Sashe 48
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rayyan ya iya cewa yana sauke wayar daga kunnen shi, fita yayi daga tashar zuwa bakin titi. Anan yayi tsaye, masu mashin da napep na ta mishi magana, harya kawo iya wuya, ga shi gari yayi duhu tunda sai bayan Magriba suka sauka.
"Alhaji tafiya ne?"
Wani mai mashin ya fadi a karo na biyu, kamar bai ga ya girgizawa mutane wajen hudu kai cikin alamar a'a ba.
"Sai ka daukeni ka dorani, me yasa dole sai kun sa mutane magana ne?"
Jinjina kai mai mashin din yayi
"Allah ya baka hakuri, daga tambaya"
Wani irin kallo Rayyan ya watsa mishi, dai-dai lokacin da wata mota baqa, kirar Honda Accord DC V6 ta tsaya a gaban shi. Gilashin aka sauke daga bangaren da yake, kafin aka kunna fitilar cikin motar haske na gaurayewa
"Rayyan?"
Bappa ya fadi daga cikin motar, Rayyan din na jinjina mishi kai
"Muje..."
Cewar Bappa, hannu Rayyan yasa yana bude murfin motar ya shiga, batare da yace komai ba ya rufe. Bappa ma baice mishi komai ba yaja motar, hankalin shi sam ba'a kan titi yake ba, shi dai yana garin Bauchi, zaune a cikin motar Bappa da sai kamshi takeyi. Amman hankali da natsuwar shi suna garin Zaria. Baisan anyi parking ba sai da Bappa yace mishi
"Mun zo"
Budewa yayi yana fita, in da duk Bappa ya sa kafar shi nan Rayyan yake mayarwa, ko sunan Hotel din bai duba ba, daga yanayin shi bayan sun shiga ya dan gane ko ina ne, ciki suke shiga sosai har suka karasa daki mai lamba 19, inda Bappa ya zaro mukulli daga aljihun shi yana bude dakin. Da sallama ya shiga, Rayyan na biye da shi, ya mayar da dakin ya rufe, akwai haske gauraye da dakin, babba ne da tanqamemen gado sai tv da take ta aiki, amman babu magana, anyi kasa da ita. Har da kujera doguwa a cikin dakin. Yayi kyau sosai da sosai. Ko ina a gyare tsaf, da alama zaiyi tsada
"Na san ka kwaso gajiya, ga sallah kuma da wahala kun tsaya..."
Bappa ya fadi yana saka Rayyan kallon shi, dogone dan da wahala idan bai mafi Rayyan din tsayi ba, sai dai shi siririne, da kasumba a fuskar shi, akwai abin sallah a goshin shi, wata natsuwa Rayyan yake gani a tattare da Bappa, duk da kananun kayane a jikin shi yayiwa Rayyan din kwarjini. Mutanen da suke mishi kwarjini basu da yawa, duk izzar da kake tare da ita kuwa. Da hannu Bappa ya nuna mishi bandaki
"Ga toilet din nan"
Jakar da take rataye a kafadar shi Rayyan ya sauke akan kujera, bandakin ya karasa yana zira takalman da suke ajiye a bakin kofa ya shiga sosai yana rufewa. Har ruwa ya watsa, sannan ya daura alwala. Sanda ya fito sai yake jin shi ya samu yar natsuwa. Sai kan shi da yake ciwo kamar ganga ake bugawa a ciki. Baiga Bappa ba a dakin ya dai shimfida mishi darduma, sun tsaya sukayi azahar inda akaci abinci, shi banda nutri-milk da biscuit babu abinda ya sakawa cikin shi, shima dan yana bukatar wani dan karfi ko ya yake kafin zullumi ya saka shi faduwa.
Sallolin shi yayi a nutse yana zaro wayar shi ya duba, ganin lokacin isha'i yayi ya saka shi gabatar da ita. Zaune yake akan kafet din yau ya rasa kalar addu'ar daya kamata yayi bayan rokon Allah da yasa daga Bilal har Layla lafiyar su kalau. Lambar Layla ya sake kira
"Dan Allah ki daga"
Ya fadi a hankali, amman bata daga din ba, haka Bilal. Rasa abinda yake mishi dadi yayi a duniya, saboda zuwa yanzun ya aminta da zuciyar shi, tabbas wani abu ya faru, babu yanda za'ayi yayi tafiya haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba. Lakca zai tafi yayi yamma, in har bai fada mishi zaiyi yamma ba ya dinga kira kenan har sai ya mishi text cewar yana aji
"Wai ni karamin yaro ne Bilal?"
Ya taba tambayar shi wani lokaci da yayi mishi kira goma akan shidda tayi ina ya tsaya bai koma gida ba
"Ni dai ka dinga fadamun in ka san zaka biya wani waje"
Bilal din ya amsa cike da damuwa a muryar shi, amman yau ya tafi wani waje mai nisa haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba, da gaske ba lafiya ba, wani abu ya faru, ko da shi ko Layla. Saboda tunanin Rayyan din sam bai kai gida ba, kallon wayar shi yake kamar yana so ta taimaka mishi da wata maslaha. Amman shiru
"Ayya..."
Zuciyar shi ta ambata, a karo na farko a tsayin rayuwar shi da yaji yana son ya kirata da kan shi, yana kuma bukatar taimakonta, watakila ita tayi magana da Bilal a tsayin ranar. Ko Bilal baiyi magana da kowa ba, tabbas zaiyi da Ayya, lambarta ya lalubo ya kira, zuciyar shi banda dokawa babu abinda takeyi mishi, tana dagawa bai jira ta gama sallamar ba yace
"Ayya kinyi magana da Bilal?"
Dan jim da tayi ya sa Rayyan din kiran
"Ayya"
Yana jin numfashin da ta sauke
"Rayyan?"
Ta kira sunan shi kamar tana shakkun cewa da gaske ya kirata, da gaske tana magana da shi
"Kunyi magana? Bilal..."
Ya sake maimaitawa
"Ina ta kira bai dauka ba, tun da safe da yace mun ya kaika ta sha, yace yana da lakca da safen da, amman ba za'ayi ba zaije gida ya kwanta yayi bacci, har yanzun bai kirani ba, na kira shi yafi sau hamsin bai daga ba. Na kasa samun natsuwa"
Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi yanajin kamar bangwayen dakin na hadewa da shi a ciki saboda wani irin tsoro daya taso mishi
"Kai ma bai neme ka ba?"
Ayya ta tambaya da wani irin yanayi a muryarta, kai Rayyan yake girgiza mata, tashin hankali bakon abune a wajen shi, ya san kunci, ya san rashin natsuwa, yasan bacin rai, har tsoro ya sani saboda yana jin shi idan ya ga mage, yana kuma jin shi duk idan ya sauke idanuwan shi akan Layla, ya san abubuwa da dama, tashin hankali bakon shine, musamman mai hade da firgici irin wannan. Kafin wasu dakika ya fara kokawa da numfashin shi
"Rayyan!"
Yaji muryar Ayya kamar a wata duniya kafin wani haske ya gilma ta cikin idanuwan shi yana saka shi runtsa su ya sake budewa, ji yake kamar an kama kafafuwan shi an sadda kan shi kasa ana jijjiga shi, idan wani abu ya sami Layla, baisan ya zaiyi ba, amman bai kara sanin asalin firgici ba sai da yai tunanin wani abu ya sami Bilal
"Gabana sai faduwa yake tun safe"
Ya tuna maganar Bilal jiya da daddare
"Kayi addu'a"
Ya amsa shi, yana kallon yanda ya danyi jim kamar mai nazarin wani abu sai kuma yaci gaba da danna wayar da yakeyi, sai yau din yaga kamar akwai rama a cikin idanuwan Bilal din da baigani ba sai yanzun yake tunawa
"Ka kwantar da hankalin ka, watakila ko ya ajiye wayar wani waje bai ganta ba, ka san Bilal"
Wani irin numfashi Rayyan ya sauke
"Ni da ke mun san Bilal baya ajiye abu ya rasa in da ya ajiye Ayya"
Cewar Rayyan yana sauke wayar daga kunnen shi ya kashe kiran, a gefe ya ajiyeta yana dafe kan shi da hannuwa biyu, tabbas da ace zai sami motar da zata juya Zaria ba zai kwana a garin nan ba yau, bashi da wata natsuwa idan bai sami Bilal ba. Bappa ne ya shigo da leda a hannun shi yanayin sallamar da Rayyan ya amsa ya dora da
"Zan iya samun motar da zata koma Zaria yau?"
Da mamaki Bappa ya kalle shi
"Da daren nan? Amman ka san hanyar ba aminci gareta ba ko? Kuma me yasa kake tambayar motar Zaria"
Cike da damuwa Rayyan yace
"Zan koma ne"
Sai da Bappa ya karasa ya ajiye ledar hannun shi ya zauna sannan ya fuskanci Rayyan sosai
"Lafiya dai ko?"
Bai san me yasa yaji kamar zai iya yadda da Bappa ba, bayan shi din baya yarda da mutane. Amman yana cikin damuwa kalar da bai taba sani ba, taimako yake bukata ko daga wajen waye
"Ina ta kiran kanina baya dagawa"
Kai Bappa ya jinjina
"Watakila baya kusa da wayar, ko kuma ya yarda ba'a kai da tsinta an kashe ba. Ko wani ya dauke, akwai dalilai irin haka"
Kai Rayyan ya girgiza mishi, yau kalamai yake nema da zai misalta abinda yakeji Bappa ya fahimta
"Banda kanina, Bilal ba haka yake ba. Zai kirani ko da wayar wani ne ya fadamun. Yaune na farko da muka yini bamuyi magana da juna ba"
Numfashi Bappa ya sauke
"In shaa Allah komai lafiya. Ka kwantar da hankalin ka, ba kada lambar ko abokin shi haka? Sai ka kira a duba shi?"
Kai Rayyan ya girgiza, a karo na farko yana dana sanin halayen shi, da ace ko lambar mutum daya a cikin gidan nasu yana da ita yau zatayi mishi rana
"Mutum yana da ranar shi Hamma, duk yanda kake tunanin baka bukatar wani bayan ni da Layla ba fata nai maka ba, Allah kar ya nuna maka ranar da zata karyata tunanin ka..."
Ga ranar ta zo yau, ranar da Bilal yayi mishi addu'a karya gani
"Allah bai amshi addu'ar ka ba Bilal"
Rayyan ya fadi a zuciyar shi
"In shaa Allah komai lafiya. Na san zai kira"
Numfashi kawai Rayyan yaja yana mikewa dakyar, kamar abinda ake kira "anxiety attack" ne yake shirin kamashi saboda tashin hankalin da yake ciki. Inda jakar shi take ya karasa ya dauka yana budewa, jikin shi babu inda baya bari sanda ya dauko kwalin sigarin shi, ya dauki kara daya ya saka a baki ya lalubo lighter din saiya tsinci kan shi da juyawa, yau abubuwan da suke baqi a wajen shi yake tayi
"In ba zaka damu ba"
"Alhaji tafiya ne?"
Wani mai mashin ya fadi a karo na biyu, kamar bai ga ya girgizawa mutane wajen hudu kai cikin alamar a'a ba.
"Sai ka daukeni ka dorani, me yasa dole sai kun sa mutane magana ne?"
Jinjina kai mai mashin din yayi
"Allah ya baka hakuri, daga tambaya"
Wani irin kallo Rayyan ya watsa mishi, dai-dai lokacin da wata mota baqa, kirar Honda Accord DC V6 ta tsaya a gaban shi. Gilashin aka sauke daga bangaren da yake, kafin aka kunna fitilar cikin motar haske na gaurayewa
"Rayyan?"
Bappa ya fadi daga cikin motar, Rayyan din na jinjina mishi kai
"Muje..."
Cewar Bappa, hannu Rayyan yasa yana bude murfin motar ya shiga, batare da yace komai ba ya rufe. Bappa ma baice mishi komai ba yaja motar, hankalin shi sam ba'a kan titi yake ba, shi dai yana garin Bauchi, zaune a cikin motar Bappa da sai kamshi takeyi. Amman hankali da natsuwar shi suna garin Zaria. Baisan anyi parking ba sai da Bappa yace mishi
"Mun zo"
Budewa yayi yana fita, in da duk Bappa ya sa kafar shi nan Rayyan yake mayarwa, ko sunan Hotel din bai duba ba, daga yanayin shi bayan sun shiga ya dan gane ko ina ne, ciki suke shiga sosai har suka karasa daki mai lamba 19, inda Bappa ya zaro mukulli daga aljihun shi yana bude dakin. Da sallama ya shiga, Rayyan na biye da shi, ya mayar da dakin ya rufe, akwai haske gauraye da dakin, babba ne da tanqamemen gado sai tv da take ta aiki, amman babu magana, anyi kasa da ita. Har da kujera doguwa a cikin dakin. Yayi kyau sosai da sosai. Ko ina a gyare tsaf, da alama zaiyi tsada
"Na san ka kwaso gajiya, ga sallah kuma da wahala kun tsaya..."
Bappa ya fadi yana saka Rayyan kallon shi, dogone dan da wahala idan bai mafi Rayyan din tsayi ba, sai dai shi siririne, da kasumba a fuskar shi, akwai abin sallah a goshin shi, wata natsuwa Rayyan yake gani a tattare da Bappa, duk da kananun kayane a jikin shi yayiwa Rayyan din kwarjini. Mutanen da suke mishi kwarjini basu da yawa, duk izzar da kake tare da ita kuwa. Da hannu Bappa ya nuna mishi bandaki
"Ga toilet din nan"
Jakar da take rataye a kafadar shi Rayyan ya sauke akan kujera, bandakin ya karasa yana zira takalman da suke ajiye a bakin kofa ya shiga sosai yana rufewa. Har ruwa ya watsa, sannan ya daura alwala. Sanda ya fito sai yake jin shi ya samu yar natsuwa. Sai kan shi da yake ciwo kamar ganga ake bugawa a ciki. Baiga Bappa ba a dakin ya dai shimfida mishi darduma, sun tsaya sukayi azahar inda akaci abinci, shi banda nutri-milk da biscuit babu abinda ya sakawa cikin shi, shima dan yana bukatar wani dan karfi ko ya yake kafin zullumi ya saka shi faduwa.
Sallolin shi yayi a nutse yana zaro wayar shi ya duba, ganin lokacin isha'i yayi ya saka shi gabatar da ita. Zaune yake akan kafet din yau ya rasa kalar addu'ar daya kamata yayi bayan rokon Allah da yasa daga Bilal har Layla lafiyar su kalau. Lambar Layla ya sake kira
"Dan Allah ki daga"
Ya fadi a hankali, amman bata daga din ba, haka Bilal. Rasa abinda yake mishi dadi yayi a duniya, saboda zuwa yanzun ya aminta da zuciyar shi, tabbas wani abu ya faru, babu yanda za'ayi yayi tafiya haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba. Lakca zai tafi yayi yamma, in har bai fada mishi zaiyi yamma ba ya dinga kira kenan har sai ya mishi text cewar yana aji
"Wai ni karamin yaro ne Bilal?"
Ya taba tambayar shi wani lokaci da yayi mishi kira goma akan shidda tayi ina ya tsaya bai koma gida ba
"Ni dai ka dinga fadamun in ka san zaka biya wani waje"
Bilal din ya amsa cike da damuwa a muryar shi, amman yau ya tafi wani waje mai nisa haka ace ko sau daya Bilal bai neme shi ba, da gaske ba lafiya ba, wani abu ya faru, ko da shi ko Layla. Saboda tunanin Rayyan din sam bai kai gida ba, kallon wayar shi yake kamar yana so ta taimaka mishi da wata maslaha. Amman shiru
"Ayya..."
Zuciyar shi ta ambata, a karo na farko a tsayin rayuwar shi da yaji yana son ya kirata da kan shi, yana kuma bukatar taimakonta, watakila ita tayi magana da Bilal a tsayin ranar. Ko Bilal baiyi magana da kowa ba, tabbas zaiyi da Ayya, lambarta ya lalubo ya kira, zuciyar shi banda dokawa babu abinda takeyi mishi, tana dagawa bai jira ta gama sallamar ba yace
"Ayya kinyi magana da Bilal?"
Dan jim da tayi ya sa Rayyan din kiran
"Ayya"
Yana jin numfashin da ta sauke
"Rayyan?"
Ta kira sunan shi kamar tana shakkun cewa da gaske ya kirata, da gaske tana magana da shi
"Kunyi magana? Bilal..."
Ya sake maimaitawa
"Ina ta kira bai dauka ba, tun da safe da yace mun ya kaika ta sha, yace yana da lakca da safen da, amman ba za'ayi ba zaije gida ya kwanta yayi bacci, har yanzun bai kirani ba, na kira shi yafi sau hamsin bai daga ba. Na kasa samun natsuwa"
Runtsa idanuwan shi Rayyan yayi yanajin kamar bangwayen dakin na hadewa da shi a ciki saboda wani irin tsoro daya taso mishi
"Kai ma bai neme ka ba?"
Ayya ta tambaya da wani irin yanayi a muryarta, kai Rayyan yake girgiza mata, tashin hankali bakon abune a wajen shi, ya san kunci, ya san rashin natsuwa, yasan bacin rai, har tsoro ya sani saboda yana jin shi idan ya ga mage, yana kuma jin shi duk idan ya sauke idanuwan shi akan Layla, ya san abubuwa da dama, tashin hankali bakon shine, musamman mai hade da firgici irin wannan. Kafin wasu dakika ya fara kokawa da numfashin shi
"Rayyan!"
Yaji muryar Ayya kamar a wata duniya kafin wani haske ya gilma ta cikin idanuwan shi yana saka shi runtsa su ya sake budewa, ji yake kamar an kama kafafuwan shi an sadda kan shi kasa ana jijjiga shi, idan wani abu ya sami Layla, baisan ya zaiyi ba, amman bai kara sanin asalin firgici ba sai da yai tunanin wani abu ya sami Bilal
"Gabana sai faduwa yake tun safe"
Ya tuna maganar Bilal jiya da daddare
"Kayi addu'a"
Ya amsa shi, yana kallon yanda ya danyi jim kamar mai nazarin wani abu sai kuma yaci gaba da danna wayar da yakeyi, sai yau din yaga kamar akwai rama a cikin idanuwan Bilal din da baigani ba sai yanzun yake tunawa
"Ka kwantar da hankalin ka, watakila ko ya ajiye wayar wani waje bai ganta ba, ka san Bilal"
Wani irin numfashi Rayyan ya sauke
"Ni da ke mun san Bilal baya ajiye abu ya rasa in da ya ajiye Ayya"
Cewar Rayyan yana sauke wayar daga kunnen shi ya kashe kiran, a gefe ya ajiyeta yana dafe kan shi da hannuwa biyu, tabbas da ace zai sami motar da zata juya Zaria ba zai kwana a garin nan ba yau, bashi da wata natsuwa idan bai sami Bilal ba. Bappa ne ya shigo da leda a hannun shi yanayin sallamar da Rayyan ya amsa ya dora da
"Zan iya samun motar da zata koma Zaria yau?"
Da mamaki Bappa ya kalle shi
"Da daren nan? Amman ka san hanyar ba aminci gareta ba ko? Kuma me yasa kake tambayar motar Zaria"
Cike da damuwa Rayyan yace
"Zan koma ne"
Sai da Bappa ya karasa ya ajiye ledar hannun shi ya zauna sannan ya fuskanci Rayyan sosai
"Lafiya dai ko?"
Bai san me yasa yaji kamar zai iya yadda da Bappa ba, bayan shi din baya yarda da mutane. Amman yana cikin damuwa kalar da bai taba sani ba, taimako yake bukata ko daga wajen waye
"Ina ta kiran kanina baya dagawa"
Kai Bappa ya jinjina
"Watakila baya kusa da wayar, ko kuma ya yarda ba'a kai da tsinta an kashe ba. Ko wani ya dauke, akwai dalilai irin haka"
Kai Rayyan ya girgiza mishi, yau kalamai yake nema da zai misalta abinda yakeji Bappa ya fahimta
"Banda kanina, Bilal ba haka yake ba. Zai kirani ko da wayar wani ne ya fadamun. Yaune na farko da muka yini bamuyi magana da juna ba"
Numfashi Bappa ya sauke
"In shaa Allah komai lafiya. Ka kwantar da hankalin ka, ba kada lambar ko abokin shi haka? Sai ka kira a duba shi?"
Kai Rayyan ya girgiza, a karo na farko yana dana sanin halayen shi, da ace ko lambar mutum daya a cikin gidan nasu yana da ita yau zatayi mishi rana
"Mutum yana da ranar shi Hamma, duk yanda kake tunanin baka bukatar wani bayan ni da Layla ba fata nai maka ba, Allah kar ya nuna maka ranar da zata karyata tunanin ka..."
Ga ranar ta zo yau, ranar da Bilal yayi mishi addu'a karya gani
"Allah bai amshi addu'ar ka ba Bilal"
Rayyan ya fadi a zuciyar shi
"In shaa Allah komai lafiya. Na san zai kira"
Numfashi kawai Rayyan yaja yana mikewa dakyar, kamar abinda ake kira "anxiety attack" ne yake shirin kamashi saboda tashin hankalin da yake ciki. Inda jakar shi take ya karasa ya dauka yana budewa, jikin shi babu inda baya bari sanda ya dauko kwalin sigarin shi, ya dauki kara daya ya saka a baki ya lalubo lighter din saiya tsinci kan shi da juyawa, yau abubuwan da suke baqi a wajen shi yake tayi
"In ba zaka damu ba"