← Book details Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 36 OF 93

Sashe 36

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Ni fa ba zan shiga net kamar kifi ba..."

Dan murmushi ne ya kwace mishi yanzun daya tuna mitar da Bilal yai tayi har washegari. Yakan yi tunanin ko bakin Bilal na mishi ciwo wani lokacin saboda mitar tsiya. A haka su Ayya suke cewa Bilal salihi, Bilal baya magana. Bayan har tsegumi yakeyi, shi kadai kuma yake yiwa, baisan ko Aisha naganin wannan bangaren na Bilal ba. Komawa yayi ya zauna, haka kawai wannan karin saiya kasa samun natsuwa, lokaci zuwa lokaci yake tsintar kan shi da kallon Layla da take bacci. Mikewa yayi ya karasa wajen kofa yana kama labulen dakin ya daga shi sama. Fankar dakin ya kurewa gudu duk da an dan fara alamar sanyi. Ya karasa ya bude net din Layla yana rufa mata bargo.

Duk da haka ya kasa samun sukuni, bai daina jin zufar rashin dalili ba duk kuwa da fankar dakin daya kure

"Me yake damuna ne haka?"

Ya furta a hankali. Kwayoyin shi ya tashi ya dauko ya sha yana mayar dasu ya adana. Amman har wajen awa biyu tsakani bai samu natsuwar da yake nema ba. Wata takardar ya dauka ya dora akan ta zanen da yakeyi yana rufa babban towel din daya siya domin hakan kawai ya dora kan shi akan tebir yana kwanciya. Kallon Layla yake da take bacci hankalinta a kwance, ba zai ce ga asalin abinda yake tunani ba, amman rabon da bacci ya dauke shi sha biyu saura ko da taimakon kwayoyi an dade, yau bacci mai nauyine ya dauke shi.

Karfe wajen biyu da rabi hankalin Bilal ya kasa kwanciya, duk yanda yaso yayi bacci saiya kasa, kalaman Abbu na danne shi. Yana jin kamar ya kamata ace ya fadawa Rayyan bai kamata su kwana daki daya da Layla ba, amman sai yayi shiru ya bar shi. Abin kuma ya dame shi sosai da sosai. Tashi yayi ya fita. Hango fitilar dakin su yayi a kunne, kwanakin nan da wuta suke kwana. Yana mamakin yanda labulen dakin yake a dage. Yasan Rayyan, ko shara Bilal din zaiyi ya daga labule sai yaita masifa, quda zai shigo musu daki.

Ya rasa hadin Rayyan da qudaje, ko kwara daya yaga gaccin shi a daki sai ya fitar dashi, ko ya kashe shi hankalin shi yake kwanciya. Balle kuma sauraye, ko jiya dariya Bilal yayi kamar zai shaqe jin Rayyan din na ma sauro masifa

"Dan ubanka idan sha zakayi ba zaka sha ka wuce ba, sai kana mun ihu a kunne"

Yanzun ma dariya ya tsinci kan shi dayi. Yana karasawa dakin. Bacci Rayyan yakeyi akan tebir, ko tunanin ciwon wuya bayayi. Cikin dakin sosai ya shiga, ya dauki maganin sauro na fesawa yana dan fesa musu saboda Rayyan din. Hannu ya saka cikin net din yana janyo dayan pillow din, ya mayar ya gyara. Dan bubbuga Rayyan din yayi daya bude idanuwan shi da suke cike da bacci

"Ka sa pillow hamma, wuyanka zaiyi ciwo"

Karbar pillow din Rayyan yayi yana ajiyewa ya mayar da kan shi ya dora, idanuwan shi ya lumshe saboda baccin da yake cikin su, sai yakejin kamar yayi kwanaki baiyi bacci ba. Wani irin numfashi Bilal ya sauke yana jinjina al'amarin su. Kafin ya fice, dan shima hamma yakeyi, idanuwan shi cike suke da bacci, hankalin shine ba'a kwance ba sai yanzun.

*

Zai iya cewa tunda safe yake tashi yayi wanka, wajen karfe hudu na safe wasu lokuttan. Yau ma da kan shi ya dora ruwa a kettle yaje ya sirka ya tashi Layla da ta dinga turo mishi baki kamar zatayi kuka. Duk da yasan babu mai fitowa sai da ya tsaya ta wajen hanyar bandakin har tayi wanka ta fito. Lokacin na shi ruwan yayi zafi, da duka kayan shi har wanda zai sake ya shiga bandakin. Yana fitowa ya tsoma wanda ya cire a wani bokitin yana zuwa ya wanke su. Alwala ya daura, saida ya kwankwasa dakin ganin Layla ta saki labulen, muryarta da alamar bacci ta amsa shi.

Hakan yasa shi ya shiga, ya sake komawa ta kudundune cikin bargo. Kai kawai Rayyan ya girgiza. Bayason jikin shi ya bushe shisa ya shafa mai, turaruka ya fesa, yana jin shi a dai-dai. Har wani shiru yake ji cikin kan shi babu wata hayaniya saboda baccin daya dan samu. Share dakin ya karayi yaji kamar ya taka kasa. Zuwa lokacin har anyi kiran sallar farko, masallaci ya fita, kafin a tashi sallah zai samu yayi raka'a biyun da yake sunna mai karfi kafin asuba. Ko da aka idar da sallar asuba ya dade a zaune cikin masallacin, ba lazumi yakeyi ba ko wani abu, kawai lokutta da dama yakan samu natsuwa a cikin masallaci.

Wani lokacin kuma kamar ana mintsinin shi haka yake so ya idar da sallah ya fita, shisa baya wasa da ranaku irin na yau. Sai da ya gaji da zaman sannan ya tashi ya fita. Dakin su ya koma, karfe takwas da rabi yake da darasi, yana nan zaune yana dan dudduba wasu abubuwan da bai fahimta ba har takwas saura, yana da biskit, da shayi ya hada yana cikin shane Hindu ta bude ido, tafi mintina biyar kafin tace

"Hamma...ina kwana"

Sai da ya ajiye kofin da yake hannun shi sannan ya amsa da

"Ya jikin ki?"

Taji sauki sosai, daman kwana biyun farko sunfi wahalar da ita

"Naji sauki..."

Ta furta a hankali, cigaba da shan shayin shi yayi harya gama

"Ina da lecture da safen nan"

Tashi zaune Layla tayi

"Nima haka... Karfe tara, sai mu wuce tare"

Kai Rayyan ya jinjina

"Zaki iya zuwa?"

Nade net din tayi tana sauko da kafafuwanta daga kan katifar

"Eh mana..."

Bai mata maganar taci wani abu ba, tunda yasan daga ita har Bilal basa iya cin abinci da safe haka. Shikam ko da asuba ne zaici, sai dai in bayajin yunwa. Iya abinda zai tafi dashi na ranar ya harhada ya dauko jakar shi yana kara shiryata ya saka a ciki. Ta riga da ta sake kayanta sanda ta fito, ta mayar da wancen cikin ledar da tazo da ita. Mayafin da ta ajiye akan gado ta janyo, doguwar rigace ta atamfa, mikewa Layla tayi tana duba ledar ta dauko dankwalin rigar ta ajiye. Ta karasa ta dauki ledar ruwa, fuskarta da bakinta take son daurayewa. Anan bakin kofa ta tsaya, tana jin idanuwan wani da batasan waye ba a cikin gidan yana kallonta, ko daga kai batayi ba harta karasa ta koma dakin.

Dankwalin ta daura tana rataya mayafin a kafadarta

"Muje?"

Ta cewa Rayyan, ba kwalliya bace a fuskarta, har lokacin idanuwanta da alamar bacci, amman zuciyar shi dokawa take kamar zata fito waje. Sam ya rasa yanda zaiyi da abinda yake ji akan Layla yanzun, bayason yanda take birkita mishi lissafi haka. Tare suka fito, jan dakin kawai yayi, idan Bilal ya fito ya rufe, yana da mukulli a jakar shi. Baibi takan wasu cikin yan gidan da suke ta binsu da kallo ba har suka fice daga gidan

"Hamma kana sauri"

Layla ta fadi, juyawa Rayyan din yayi, ya kamo hannunta, suka taka zuwa titi, saboda ita yau zai hau abin hawa da safe zuwa makaranta, saboda kuma bata da lafiya.

*

Littafina na siyarwa ne akan naira #300

Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank

Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Dec 1, 2020

14

Kwance yake yana juyi. Maganganun Bilal ne suke mishi yawo, duk idan ya zauna haka kawai sai su dinga dawo mishi. Baisan me yasa Bilal din zai fada mishi su ba

"Tuntuni ya kamata in maka magana Hamma, tun ranar farko da naga hannun Layla cikin naka ya kamata in tuna maka rashin dacewar haka, in tuna maka yanda tasowa gida daya a karkashin kulawar Abbu bai saka halaccin nan a tsakanin ku ba. Ka daina tabata, idan kana son ta ne kayi wani abu a kai ta zama mallakin ka, amman ka daina..."

Bai amsa Bilal din ba sanda yayi mishi maganar, a cikin makaranta ne, shi yayi jarabawar safe, Bilal din kuma yana da ta azahar, haka ma Layla, baisan dalilin su na shigowa makarantar tun wajen sha biyu saura ba. Layla na karasowa wajen yaji ta riko mishi hannu ta baya, kusan rabin jikinta akan nashi, zai iya cewa ta rungume shine ta gefe

"Hamma..."

Ta fadi cike da wani nishadi da baisan dalilin ta nayin shi ba. Kuma a gaban Bilal din ya bambareta daga jikin shi. Ba zai manta da hawaye tabar wajen ba. Bai tuna rana daya da ya cewa Bilal shi yana son Layla ba, maganar ma wata irin dirar mikiya tayi mishi, tana hautsina wani abu a tare da shi da baisan yana a nutse ba. Yana zaman shi lafiya, yana lallaba rashin natsuwar da yake fama da ita a duk rana, Bilal yazo ya kara mishi wani tunani na daban. Ya saka shi yana neman ma'anar alakar da take tsakanin shi da Layla. Bai saba yawan magana ba, rabin da kwata na maganar da yakeyi a rayuwar shi tsakanin shi da kan shine, a iya tunanin shi maganganun suke makalewa.

Kuma bai saba yiwa kan shi karya ba, yasan yanda yake jin Layla da ban da yanda yake jin su Rukayya, da sai yace ita din matsayin kanwa take a wajen shi. Duk da a ranar ne maganganun Bilal suka saka shi tantance hakan. Shi baice yana son ta ba, bai taba tunanin wata soyayya ba, bayajin yana da natsuwar janyo wata duniyar shi da take a hargitse. Me yasa ma Bilal din zai hargitsa mishi lissafi har haka, yanzun yana saka duk lokacin da jikin Layla zai hadu da nashi sai yaji wani irin tashin hankali na daban. Ya kuma rasa ta inda zai fara hanata rike shi ko da shi bai kokarin riketa ba.
Chapter 36 · 0% Book details