← Book details Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 93

Sashe 16

Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ahmadi ya kira cike da kashedi, sauran karshen sigarin daya rage Bilal ya dago hannun shi yana nunawa Ahmadi da fadin

"Ba shi bane Abbu, ni ne"

Ya karasa maganar muryar shi na fitowa can kasan makoshi

"Bilal"

Wannan karin da mamaki Ahmadi yai maganar, badan baya ganin samari sa'annin su Bilal da wanda ma basu kaisu ba da shan abinda yafi sigari, sai dan haline da ko a mugun mafarki bai hango Bilal din dayi ba

"Sigari Bilal? Ina kuke so in saka raina, kamar Rayyan bai ishi sakani juyi duk dare ba, sai ka fara kaima ko? Hawan jini kuke son ganin na samu? Kun kyauta mun kenan yanzun? Um? Bilal ka kyauta mun?"

Kan shi Bilal ya sadda kasa, yanajin wani abu na taso mishi tun daga dan yatsan kafar shi har zuwa kirjin shi inda yai mishi karan tsaye a zuciyar shi.

"Allah ya kyauta"

Ahmadi ya fadi yana juyawa ya fice daga dakin, zuciyar shi zafi takeyi, duk da wani bangare na zuciyar shi da yake jin kamar bai kyauta mishi ba wajen jin dadi da ba Rayyan bane ya sha sigarin, a lokaci daya wani abu da baiyi tunani bane yaji ya karya a zuciyar shi, kamar Bilal ya karya yardar da yayi mishi ne. Saboda ko a cikin mutane yakan yi alfahari da halayen Haris da Bilal, yakan ce zai shaidi yaran nashi su biyu akan komai. Idan shima yace zai fara rashin jin nan baisan inda zai saka kan shi ba.

Da yawan mutanen da suke zagaye da shi kanyi zaton hakurin da yake da shine raunin shi, yana mamaki yanda mutane suke daukar hakuri a matsayin rauni. Sam hakuri ko da yayi yawa baya taba zama rauni, idan baka da karfin zuciya ba zaka iya hakuri akan lamurra da yawa ba, sai juriyarka ta kai wani mataki ne zaka iya kauda kai akan wasu abubuwan. Hakurin shi ne karfin zuciyar shi, yaran shi sune raunin shi, yaran shi sune cikon farin cikin shi, tunda ya same su duk inda zai juya da tunanin su manne da zuciyar shi.

Kaddara ce ta bashi Layla da Bilal, duk da jinin shi na yawo cikin nasu, amman basu da gadon shi, shisa a duk cikin yaran Bilal ne kadai ya taba siyan fili da sunan shi, takardun na ajiye ko Maimuna bata san da shi ba, yana jin yaran inda yake jin su Haris. Da gaske yake wani abu ya karye a zuciyar shi, baisan wani zazzabin tashin hankali ya rufe shi ba saida ya watsa ma jikin shi ruwa yaji tsikar jikin nashi na mimmiqewa da alamun wani sanyi da yake ratsa shi.

Ko da Maimuna ta shigo yayi duk wani kokarin shi na ganin bata karanci damuwar da yake tattare da ita ba, abincin da ta kawo haka ya dinga saka shi a baki yana taunawa yana hadiyewa, lomar da yaji ta kakare a makoshin shi sai ya bita da ruwa. Da tayi magana kan canjin yanayin shi ca yayi mata

"A gajiye nake jina Maimuna, kamar gajiya ke son saka mun zazzabi"

Da ta bashi maganin zazzabi bai musa mata ba ya karba yana hadiya tunda da gaske yanajin zazzabin. Sai dai barawon bacci ma kasa samu yayi duk da ya raya daren ne da salloli yana rokama yaran nashi karin shirya, addu'ar tashi na yawaita akan Bilal, Rayyan da kuma Layla. Saboda yanda yake jin kamar duk wata kaddara da zata same shi ta bangaren yaran da wahala ta wuce kan su ukkun, tunda su kadai ne suke caja mishi kai har haka.

*

Tunda Ahmadi ya fice daga dakin babu wanda ya motsa a cikin su har lokacin, Bilal jin shi yake kamar iskar da yake shaka bata kaiwa cikin shi, kamar iskar dakin gabaki dayanta tayi mishi kadan, hakan ne yasa shi takawa yaje inda makunnin fankar dakin take yana kure gudunta gabaki daya. Tsaye yayi a wajen yana sauke numfashi cikin son yaji ya koma mishi yanda yake da kafin maganganun Abbu. Sai dai me, yana juyawa yaji komai ya jagule mishi, ganin Rayyan ya dauko zaro kwalin sigarin shi daga cikin aljihu yana zaro lighter din shi, ya bude kwalin ya zaro kara daya ya saka a bakin shi yana riketa a tsakanin labban shi, kafin yayi ma karshen sigarin rumfa da hannun shi ya kunna wutar lighter din gudun kar iskar fankar ta hure mishi

"Hamma..."

Bilal ya kira da duk wani bacin rai da zai iya dorawa a kan muryar shi. Satika ukku da suka wuce yana kwance Rayyan din ya shigo dakin, sai da gaban shi ya fadin jin warin sigarin da yake yi

"Hamma warin sigari kakeyi, daga ina kake?"

Shine tambayar da yayi wa Rayyan din yana mikewa zaune babu shiri, da wani yanayi a fuskar Rayyan din yace

"Da gaske? Warin kaji a jikina?"

Kai Bilal ya daga mishi yana tabbatar mishi, baice komai ba ya taka inda suke ajiye turarukan su ya dauki daya yana fesa ma jikin shi, hadi da dan daga hannayen shi yana shakar iskar ko zaiji warin sigarin da Bilal yace yaji yanayi

"Yanzun fa?"

Ya bukata, yana saka Bilal din binshi da wani irin kallo

"Daga ina kake? Me yasa kake warin sigari?"

Kujera Rayyan yaja ya zauna batare da yace komai ba, hakan yakan yi duk idan Bilal yayi mishi tambayar da yasan idan ya amsa mishi ita zai sake bude mishi kofar jifan shi da wasu sababbin tambayoyin ne. Daga waje yake, kuma yana warin sigari ne saboda ya sha, idan ya amsa Bilal zai fara tambayar shi dalilin da ya saka shi shan sigari, kuma shi da kan shi baisani ba, wucewa yazo yi yaga wasu gungun samari anan kasan layin su sun taru suna ta sha, baisan meye dayan abin ba, sigarin kawai ya iya ganewa, kuma haka kawai yaji a duniya babu wani abu da yake son yi banda ya sha sigari.

Shagon da yaje siye sai da mutumin ya tambaye shi har sau biyu idan sigari yake son siye

"Malam idan babu ne ka fadamun in tafi"

Rayyan ya fadi maimakon amsa tambayar da mai shagon yayi mishi

"Akwai, wacce iri?"

Cewar mai shagon da wani yanayi a muryar shi

"Ni dai kabani kowacce iri"

Hakan kuwa ya siyi sigarin da sai bayan an bashi ita da lighter din daya siya yabar shagon tukunna ya duba kwalin yana ganin an rubuta aspen a jiki. Zuqar farko da yayi wani irin tarine ya sarqe shi kamar zai shide, amman yana gama dawowa ya sake gwadawa, har ya sha kara biyu bai gane dalilin da yasa mutane suke sha ba, banda bakin shi, da makoshin shi da yaji suna wani qauri-qauri, kirjin shi a cike yake fal da hayaqi. Daga ranar ne kullum idan ya fita sai ya busa yakai kara biyar, har zuwa yanzun ba zaice ga dadin sigari ba, ba zaice ga dalilin shi na sha ba, abu daya zai iya shaidawa, yanda idan yaji yana son sha din jikin shi har wani iri yake yi mishi.

Ya gane dalilin da yasa ake cewa sigari na da wahalar barin sha, duk sanda zai sha a waje zai saka minti a bakin shi dan ya daina warinta, amman shekaranjiya har Ayya sai da tace

"Ni kam bansan inda hancina yake dibomun warin sigari ba"

Sanda ya shiga ya dauki abinci, hakan yasa shi yana shiga daki ya sake kayan jikin shi yana kuma watsa ruwa. Bilal a satika ukkun bai gaji da tambayar shi ba, shikuma bai daina yi mishi shiru ba, har sai jiya da yaji yana son ya sha, amman bayason fita daga gida kuma, saboda zaune yake yana zane, yanzun daya zana jarabawar shi ta gama sakandire yana zaune jiran sakamako ya fito, yakan tsinci kan shi da jin kadaici na rashin abinyi. Musamman idan Bilal yana makaranta, shisa zanen ne kawai abinda yake debe mishi kewa, ba abokai yake dasu ba ko a cikin unguwa ballantana yace zai fita suyi hira.

Idan yagaji da zama a daki yakan fito ko zai ga giccin Layla, haka zai ta mata aiken rashin dalili har saita kosa ta mayar mishi da magana yaga yasa ta kuka tukunna, to jiyan sam bai ganta ba, sanda ya aika a kirata ance mishi kanta yake ciwo ta sha magani ta kwanta. Zai iya cewa harda son ya ganta da yakeyi, ya duba yaga ya jikinta da kuma kin son ganinta da ya hade mishi waje daya ya kara mishi son busa hayakin, ko ba komai zai kalli yanda ya gwanance yake fitar da samfur samfur na hayakin cikin satika kadan haka.

Ya zuqa sosai yana fito da hayakin Bilal ya shigo, bai ma gama ba ya koma mishi ciki yana saka shi fara tari

"Hamma..."

Bilal ya fadi da bayanannen tashin hankali yana karasawa inda Rayyan din yake hadi da mika hannu zai karbe sigarin, Rayyan ya janye hannun shi yana fadin

"Meye haka? Ka daina yi kamar baka san ina sha ba"

Ya san yana sha, tun ranar farko da yaji warinta a jikin shi, da yana da abokai ne ma sai yayi zargin wani daga cikin sune yake shan sigarin suka zauna waje daya har jikin shi ya dibo warin hayakinta, amman Rayyan ne, bashi da zuciyar hakuri da mutane har suyi sabon zama abokai, koya kaso jurewa shine zaiyi fada da kai ya daina maka magana.

"A waje kake sha, me yasa zaka fara a cikin gida? Me yasa? Idan Ayya ta gani fa? Idan Abbu yagani me zaka ce?"

Sake kai sigarin shi Rayyan yayi a bakin shi yana zuqa hadi da fitar da hayakin

"Dan Allah, dan girman Allah ka kashe, idan dole ya zame maka sai kasha, kayi a waje, kar kabari Ayya ko Abbu sugani... Ni dai na roke ka"

Bilal din ya fadi kamar zaiyi kuka, idan har zuciyar shi na zafi akan wannan sabuwar dabi'ar da Rayyan ya kwaso musu, baisan me Ayya da Abbu zasuji ba, maimakon halayen Rayyan din su gyaru, kullum kara watsewa suke kamar ba'a mishi addu'ar shiriya

"Hamma..."

Bilal ya kira yana kallon yanda Rayyan din yake cigaba da busa tabar shi kamar bada shi yake magana ba. Idan yayi wani abin Layla tace
Chapter 16 · 0% Book details