Sashe 84
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kanta Mami ta sadda kasa tana kai yatsanta a hankali ta share kwallan daya taru a cikin idanuwanta, zuciyarta na wata irin kuna, mikewa matar tayi babu ko sallama ta raba Layla ta wuce. Har lokacin jikin Jabir bari yakeyi. Sakin hannun Layla yayi yana wucewa dakinta da kan shi ya dauko hijabi ya mika mata
"Hamma..."
Ta fadi muryarta na rawa, idanuwanta cike da hawaye, kai Jabir ya girgiza. Zuciyar shi sam ba zata iya dauka ba. Baice abinda Layla tayi bashi da muni ba, amman tsakaninta ne da Ubangiji, a cikin duk tarin mutanen da suke mata surutu, suke nunata da yatsa babu wanda za'a binne su a tare, sanda za'a kaita a rufo a barta da ayyukanta ba lallai su sani ba, addu'ar neman Rahma ma ba lallai bane su bita da ita. Baisan inda tarin mutanen suka shiga ba a lokacin da ta samu makaranta, lokacin da tayi saukar Al'Qur'ani mai girma, duka bai gansu sun shigo tayata murna ko jinjina ma su Mami kan kokarin su ba.
Sai yanzun da kowa yake tunanin sunyi kuskure a rikon Layla, sai yanzun da ita kanta Layla din wani abu mai muni ya sameta, tarin mutanen da basu da masaniya akan kominta sune a gaba wajen yanke mata hukuncin da basuda hurumin yin haka. Yana gab da fara sakawa mutane hannu idan yana gidan suka shigo, baisan me yasa Mami bata binsu da tabarya ba, shi bashida wannan hakurin sam
"Ba zaki kare duka rayuwarki a cikin bango hudu na dakin ki ba Layla, idan baki fita da cikin nan ba zaki fita da yaro ko yarinya. Mutane suna magana yanzun, ba zasu daina magana ba, karki barsu, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure"
Jabir ya karasa maganar da wani irin yanayi a muryar shi da yasa hawayen da ke cikin idanuwan ta zuba
"Jabir ka kyaleta, me yasa baka da hankaline kai?"
Mami tayi maganar tana kokarin tarbe kukan da yake barazanar kwace mata, hijabin Layla ta karba tana sakawa a jikinta. Zuciyarta na wata irin dokawa kamar zata baro kirjinta. Mami bata hana su ba, tana kallo Jabir ya koma ya daukowa Layla takalmanta, fitar sukayi, daga farkon layin har titi, Layla tana jinta kamar babu kaya a jikinta saboda kallon da mutane suke binta da shi, kamar yanda Jabir ya fadane, ba zata cigaba da boyewa ba har abada, zancen ya rigada ya bazu, gara ta fara koyan yanda zatayi rayuwa da tabon da yake jikinta.
Sanda suka koma numfashi ma dakyar take fitar da shi, har bakin kofar dakinta Jabir ya rakata sannan ya tsaya yana fadin
"Babu hakkin mutane a kanki. Ba zan miki karya ba kin sani, duka rayuwar ki ta duniya ce ta samu tangarda, ba zancen zancen ki ba zai wuce a baku nan mutane ba, amman duk sanda zaki gifta zaki tuna musu abinda yake adane a zukatan sune, bansan al'adun mu na hausawa basawa mata adalci ba sai yanzun Layla, sai da rashin adalcin ya biyo ta cikin gidan mu...."
Wani irin numfashi Jabir yaja, bayason hawayen shi su zuba a gabanta, zai kara karya mata zuciya
"Ba zaki iya gyara tsakanin ki da mutane ba, ki gyara abinda kike da tabbas akan shi, ki gyara tsakanin ki da Allah, sai Ya tausaya miki ya gyara duniyar ki, karki bar su, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure, kina jina"
Kai ta daga mishi tana goge hawayenta. Sai da yaga ta shiga daki sannan ya juya yana komawa wajen Mami ma da tun da suka fita tana zaune tana wani irin kuka mai cin rai
"Dan Allah ki rage sanyin halin nan Mami, ki daina barin mutane suna bi takan ki akan abinda baya karkashin ikon ki, idan ba zaki iya korar su ba Mami ki daina sauraren me zasu ce suna bata miki rai, dan Allah. Wallahi zuciyata zafi takeyi mun, sosai da sosai"
Cewar Jabir yana ficewa daga dakin saboda bayason ganin kukan da Mami takeyi. Har Abbu ya samu da daren ranar, dan Abbu ba zai manta yanda Jabir ya shiga dakin babu ko sallama ba
"Yaushe abin nan zai wuce mana Abbu? Me yasa mutane ba zasu kyale mu ba? Ina ruwan su da rayuwar mu?"
Hannu Abbu ya dan bubbuga a gefen shi yanawa Jabir din alamu daya je ya zauna, bai musa ba kuwa ya karasa yana zama inda Abbu ya nuna mishi, idanuwan shi sun kada sunyi ja, watakila da yayi kuka zai samu sauki
"Nagaji da ganin Mami na kuka kullum, ina jina so helpless..."
Dan murmushi Abbu yayi
"Ka kalleni Jabir, ban san inda nake samun karfin bude idanuwa ba a duk safiya, saboda wannan ne karo na farko da ko kalaman lallashi bani da su, damuwar ku gabaki daya ta tarar mun, ni ya kake tunanin ina ji? Um Jabir? Dan Allah ka dan kara daurewa, komai zaiyi sauki In shaa Allah"
Jabir ya dade zaune a dakin ya hade kan shi da gwiwa yana neman sauki koyaya ne. Kamar yanda shima Abbu yake tsaye a wajen yana neman sauki a yanzun, daga shi, Ayya sai kuma Mami a asibitin, da yake dare ya farayi sanda suka fito din, wajen sha daya. Addu'ar duk da tazo bakin Abbu ita yakeyi, kafin wayar shi da take aljihun shi ta fara ringing, yana fito da ita yaga Rayyan ne, yana dagawa ya saka a kunnen shi muryar Rayyan din ta daki kunnen shi
"Ina ta kiran Ayya bata daga ba, Mami ma haka, Layla fa? Nakudar ce ta sake dawowa ko Abbu? Ina magana da ita naji shiru, sai kira nakeyi itama bata dagawa"
Dan siririn numfashi Abbu ya sauke
"Gamu nan a asibiti m..."
Rayyan bai bari Abbu ya karasa ba yace
"Me suka ce? Ga shi dare yayi ni ba zan iya tahowa ba yanzun"
Duk da halin da Abbu yake ciki sai da yayi dan murmushi
"Ka kwantar da hankalin ka. Babu abinda zai faru sai alkhairi da yardar Allah, zan dinga kiran ka ina fada maka yanda ake ciki, kayi mata addu'a kai dai kaji"
Sai da ya amsa sannan sukayi sallama, su Mami ya kalla
"Rayyan ne"
Kai Mami ta jinjina, ko lokacin da ake maganar soyayya a dangin su, zancen baya wuce
"Anya akwai matar da tayi sa'a irin Maimunan Ahmadi?"
Ko da ta aure shi ta sabajin yanda ake fadin
"Maimunan Ahmadi"
Shisa sam bata jin kishin haka, zata so a yanzun na minti daya idanuwa da hankulan kowa su dauke daga cikin Layla su koma kan ita da Rayyan, tana da tabbacin tsantsar kaunar da take tsakanin su zai saka su fara sabon mamaki, ba kowanne namiji bane zaiyi abinda Rayyan din yayi. Ko ita maganar ta daketa da tajita daga farko, sai ta dinga ganin kamar mafarkine, duk da tasan da yawa zasu ce tayi azarbabi, kamar ta jira taga yanda zaman Rayyan da Layla zai kasance a karkashin inuwar aure kafin ta yanke hukunci akan tarin kaunar da suke yiwa juna. Sai dai ta kasa, tana da yakini mai girma akan kaunar Layla da take gani tattare da Rayyan din.
Watakila kuma idanuwanta ne suka rufe saboda nauyin da Rayyan din ya dauke mata na tunanin wanda zai zamo miji a wajen Layla, wanda zai kauda kai daga tabon da yake tare da ita harya ganta din, da tarin kalubalen da zata iya fuskanta daga wajen dangin shi idan har ta samu din ma. Duka rayuwar 'ya mace zagaye take da martabar da tabuwarta yake dai-dai da nakasun da zai taba gabaki daya ahalinta. Kuskure daya tak zai iya canza komai ta fannin da gyaruwar shi zatayi wahala. Dukan su a tsaye suke duk kuwa da kujerun da suke a wajen, babu mai natsuwar zama, kowa da abinda yake sakawa yana kwancewa a cikin zuciyar shi.
*
Motar farko ya samu daga Kaduna zuwa Kano, asuba ma a tasha yayita. Da yake Bappa ya kai shi, amman gani yakeyi kamar motar bata sauri, yau ne ya sake jin takaicin rashin iya tuqi, da yana da mota a hannun shi iya gudun da yake so zaiyi. Abbu ma da safen nan kira biyu yayi mishi bai daga ba, ga shi yanzun sun fara shiga wajajen da babu network me karfi, ko shi tun yana gwada kira harya hakura ma, ko baccin kirki bai samu ba, lokaci zuwa lokaci yake kira yaji ko ta haihu.
"Har yanzun dai, da ta sauka din zan kiraka In shaa Allah"
Shine amsar da yake samu wajen Abbu. Ba dan baisan yawan yan gidan su gabaki daya ba, amman a daren sai da ya tsinci kan shi da kirgasu, saboda yana son yaga sau nawa Abbu ya jure tashin hankali irin wanda yake jin shi a ciki. Yama fi jinjinawa matan, dan yana da yakinin idan shine a matsayin su babu abinda zai hada shi da ciki. Yara ne ya ga na yan uwa sun ishe shi, amman da yake Allah yayi wa mata wata irin jarumar zuciya, sai ka sha wahalar nan kuma gobe ma ka sake maya wata. Babu kalar tunanin da baiyi ba, ciki harda na yanda da yasan cewar kaso kusan casa'in cikin matsalar shi bata da alaka da asibiti, da saiya tafi fannin mata wato Gynecology ko dan rana irin wannan.
Sanda ya sauka garin Kano, daga tasha kan shi tsaye asibitin da Layla take wanda na kudine ya tari mashin yana nufa. Tun bai karasa sauka ba yake kiran Abbu da ayi mishi kwatancen inda suke din, shisa sanda ya karasa Abbu din ma ya fito bakin kofar asibitin yana jiran shi
"Da ka zauna ai Rayyan"
Abbu yace bayan sun gaisa, kai Rayyan din ya girgiza mishi
"Hankalina ba zai kwanta ba Abbu. Gara ina nan din dai"
Da gaske yakeyi, dan duk abinda suke fada mishi jinsu kawai yake, yafi so yana gani da idanuwan shi. Sauran duk da tayi ba'a dadewa haka ake ce mishi ta samu bacci ba haihuwar bace da ta tashi zasu tafi gida, ko kuma gasu a hanya zasu koma. Amman yau har yanzun da suke takawa suna shiga cikin asibitin babu wani labari.
"Ayya..."
"Hamma..."
Ta fadi muryarta na rawa, idanuwanta cike da hawaye, kai Jabir ya girgiza. Zuciyar shi sam ba zata iya dauka ba. Baice abinda Layla tayi bashi da muni ba, amman tsakaninta ne da Ubangiji, a cikin duk tarin mutanen da suke mata surutu, suke nunata da yatsa babu wanda za'a binne su a tare, sanda za'a kaita a rufo a barta da ayyukanta ba lallai su sani ba, addu'ar neman Rahma ma ba lallai bane su bita da ita. Baisan inda tarin mutanen suka shiga ba a lokacin da ta samu makaranta, lokacin da tayi saukar Al'Qur'ani mai girma, duka bai gansu sun shigo tayata murna ko jinjina ma su Mami kan kokarin su ba.
Sai yanzun da kowa yake tunanin sunyi kuskure a rikon Layla, sai yanzun da ita kanta Layla din wani abu mai muni ya sameta, tarin mutanen da basu da masaniya akan kominta sune a gaba wajen yanke mata hukuncin da basuda hurumin yin haka. Yana gab da fara sakawa mutane hannu idan yana gidan suka shigo, baisan me yasa Mami bata binsu da tabarya ba, shi bashida wannan hakurin sam
"Ba zaki kare duka rayuwarki a cikin bango hudu na dakin ki ba Layla, idan baki fita da cikin nan ba zaki fita da yaro ko yarinya. Mutane suna magana yanzun, ba zasu daina magana ba, karki barsu, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure"
Jabir ya karasa maganar da wani irin yanayi a muryar shi da yasa hawayen da ke cikin idanuwan ta zuba
"Jabir ka kyaleta, me yasa baka da hankaline kai?"
Mami tayi maganar tana kokarin tarbe kukan da yake barazanar kwace mata, hijabin Layla ta karba tana sakawa a jikinta. Zuciyarta na wata irin dokawa kamar zata baro kirjinta. Mami bata hana su ba, tana kallo Jabir ya koma ya daukowa Layla takalmanta, fitar sukayi, daga farkon layin har titi, Layla tana jinta kamar babu kaya a jikinta saboda kallon da mutane suke binta da shi, kamar yanda Jabir ya fadane, ba zata cigaba da boyewa ba har abada, zancen ya rigada ya bazu, gara ta fara koyan yanda zatayi rayuwa da tabon da yake jikinta.
Sanda suka koma numfashi ma dakyar take fitar da shi, har bakin kofar dakinta Jabir ya rakata sannan ya tsaya yana fadin
"Babu hakkin mutane a kanki. Ba zan miki karya ba kin sani, duka rayuwar ki ta duniya ce ta samu tangarda, ba zancen zancen ki ba zai wuce a baku nan mutane ba, amman duk sanda zaki gifta zaki tuna musu abinda yake adane a zukatan sune, bansan al'adun mu na hausawa basawa mata adalci ba sai yanzun Layla, sai da rashin adalcin ya biyo ta cikin gidan mu...."
Wani irin numfashi Jabir yaja, bayason hawayen shi su zuba a gabanta, zai kara karya mata zuciya
"Ba zaki iya gyara tsakanin ki da mutane ba, ki gyara abinda kike da tabbas akan shi, ki gyara tsakanin ki da Allah, sai Ya tausaya miki ya gyara duniyar ki, karki bar su, karki bari su takura ki fiye da yanda kike a takure, kina jina"
Kai ta daga mishi tana goge hawayenta. Sai da yaga ta shiga daki sannan ya juya yana komawa wajen Mami ma da tun da suka fita tana zaune tana wani irin kuka mai cin rai
"Dan Allah ki rage sanyin halin nan Mami, ki daina barin mutane suna bi takan ki akan abinda baya karkashin ikon ki, idan ba zaki iya korar su ba Mami ki daina sauraren me zasu ce suna bata miki rai, dan Allah. Wallahi zuciyata zafi takeyi mun, sosai da sosai"
Cewar Jabir yana ficewa daga dakin saboda bayason ganin kukan da Mami takeyi. Har Abbu ya samu da daren ranar, dan Abbu ba zai manta yanda Jabir ya shiga dakin babu ko sallama ba
"Yaushe abin nan zai wuce mana Abbu? Me yasa mutane ba zasu kyale mu ba? Ina ruwan su da rayuwar mu?"
Hannu Abbu ya dan bubbuga a gefen shi yanawa Jabir din alamu daya je ya zauna, bai musa ba kuwa ya karasa yana zama inda Abbu ya nuna mishi, idanuwan shi sun kada sunyi ja, watakila da yayi kuka zai samu sauki
"Nagaji da ganin Mami na kuka kullum, ina jina so helpless..."
Dan murmushi Abbu yayi
"Ka kalleni Jabir, ban san inda nake samun karfin bude idanuwa ba a duk safiya, saboda wannan ne karo na farko da ko kalaman lallashi bani da su, damuwar ku gabaki daya ta tarar mun, ni ya kake tunanin ina ji? Um Jabir? Dan Allah ka dan kara daurewa, komai zaiyi sauki In shaa Allah"
Jabir ya dade zaune a dakin ya hade kan shi da gwiwa yana neman sauki koyaya ne. Kamar yanda shima Abbu yake tsaye a wajen yana neman sauki a yanzun, daga shi, Ayya sai kuma Mami a asibitin, da yake dare ya farayi sanda suka fito din, wajen sha daya. Addu'ar duk da tazo bakin Abbu ita yakeyi, kafin wayar shi da take aljihun shi ta fara ringing, yana fito da ita yaga Rayyan ne, yana dagawa ya saka a kunnen shi muryar Rayyan din ta daki kunnen shi
"Ina ta kiran Ayya bata daga ba, Mami ma haka, Layla fa? Nakudar ce ta sake dawowa ko Abbu? Ina magana da ita naji shiru, sai kira nakeyi itama bata dagawa"
Dan siririn numfashi Abbu ya sauke
"Gamu nan a asibiti m..."
Rayyan bai bari Abbu ya karasa ba yace
"Me suka ce? Ga shi dare yayi ni ba zan iya tahowa ba yanzun"
Duk da halin da Abbu yake ciki sai da yayi dan murmushi
"Ka kwantar da hankalin ka. Babu abinda zai faru sai alkhairi da yardar Allah, zan dinga kiran ka ina fada maka yanda ake ciki, kayi mata addu'a kai dai kaji"
Sai da ya amsa sannan sukayi sallama, su Mami ya kalla
"Rayyan ne"
Kai Mami ta jinjina, ko lokacin da ake maganar soyayya a dangin su, zancen baya wuce
"Anya akwai matar da tayi sa'a irin Maimunan Ahmadi?"
Ko da ta aure shi ta sabajin yanda ake fadin
"Maimunan Ahmadi"
Shisa sam bata jin kishin haka, zata so a yanzun na minti daya idanuwa da hankulan kowa su dauke daga cikin Layla su koma kan ita da Rayyan, tana da tabbacin tsantsar kaunar da take tsakanin su zai saka su fara sabon mamaki, ba kowanne namiji bane zaiyi abinda Rayyan din yayi. Ko ita maganar ta daketa da tajita daga farko, sai ta dinga ganin kamar mafarkine, duk da tasan da yawa zasu ce tayi azarbabi, kamar ta jira taga yanda zaman Rayyan da Layla zai kasance a karkashin inuwar aure kafin ta yanke hukunci akan tarin kaunar da suke yiwa juna. Sai dai ta kasa, tana da yakini mai girma akan kaunar Layla da take gani tattare da Rayyan din.
Watakila kuma idanuwanta ne suka rufe saboda nauyin da Rayyan din ya dauke mata na tunanin wanda zai zamo miji a wajen Layla, wanda zai kauda kai daga tabon da yake tare da ita harya ganta din, da tarin kalubalen da zata iya fuskanta daga wajen dangin shi idan har ta samu din ma. Duka rayuwar 'ya mace zagaye take da martabar da tabuwarta yake dai-dai da nakasun da zai taba gabaki daya ahalinta. Kuskure daya tak zai iya canza komai ta fannin da gyaruwar shi zatayi wahala. Dukan su a tsaye suke duk kuwa da kujerun da suke a wajen, babu mai natsuwar zama, kowa da abinda yake sakawa yana kwancewa a cikin zuciyar shi.
*
Motar farko ya samu daga Kaduna zuwa Kano, asuba ma a tasha yayita. Da yake Bappa ya kai shi, amman gani yakeyi kamar motar bata sauri, yau ne ya sake jin takaicin rashin iya tuqi, da yana da mota a hannun shi iya gudun da yake so zaiyi. Abbu ma da safen nan kira biyu yayi mishi bai daga ba, ga shi yanzun sun fara shiga wajajen da babu network me karfi, ko shi tun yana gwada kira harya hakura ma, ko baccin kirki bai samu ba, lokaci zuwa lokaci yake kira yaji ko ta haihu.
"Har yanzun dai, da ta sauka din zan kiraka In shaa Allah"
Shine amsar da yake samu wajen Abbu. Ba dan baisan yawan yan gidan su gabaki daya ba, amman a daren sai da ya tsinci kan shi da kirgasu, saboda yana son yaga sau nawa Abbu ya jure tashin hankali irin wanda yake jin shi a ciki. Yama fi jinjinawa matan, dan yana da yakinin idan shine a matsayin su babu abinda zai hada shi da ciki. Yara ne ya ga na yan uwa sun ishe shi, amman da yake Allah yayi wa mata wata irin jarumar zuciya, sai ka sha wahalar nan kuma gobe ma ka sake maya wata. Babu kalar tunanin da baiyi ba, ciki harda na yanda da yasan cewar kaso kusan casa'in cikin matsalar shi bata da alaka da asibiti, da saiya tafi fannin mata wato Gynecology ko dan rana irin wannan.
Sanda ya sauka garin Kano, daga tasha kan shi tsaye asibitin da Layla take wanda na kudine ya tari mashin yana nufa. Tun bai karasa sauka ba yake kiran Abbu da ayi mishi kwatancen inda suke din, shisa sanda ya karasa Abbu din ma ya fito bakin kofar asibitin yana jiran shi
"Da ka zauna ai Rayyan"
Abbu yace bayan sun gaisa, kai Rayyan din ya girgiza mishi
"Hankalina ba zai kwanta ba Abbu. Gara ina nan din dai"
Da gaske yakeyi, dan duk abinda suke fada mishi jinsu kawai yake, yafi so yana gani da idanuwan shi. Sauran duk da tayi ba'a dadewa haka ake ce mishi ta samu bacci ba haihuwar bace da ta tashi zasu tafi gida, ko kuma gasu a hanya zasu koma. Amman yau har yanzun da suke takawa suna shiga cikin asibitin babu wani labari.
"Ayya..."