nur ba zata hana komai ba in dai tana son ka har yanzun, zata fahimce ka, kuskuren ka a wajen Allah ma mai yafuwa ne balle kuma mutum, rashin ta ne idan bata fahimta ba, sai ka hakura, sai ku hakura da juna. Amman kaje, ko ba komai ta cancanci kayi mata bayani"
Chapter 92 · 0% Book details