Sashe 17
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Jujun ne ya motsa"
Sai abin yaba Bilal dariya, amman yanzun da gaske ya fara yarda da maganarta, Rayyan ba zai rasa almatsutsai ba, in ba haka ba, kana zaune lafiya ba zaka tattago abinda zai saka ran kowa da yake kusa da kai ya baci ba. Tsaye yayi har sai da ya gama shanye sigarin, dan yasan idan gidan Radio zai bude a wajen saboda surutu Rayyan ba zai kula shi ba. Karshen da ya ajiye kan tebir Bilal ya dauka ya saka a aljihun shi
"Ka rufa mun asiri, ka boyeta inda wani ba zai gani ba"
Daukar kwalin Rayyan yayi yana sakawa cikin aljihun wandon shi. Yana sake gyara zama a cikin kujerar da yake zaune, yana kallon Bilal din ya dinga feshe dakin da turaruka. To yau ma da yayi sallar isha'i a waje ya tsaya suna zancen wasan kwallon kafa da matasan unguwa shisa bai shigo gida da wuri ba, ganin lokaci na jira, kuma yasan Ayya na can tana tunanin dalilin da yasa har lokacin bai shiga ya dauki abincin ba yasa shi yi musu sallama ya shigo gida. Yayi niyyar wucewa bangaren Ayya kai tsaye, sai kuma yaji yana son shiga bayi, shisa ya nufi dakin su, inda ya sami Rayyan zaune yana shan sigarin shi kamar yana abin kirki.
Fada yakeyi kamar zai ari baki, ya karasa ya kwace karshen sigarin kenan ya kasheta jikin tebirin da yake ajiye ya sake bude baki zaiyi magana Abbu ya shigo. Tun tasowar su akwai kananun laifuka da Rayyan din zaiyi ya dauke mishi su, zuwa yanzun kuma ko a aiko Rayyan ya kira shi bai fada mishi ba, zai ce ya fada shine ya manta baije kiran ba, irin kananun abubuwa haka da zai iya dauka na laifukan Rayyan duk yanayo. Shisa yau sam karyar cewa shi yake shan sigarin batayi wahalar fitowa daga bakin shi ba sam. Musamman da yaga abinda yake cikin idanuwan Abbu, yanda ya nuna ba zai iya jure wata gurbatacciyar halayya daga bangaren Rayyan din ba.
Sai dai maganganun shi sun daga hankalin Bilal fiye da yanda yayi zato, ya dauka maganganun sun taba zuciyar Rayyan, sai yanzun da yake kallon shi ya sake kunna sigarin shi kamar komai bai faru ba, kamar Abbu bai fadi abinda ya fada ba
"Anya akwai hankali a tattare da kai kuwa Hamma? Ko zuciya ce kai ba'a halliceka da ita ba, da gaske sigarin kake kara kunnawa? Baka ga halin da Abbu ya fita a ciki bane halan? Baka ga me kasa nayi ba?"
Karan sigarin Rayyan ya cire daga bakin shi, saboda baiga dalilin da zaisa Bilal ya tsare shi yana mishi fada kamar kanin shi ba
"Me nasa kayi?"
Ya bukata yana tsare Bilal din da idanuwa, dariyar takaici mai sauti ce ta kwacewa Bilal din
"Tambayata kakeyi? Hamma tambayata kakeyi?"
Yana kallon yanda kowa a gida yake fadin ba'a batawa Bilal rai, jinsu kawai yake, ko suce Bilal na da hakuri, Bilal baya fada, Bilal baya fushi, suna magana kamar a duniya babu wanda yake da halaye nagartattu kamar Bilal, bayan rana bata fitowa ta fadi baiga kalar rashin hakurin Bilal ba, baya saukewa akan kowane sai shi, yanzun ma ga bacin rai nan bayyane a fuskar shi
"Ka daina girmamani kana kirana Hamma, kana kuma hadawa da ihu a karshen zancen ka"
Karasawa Bilal yayi inda Rayyan din yake yasa hannu ya dauki kwalin sigarin da ya ajiye da lighter din, hannu Rayyan ya dago, kallon da Bilal yayi mishi yana saka shi mayar da hannun
"Woo... Allah ya baka hakuri"
Rayyan ya fadi yana dariya ganin yanda ran Bilal din ya baci da gaske, shikuma a cikin abinda ya faru duka baiga wani abu na bacin rai ba, sigari ce ya fara sha baisan dalili ba, yanzun kuma bashi da wani dalilin dainawa. Shi baice Abbu yaji haushi dan ya sha sigari ba, baice Bilal ya dauki laifin da ba na shi ba, yana kallon shi tun tasowar su yana hakan, so yake yanda bai taba tambayar shi dalili ba, shima ya daina tambayar shi dalili akan abubuwa irin haka. Yana kallo Bilal ya fice daga dakin, mikewa yayi yana shiga wanka abin shi, idan Bilal ya gama fushin ya huce zai neme shi ya sani.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 14, 2020
07
Bai fara dana sanin neman gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello da take garin Zaria ba sai da ya samu. Bai san sa'a bace ko kuma matakan su daya tsallake ko kuma sanayya ta manyan mutane da Abbu yayi ta saka shi samun abinda ya nema. Kawai dai yasan ya fara dana sani ne daga jiya da Haris ya dawo har dakin su ya shigo da sallamar shi yana zaune, maganar shi ta farko bayan sun gaisa ita ce
"Abbu yake fadamun ka samu gurbin karatu a makarantar mu, shine ko ka kira ka sanar dani. Naji dadi wallahi, saboda duk bangaren lafiya dai ne"
Tsayawa yayi yana kallon Haris da yake magana kamar ya fada mishi ya zabi karantar fannin daya danganci kwakwalwa da sanin halayyar dan Adam wato Psychology saboda ya kasance waje daya da shi. Ya zabi fannin ne saboda yana son fahimtar wasu daga cikin halayen shi, wasu cikin tarin tambayoyin da yake tunanin bangaren zai amsa mishi akan kan shi, badan wani dalili ba. Kuma ko ba komai kaunar da yake ma uniform zai kasance yana saka farar rigar nan lokaci zuwa lokaci. Saka uniform ne abu daya da yayi kewa bayan gama sakandire din shi. Haka kawai sai yaga duk kayan da zai saka ba zasu kai yanda yake saka uniform yin kyau ba.
Wani lokaci can baya kaunar da yake ma uniform ta saka shi tunanin aikin soja, sai dai har kasan zuciyar shi yaji haka kawai ba zai iya nisa da gida ba, kuma bayason takurar da take tattare da aikin, yana da taurin kan da yake da tabbacin zai wahala a aikin. Zuciyar shi ba tada sanyin da zata lankwasu yayi biyayyar da yaji ana labarin yiwa manya. Shisa bai kara barin tunanin ya dame shi ba, kafin ya yanke hukuncin zabar fannin da ya zaba yanzun, yayi tunani kala-kala, ayyuka barkatai sun zo ran shi. Sai dai zuciyar shi tafi rinjaye akan Psychology din ne.
Haris din kuma yana bangaren lafiyar yara ne wato Pediatric. Ba shiga harkar kowa yake ba a gidan banda Bilal, anso hada su daki daya. Tashin hankalin da ya dinga yine yasa su Abbu suka bar su shida Bilal a daki daya. Lokacin da yaji labarin bangaren da Haris ya samu gurbin karatu da Bilal kawai yayi zancen
"Hamma zaiyi kyau da likitan yara...ko a gidan nan ka kalli yanda su Intisar ke son shi. Ko masallaci muka fito ba zaka rasa ganin shi rike da wani yaron ba"
Murmushi Bilal yayi
"Duk yaushe ka kula da Haris haka?"
Harar Bilal yayi
"Dan bana shiga harkar kowa baya nufin bana kula da abinda yake faruwa"
Jinjina kai Bilal yayi
"Naga alama ai, ko Ayya zancen da tayi mun kenan. Sanyin halin shi ne yasa yara suke manne da shi, ga kyauta kuma, ba zaka raba aljihun shi da dan biskit ko alawa ba"
Rayyan kwanciya ya gyara yana yin shiru, surutun Bilal ya cigaba da yi har saida ya kule
"Wai bacci kayi ko wulakanci ne yasa kayi banza ka kyaleni ina ta zuba ni kadai?"
Ba baccin da yakeyi, ya lumshe idanuwan shine, yana jin shi, a duka zancen shi babu wanda zai bada amsa, a wajen shi hirar ta rigada ta kare, ya fadi abinda yake son fada. Duk da yaso hirar tayi tsayi sai Bilal din ya kunna shi da maganar da yayi kan yaushe yake kula da halayen Haris. Yana so ya mayar da shi kamar baisan abinda yakeyi ba. Shisa sam mutanen da yake ji a ran shi basu da wani yawa, saboda halayen su na saurin cakar da shi.
Jiyan ma kallon Haris ya dinga yi, har ya gama surutun da zaiyi. Ganin ba amsa shi zai ba yasa ya tashi ya fita daga dakin. Yanayin fuskar shi ma ya bala'in bata ma Rayyan din rai, saboda haka kawai ba gayyato shi yayi ba, baice ya shigo daki ya same shi ba. Da suka gaisa bai sashi zama ya fara mishi hirar rashin dalili ba, yazo yasa yanajin kamar yayi mishi laifi. A fuska ya nuna baiji dadin shirun da yayi ba.
"Tsalle kake so inyi mu rungume juna saboda zamu kasance a makaranta daya ko me?"
Rayyan din ya furta cikin sigar mita yana karasa maganar da jan tsaki. Yana da dalilai da yawa da yasa baya shiga harkar kowa. To yau ma yana haduwa da Haris din yake tambayar yaushe yake da niyyar zuwa ya fara hada-hadar registration
"Ko zamu tafi tare gobe ne?"
Kai ya girgiza mishi, da alamar kosawa a muryar shi yace
"Zan taho da kaina Hamma..."
Dan jim Haris din yayi, yana son duka yan uwan shi, ba su kadai ba, shi mutum ne na mutane. Wasu lokuttan Rayyan na saka shi son tambayar shi ko ya taba mishi wani abune da bai sani ba shisa yake karayin kicin-kicin da fuskar shi duk idan sun hadu. Shi bayaso ya bata ran kowa sam-sam, ko wani yagani cikin bacin rai yakan yi kokarin ganin yaja shi da raha har saiya murmusa. Tun tasowar su abu kadan Rayyan bai taba duba cewa ya bashi shekaru kusan ukku ba, haka zai kama shi da jibga kamar ganga. Da suka fara hankali kuma baya magana da shi, in zasuyi haduwa goma idan bai mishi magana ba zai rabe gefe kamar bayason wani abu ya hadasu.
Ranakun duk da Rayyan ya fara mishi magana to na farko ba zai manta ba, rashin lafiya yayi harya kwanta asibiti, da sukaje duba shi yayi mishi ya jiki, amman yana iya yin jinya. Rayyan din ya shiga dakinsu da sunan duba shi, bayan sallama zai iya mintina goma a tsaye ya jingina bayan shi da bangon dakin, har sai in shi ya gaji da jin shirun yai yawa yace
"Rayyan..."
Sai abin yaba Bilal dariya, amman yanzun da gaske ya fara yarda da maganarta, Rayyan ba zai rasa almatsutsai ba, in ba haka ba, kana zaune lafiya ba zaka tattago abinda zai saka ran kowa da yake kusa da kai ya baci ba. Tsaye yayi har sai da ya gama shanye sigarin, dan yasan idan gidan Radio zai bude a wajen saboda surutu Rayyan ba zai kula shi ba. Karshen da ya ajiye kan tebir Bilal ya dauka ya saka a aljihun shi
"Ka rufa mun asiri, ka boyeta inda wani ba zai gani ba"
Daukar kwalin Rayyan yayi yana sakawa cikin aljihun wandon shi. Yana sake gyara zama a cikin kujerar da yake zaune, yana kallon Bilal din ya dinga feshe dakin da turaruka. To yau ma da yayi sallar isha'i a waje ya tsaya suna zancen wasan kwallon kafa da matasan unguwa shisa bai shigo gida da wuri ba, ganin lokaci na jira, kuma yasan Ayya na can tana tunanin dalilin da yasa har lokacin bai shiga ya dauki abincin ba yasa shi yi musu sallama ya shigo gida. Yayi niyyar wucewa bangaren Ayya kai tsaye, sai kuma yaji yana son shiga bayi, shisa ya nufi dakin su, inda ya sami Rayyan zaune yana shan sigarin shi kamar yana abin kirki.
Fada yakeyi kamar zai ari baki, ya karasa ya kwace karshen sigarin kenan ya kasheta jikin tebirin da yake ajiye ya sake bude baki zaiyi magana Abbu ya shigo. Tun tasowar su akwai kananun laifuka da Rayyan din zaiyi ya dauke mishi su, zuwa yanzun kuma ko a aiko Rayyan ya kira shi bai fada mishi ba, zai ce ya fada shine ya manta baije kiran ba, irin kananun abubuwa haka da zai iya dauka na laifukan Rayyan duk yanayo. Shisa yau sam karyar cewa shi yake shan sigarin batayi wahalar fitowa daga bakin shi ba sam. Musamman da yaga abinda yake cikin idanuwan Abbu, yanda ya nuna ba zai iya jure wata gurbatacciyar halayya daga bangaren Rayyan din ba.
Sai dai maganganun shi sun daga hankalin Bilal fiye da yanda yayi zato, ya dauka maganganun sun taba zuciyar Rayyan, sai yanzun da yake kallon shi ya sake kunna sigarin shi kamar komai bai faru ba, kamar Abbu bai fadi abinda ya fada ba
"Anya akwai hankali a tattare da kai kuwa Hamma? Ko zuciya ce kai ba'a halliceka da ita ba, da gaske sigarin kake kara kunnawa? Baka ga halin da Abbu ya fita a ciki bane halan? Baka ga me kasa nayi ba?"
Karan sigarin Rayyan ya cire daga bakin shi, saboda baiga dalilin da zaisa Bilal ya tsare shi yana mishi fada kamar kanin shi ba
"Me nasa kayi?"
Ya bukata yana tsare Bilal din da idanuwa, dariyar takaici mai sauti ce ta kwacewa Bilal din
"Tambayata kakeyi? Hamma tambayata kakeyi?"
Yana kallon yanda kowa a gida yake fadin ba'a batawa Bilal rai, jinsu kawai yake, ko suce Bilal na da hakuri, Bilal baya fada, Bilal baya fushi, suna magana kamar a duniya babu wanda yake da halaye nagartattu kamar Bilal, bayan rana bata fitowa ta fadi baiga kalar rashin hakurin Bilal ba, baya saukewa akan kowane sai shi, yanzun ma ga bacin rai nan bayyane a fuskar shi
"Ka daina girmamani kana kirana Hamma, kana kuma hadawa da ihu a karshen zancen ka"
Karasawa Bilal yayi inda Rayyan din yake yasa hannu ya dauki kwalin sigarin da ya ajiye da lighter din, hannu Rayyan ya dago, kallon da Bilal yayi mishi yana saka shi mayar da hannun
"Woo... Allah ya baka hakuri"
Rayyan ya fadi yana dariya ganin yanda ran Bilal din ya baci da gaske, shikuma a cikin abinda ya faru duka baiga wani abu na bacin rai ba, sigari ce ya fara sha baisan dalili ba, yanzun kuma bashi da wani dalilin dainawa. Shi baice Abbu yaji haushi dan ya sha sigari ba, baice Bilal ya dauki laifin da ba na shi ba, yana kallon shi tun tasowar su yana hakan, so yake yanda bai taba tambayar shi dalili ba, shima ya daina tambayar shi dalili akan abubuwa irin haka. Yana kallo Bilal ya fice daga dakin, mikewa yayi yana shiga wanka abin shi, idan Bilal ya gama fushin ya huce zai neme shi ya sani.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:06 PM - 111: Nov 14, 2020
07
Bai fara dana sanin neman gurbin karatu a jami'ar Ahmadu Bello da take garin Zaria ba sai da ya samu. Bai san sa'a bace ko kuma matakan su daya tsallake ko kuma sanayya ta manyan mutane da Abbu yayi ta saka shi samun abinda ya nema. Kawai dai yasan ya fara dana sani ne daga jiya da Haris ya dawo har dakin su ya shigo da sallamar shi yana zaune, maganar shi ta farko bayan sun gaisa ita ce
"Abbu yake fadamun ka samu gurbin karatu a makarantar mu, shine ko ka kira ka sanar dani. Naji dadi wallahi, saboda duk bangaren lafiya dai ne"
Tsayawa yayi yana kallon Haris da yake magana kamar ya fada mishi ya zabi karantar fannin daya danganci kwakwalwa da sanin halayyar dan Adam wato Psychology saboda ya kasance waje daya da shi. Ya zabi fannin ne saboda yana son fahimtar wasu daga cikin halayen shi, wasu cikin tarin tambayoyin da yake tunanin bangaren zai amsa mishi akan kan shi, badan wani dalili ba. Kuma ko ba komai kaunar da yake ma uniform zai kasance yana saka farar rigar nan lokaci zuwa lokaci. Saka uniform ne abu daya da yayi kewa bayan gama sakandire din shi. Haka kawai sai yaga duk kayan da zai saka ba zasu kai yanda yake saka uniform yin kyau ba.
Wani lokaci can baya kaunar da yake ma uniform ta saka shi tunanin aikin soja, sai dai har kasan zuciyar shi yaji haka kawai ba zai iya nisa da gida ba, kuma bayason takurar da take tattare da aikin, yana da taurin kan da yake da tabbacin zai wahala a aikin. Zuciyar shi ba tada sanyin da zata lankwasu yayi biyayyar da yaji ana labarin yiwa manya. Shisa bai kara barin tunanin ya dame shi ba, kafin ya yanke hukuncin zabar fannin da ya zaba yanzun, yayi tunani kala-kala, ayyuka barkatai sun zo ran shi. Sai dai zuciyar shi tafi rinjaye akan Psychology din ne.
Haris din kuma yana bangaren lafiyar yara ne wato Pediatric. Ba shiga harkar kowa yake ba a gidan banda Bilal, anso hada su daki daya. Tashin hankalin da ya dinga yine yasa su Abbu suka bar su shida Bilal a daki daya. Lokacin da yaji labarin bangaren da Haris ya samu gurbin karatu da Bilal kawai yayi zancen
"Hamma zaiyi kyau da likitan yara...ko a gidan nan ka kalli yanda su Intisar ke son shi. Ko masallaci muka fito ba zaka rasa ganin shi rike da wani yaron ba"
Murmushi Bilal yayi
"Duk yaushe ka kula da Haris haka?"
Harar Bilal yayi
"Dan bana shiga harkar kowa baya nufin bana kula da abinda yake faruwa"
Jinjina kai Bilal yayi
"Naga alama ai, ko Ayya zancen da tayi mun kenan. Sanyin halin shi ne yasa yara suke manne da shi, ga kyauta kuma, ba zaka raba aljihun shi da dan biskit ko alawa ba"
Rayyan kwanciya ya gyara yana yin shiru, surutun Bilal ya cigaba da yi har saida ya kule
"Wai bacci kayi ko wulakanci ne yasa kayi banza ka kyaleni ina ta zuba ni kadai?"
Ba baccin da yakeyi, ya lumshe idanuwan shine, yana jin shi, a duka zancen shi babu wanda zai bada amsa, a wajen shi hirar ta rigada ta kare, ya fadi abinda yake son fada. Duk da yaso hirar tayi tsayi sai Bilal din ya kunna shi da maganar da yayi kan yaushe yake kula da halayen Haris. Yana so ya mayar da shi kamar baisan abinda yakeyi ba. Shisa sam mutanen da yake ji a ran shi basu da wani yawa, saboda halayen su na saurin cakar da shi.
Jiyan ma kallon Haris ya dinga yi, har ya gama surutun da zaiyi. Ganin ba amsa shi zai ba yasa ya tashi ya fita daga dakin. Yanayin fuskar shi ma ya bala'in bata ma Rayyan din rai, saboda haka kawai ba gayyato shi yayi ba, baice ya shigo daki ya same shi ba. Da suka gaisa bai sashi zama ya fara mishi hirar rashin dalili ba, yazo yasa yanajin kamar yayi mishi laifi. A fuska ya nuna baiji dadin shirun da yayi ba.
"Tsalle kake so inyi mu rungume juna saboda zamu kasance a makaranta daya ko me?"
Rayyan din ya furta cikin sigar mita yana karasa maganar da jan tsaki. Yana da dalilai da yawa da yasa baya shiga harkar kowa. To yau ma yana haduwa da Haris din yake tambayar yaushe yake da niyyar zuwa ya fara hada-hadar registration
"Ko zamu tafi tare gobe ne?"
Kai ya girgiza mishi, da alamar kosawa a muryar shi yace
"Zan taho da kaina Hamma..."
Dan jim Haris din yayi, yana son duka yan uwan shi, ba su kadai ba, shi mutum ne na mutane. Wasu lokuttan Rayyan na saka shi son tambayar shi ko ya taba mishi wani abune da bai sani ba shisa yake karayin kicin-kicin da fuskar shi duk idan sun hadu. Shi bayaso ya bata ran kowa sam-sam, ko wani yagani cikin bacin rai yakan yi kokarin ganin yaja shi da raha har saiya murmusa. Tun tasowar su abu kadan Rayyan bai taba duba cewa ya bashi shekaru kusan ukku ba, haka zai kama shi da jibga kamar ganga. Da suka fara hankali kuma baya magana da shi, in zasuyi haduwa goma idan bai mishi magana ba zai rabe gefe kamar bayason wani abu ya hadasu.
Ranakun duk da Rayyan ya fara mishi magana to na farko ba zai manta ba, rashin lafiya yayi harya kwanta asibiti, da sukaje duba shi yayi mishi ya jiki, amman yana iya yin jinya. Rayyan din ya shiga dakinsu da sunan duba shi, bayan sallama zai iya mintina goma a tsaye ya jingina bayan shi da bangon dakin, har sai in shi ya gaji da jin shirun yai yawa yace
"Rayyan..."