Sashe 31
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka sukayi sallama da Mamin, bacci take ji idanuwanta har wani yaji-yaji yakeyi. Shisa sanda Bilal yazo daukar kayanta bata samu ta gaishe dashi ba sai yanzun. Abbu ya gaya mata ya basu mota, kuma tasan motar, tana zuwa ta bude bayan motar ta shiga. Ko kadan batayi tunanin Rayyan yana ciki ba harta ja murfin ta zauna. Numfashi ta sauke, Rayyan kuma idanuwan shi a lumshe suke, dan yasan yau zai samu yayi baccin safe tunda motar gida ce bata haya ba. Kawai yaji ana shigowa, hakan yasaka shi bude idanuwan shi, gyara kwanciya yayi yana juya kan shi ya kafa ma Layla ido.
Itama zama ta gyara tana dan juyawa taga an mata quri
"Wayyoo Allah..."
Ta furta da karfi saboda gabanta ya fadi sosai
"Hamma"
Ta furta har lokacin da tsoro a muryarta
"Baki da hankali? Da safe zaki zo kina mun ihu a kunne?"
Ita bata neman tashin hankali, tasan ko tafiya zasuyi zai zauna a gaban mota ne. Shisa ma ta bude bayan motar ta shiga abinta. Baccine a idanuwanta har sun mata nauyi
"Kayi hakuri, dan girman Allah Hamma, wallahi bansan kana nan ba sam sam, ina kwana"
Ta karashe a gajiye, hararta yayi yana jan wani tsaki dai-dai lokacin da Bilal ya shigo motar ya zauna. Juyawa yayi yana kallon su hadi da sauke numfashi
"Me kuke nufi?"
Ya bukata, tunda shi yasan su duka Abbu ya baiwa mota, baice ya zama direban su ba balle su kame a bayan mota gabaki daya
"Wani ya dawo gaba"
Ya fadi yana kallon Rayyan daya kauda kai
"Magana fa nakeyi"
Cikin ido Rayyan ya kalle shi
"Kana shamun kamshi tun da safe"
Ya fadi kamar wani dan karamin yaron da kaiwa dukan tsiya kazo kuma kana yiwa dariya. Layla Bilal ya kalla, ita kuma ta kalli Rayyan din kamar tana neman izinin shine kafin ta koma, shikuma ya rigada ya lumshe idanuwan shi. Numfashi Bilal ya sauke yana runtsa idanuwan shi ya bude su a lokaci daya. Tuqi zaiyi, yana bukatar gabaki daya natsuwar shi, idan ya biye musu zasu birkita mishi lissafi, hakan yasa shi gyara zama, addu'a yayi yana jan motar suka fice daga gidan, sun kama hanyar da zata fitar dasu daga Kano kenan Rayyan ya bude idanuwan shi yana ganin Layla a zaune a kusa da shi
"Mayya ce ke? Dole sai inda nake zaki zauna?"
Wani abu taji ya tokare mata zuciya yanayin yanda Rayyan din yayi magana. Inda ta tashi ta koma gaba ya bude ido kamar yanda yayi tana da tabbas zaice wani abu, dole saiya nemi dalilin da zai sata dana sanin tafiyar nan, bayan tun da satin ya kama take tunanin yanda zata zauna mota daya da shi, nishadin duk da takeyi ya dishe mata shi
"Hamma ka tsaya in dawo gaba"
Layla ta fadi da wani yanayi a muryarta, ta mudubin gaban motar Bilal ya kalle su
"Na dora wayata a kujerar, kuyi zaman ku"
Kafin ta karayin magana ya kunna radio din motar yana kure maganar
"Ka fasa mana kunne Bilal!"
Rayyan ya fadi a masife, ko kallon su Bilal baiyi ba, balle kuma suyi tunanin zai saurare su, ba yanda za'ayi su rabashi da nutsuwar shi yana tuqi. Matsawa Layla tayi tana kara bada tazara tsakaninta da Rayyan din, jingina kanta tayi da jikin motar tana rufe idanuwan ta, duk yanda take jin ranta na mata susa bai hana bacci dauketa ba, Rayyan kallonta yakeyi duk da yasan bacci ya kamata yayi. Yanajin inama ace haka zata zauna, yanda zuciyar shi tayi wani luf a kirjin shi abin ya mishi dadi, amman yasan tashi zatayi, bude idanuwanta zatayi ta hargitsa mishi komai kamar yanda ta saba. Baisan me yasa zata zo da idanuwan mage ba.
Idanuwan shi na kafe a kanta, tana ta baccin ta, a cikin baccin ta juyo kwanciya, ganin da yayi kamar wuyanta zaiyi ciwo yasa shi girgiza kai kawai, babu wani abu da zatayi dai-dai, baccin ma ba zatayi shi dai-dai ba. Yana wannan mitar a zuciyar shi ya mika hannu ta baya dan ya dauko ruwan da Bilal ya ajiye, sai jin kan Layla yayi saman hannun shi, kamar ya mika ne dan ta kwanto, da dayan hannun shi ya tallabe wannan, yana zare shi a hankali, ruwan ya dauka sai ya dan janyo jikin shi yana gyara zama yanda kanta zai kwanta a kafadar shi da kyau.
Robar ruwan ya bude yana sha sosai, ya mayar ya kulle, yanajin Layla ta kara gyara kwanciyar ta a jikin shi, tana kwantowa sosai. Wani irin dokawa zuciyar shi takeyi kamar zata fito daga kirjin shi
"Mayya..."
Ya furta a hankali yana sauke numfashi, sosai ya jingina kan shi da motar yana lumshe idanuwan shi, bugun zuciyar shi yake saurare da yake ji har cikin kunnuwan shi, kafin wata natsuwa daya kwana biyu baiji ba ta saukar mishi, bacci mai sanyi na dauke shi, baisan sanda ya jingina nashi kan dana Layla da yake kafadar shi ba. Kawai abinda ya sani wannan karin baccin nashi babu mugayen mafarkai ko daya. Ta gaban mudubi Bilal ya hango su, yanajin kamar an soka mishi wani abu a kirjin shi, sosai zuciyar shi ke dokawa kamar mai shirin samun matsalar bugun zuciya.
Shi yake bukatar kulawa
Shi yake cikin matsala
Shi yake bukatar Abbu da Mami su fadawa Rayyan daya kula da shi
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 26, 2020
12
Kan shi ciwo yake kamar zai rabe gida biyu. Dan bai iya takawa gida ba, sai da ya hau mashin. Da yake ba surutu yake son yi ba, canjin dari da ya baiwa mai mashin dinma da hannu yayi mishi alama daya tafi
"Allah yasa kar in ga kowa, Allah yasa kar kowa ya ganni"
Rayyan ya furta a cikin kan shi. Bayason mutane, baya kuma son 'yan cikin gidan da suke haya fiye da sauran mutane, saboda suna saka shi yanayin magana a lokuttan da ko kadan bayason yi. Gashi yanzun Bilal yace ya dinga yiwa mutane murmushi idan sun mishi magana, baisan ya zai fara ba, motsa labban shi kawai yakeyi wasu lokuttan, tunda bayajin yin fara'a sam-sam. Ya gaisa dasu, baisan kirkin me Bilal yake so ya dinga musu ba
"Ko rashin lafiya ta kamaka ba fata nake ba, su dinne mutanen farko da zasu taimaka maka tunda kuna gida, kasan abubuwan nan, kasan hakkin makota Hamma"
Bilal din ya fada mishi
"Bana son su"
Shine amsar daya baiwa Bilal din
"Su ma na tabbata ba son ka sukeyi ba. Ka dinga murmushi dan Allah in zaka gaisa da mutane, ka dan saki fuska ba kamar an maka dole ba"
Bilal saiya dinga mishi magana kamar baisan dolen akayi mishi yake gaisawa da su ba. Hakkin musulunci kawai yake saukewa. Kamar barawo haka yake sanda wajen shiga gidan, sam baya so wani ya gan shi. Kusan da gudu ya karasa dakin su yana daga labulen ya shiga da sauri
"Subhanallah..."
Bilal da yake zaune ya bude kular abinci ya fadi, dan sosai Rayyan din ya bashi tsoro
"Assalamu alaikum..."
Cewar Rayyan, amsawa Bilal din yayi yana girgiza kai kawai. Taliya ce da miya sai soyayyen dankalin turawa, rabon su da dora tukunya a wuta harya manta, sai dai ko in sunyi marmarin shan shayi zasu dafa, amman Aysha na musu kokari matuka ta fannin abinci tunda tazo makarantar. Bilal baiyi mishi tayin abinci ba, tunda yasan sai yayi wanka, aikam ficewa daga dakin Rayyan yayi. Sai bayan yayo wankan ya dawo ya sake kayane ya zauna yana mayar da numfashi Bilal yace
"Abinci fa?"
Kai Rayyan din ya girgiza mishi
"Babu abinda kaci fa duk yau"
Tunda tare suka fita, kuma yasan babu abinda Rayyan din zaici a waje banda biskit, idan ya samu kalar wanda yakeci din kenan.
"Zanci sai anjima"
Rayyan ya furta yana kwanciya kan katifar da yake zaune a gefe, sai yaji wani dadi a ran shi daya kwanta din, kamar gajiyar daya kwaso ta dan sake shi. Wayar shi da Bilal ya janyone yaga yau din Alhamis, numfashi ya sauke
"Azumi kakeyi ko?"
Ya tambaya
"Me yasa baka gajiya da surutu? Dan Allah ka kyaleni ni"
Rayyan yayi maganar cikin alamar gajiya. Murmushi kawai Bilal din yayi. Bai taba gane azumin alhamis da litinin baya wuce Rayyan ba sai wannan dawowar da sukayi. Sai yake tuna ranakun da Rayyan din zai wuni baici komai ba, duk surutun da zai mishi. Sai sun dawo sallar Magriba tukunna, ko in yayo alwala ya shigo daki an kira, Bilal zai ga ya sha ruwa, ko yaci dabino. To bai taba kawo komai a ran shi ba, tunda Rayyan na da shan ruwa, kuma dabino kamar biskit ne a wajen shi, da wahala ka raba jakar shi da su, ko cikin kayan shi ka duba zaka samu.
Zurfin ciki irin na Rayyan baya gajiya da bashi mamaki, shima ranar alhamis din daya san azumi Rayyan yakeyi, alhamis din kuma daya tabbatar da abinda ya dade da sani, wajen Rayyan din yaje daga nasu bangaren, ya same shi a can karkashin wata bishiya, inda yake shimfida darduma ya zauna idan basu da darasi ba kuma yason komawa gida. Tunda wani lokaci ko baiyi niyya ba idan ya zauna cikin aji sai an sami wani mayen yayi mishi magana. Ko mintina biyar da isa baiyi ba sai ga Layla da tun daga nesa take fadin
"Hamma Rayyann!"
Tana daga mishi hannu da fara'a a fuskarta, yana kallon Rayyan din ya lumshe idanuwan shi yana bude su a kan Layla da take karasowa, doguwar rigace ta atamfa a jikinta, dinkin da ake kira "Fitted gown" a turance, dan tabi jikinta sosai, sai mayafi data dan rataya a wuyanta, ga dauri ta kafa, fuskarta da kwalliya marar nauyi. Da wahala ta wuce ka baka sake kallonta ba, kafin kaga idanuwanta jikinta ne zai fara jan hankalinka, balle kuma idan ka tsayar da hankalinka akan fuskarta da take da wani irin kyau mai sanyi. Dan Bilal sai da yaji jikin shi ya dauki dumi, hakanne yasa shi sauke idanuwan shi daga kanta
"Hamma..."
Itama zama ta gyara tana dan juyawa taga an mata quri
"Wayyoo Allah..."
Ta furta da karfi saboda gabanta ya fadi sosai
"Hamma"
Ta furta har lokacin da tsoro a muryarta
"Baki da hankali? Da safe zaki zo kina mun ihu a kunne?"
Ita bata neman tashin hankali, tasan ko tafiya zasuyi zai zauna a gaban mota ne. Shisa ma ta bude bayan motar ta shiga abinta. Baccine a idanuwanta har sun mata nauyi
"Kayi hakuri, dan girman Allah Hamma, wallahi bansan kana nan ba sam sam, ina kwana"
Ta karashe a gajiye, hararta yayi yana jan wani tsaki dai-dai lokacin da Bilal ya shigo motar ya zauna. Juyawa yayi yana kallon su hadi da sauke numfashi
"Me kuke nufi?"
Ya bukata, tunda shi yasan su duka Abbu ya baiwa mota, baice ya zama direban su ba balle su kame a bayan mota gabaki daya
"Wani ya dawo gaba"
Ya fadi yana kallon Rayyan daya kauda kai
"Magana fa nakeyi"
Cikin ido Rayyan ya kalle shi
"Kana shamun kamshi tun da safe"
Ya fadi kamar wani dan karamin yaron da kaiwa dukan tsiya kazo kuma kana yiwa dariya. Layla Bilal ya kalla, ita kuma ta kalli Rayyan din kamar tana neman izinin shine kafin ta koma, shikuma ya rigada ya lumshe idanuwan shi. Numfashi Bilal ya sauke yana runtsa idanuwan shi ya bude su a lokaci daya. Tuqi zaiyi, yana bukatar gabaki daya natsuwar shi, idan ya biye musu zasu birkita mishi lissafi, hakan yasa shi gyara zama, addu'a yayi yana jan motar suka fice daga gidan, sun kama hanyar da zata fitar dasu daga Kano kenan Rayyan ya bude idanuwan shi yana ganin Layla a zaune a kusa da shi
"Mayya ce ke? Dole sai inda nake zaki zauna?"
Wani abu taji ya tokare mata zuciya yanayin yanda Rayyan din yayi magana. Inda ta tashi ta koma gaba ya bude ido kamar yanda yayi tana da tabbas zaice wani abu, dole saiya nemi dalilin da zai sata dana sanin tafiyar nan, bayan tun da satin ya kama take tunanin yanda zata zauna mota daya da shi, nishadin duk da takeyi ya dishe mata shi
"Hamma ka tsaya in dawo gaba"
Layla ta fadi da wani yanayi a muryarta, ta mudubin gaban motar Bilal ya kalle su
"Na dora wayata a kujerar, kuyi zaman ku"
Kafin ta karayin magana ya kunna radio din motar yana kure maganar
"Ka fasa mana kunne Bilal!"
Rayyan ya fadi a masife, ko kallon su Bilal baiyi ba, balle kuma suyi tunanin zai saurare su, ba yanda za'ayi su rabashi da nutsuwar shi yana tuqi. Matsawa Layla tayi tana kara bada tazara tsakaninta da Rayyan din, jingina kanta tayi da jikin motar tana rufe idanuwan ta, duk yanda take jin ranta na mata susa bai hana bacci dauketa ba, Rayyan kallonta yakeyi duk da yasan bacci ya kamata yayi. Yanajin inama ace haka zata zauna, yanda zuciyar shi tayi wani luf a kirjin shi abin ya mishi dadi, amman yasan tashi zatayi, bude idanuwanta zatayi ta hargitsa mishi komai kamar yanda ta saba. Baisan me yasa zata zo da idanuwan mage ba.
Idanuwan shi na kafe a kanta, tana ta baccin ta, a cikin baccin ta juyo kwanciya, ganin da yayi kamar wuyanta zaiyi ciwo yasa shi girgiza kai kawai, babu wani abu da zatayi dai-dai, baccin ma ba zatayi shi dai-dai ba. Yana wannan mitar a zuciyar shi ya mika hannu ta baya dan ya dauko ruwan da Bilal ya ajiye, sai jin kan Layla yayi saman hannun shi, kamar ya mika ne dan ta kwanto, da dayan hannun shi ya tallabe wannan, yana zare shi a hankali, ruwan ya dauka sai ya dan janyo jikin shi yana gyara zama yanda kanta zai kwanta a kafadar shi da kyau.
Robar ruwan ya bude yana sha sosai, ya mayar ya kulle, yanajin Layla ta kara gyara kwanciyar ta a jikin shi, tana kwantowa sosai. Wani irin dokawa zuciyar shi takeyi kamar zata fito daga kirjin shi
"Mayya..."
Ya furta a hankali yana sauke numfashi, sosai ya jingina kan shi da motar yana lumshe idanuwan shi, bugun zuciyar shi yake saurare da yake ji har cikin kunnuwan shi, kafin wata natsuwa daya kwana biyu baiji ba ta saukar mishi, bacci mai sanyi na dauke shi, baisan sanda ya jingina nashi kan dana Layla da yake kafadar shi ba. Kawai abinda ya sani wannan karin baccin nashi babu mugayen mafarkai ko daya. Ta gaban mudubi Bilal ya hango su, yanajin kamar an soka mishi wani abu a kirjin shi, sosai zuciyar shi ke dokawa kamar mai shirin samun matsalar bugun zuciya.
Shi yake bukatar kulawa
Shi yake cikin matsala
Shi yake bukatar Abbu da Mami su fadawa Rayyan daya kula da shi
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 26, 2020
12
Kan shi ciwo yake kamar zai rabe gida biyu. Dan bai iya takawa gida ba, sai da ya hau mashin. Da yake ba surutu yake son yi ba, canjin dari da ya baiwa mai mashin dinma da hannu yayi mishi alama daya tafi
"Allah yasa kar in ga kowa, Allah yasa kar kowa ya ganni"
Rayyan ya furta a cikin kan shi. Bayason mutane, baya kuma son 'yan cikin gidan da suke haya fiye da sauran mutane, saboda suna saka shi yanayin magana a lokuttan da ko kadan bayason yi. Gashi yanzun Bilal yace ya dinga yiwa mutane murmushi idan sun mishi magana, baisan ya zai fara ba, motsa labban shi kawai yakeyi wasu lokuttan, tunda bayajin yin fara'a sam-sam. Ya gaisa dasu, baisan kirkin me Bilal yake so ya dinga musu ba
"Ko rashin lafiya ta kamaka ba fata nake ba, su dinne mutanen farko da zasu taimaka maka tunda kuna gida, kasan abubuwan nan, kasan hakkin makota Hamma"
Bilal din ya fada mishi
"Bana son su"
Shine amsar daya baiwa Bilal din
"Su ma na tabbata ba son ka sukeyi ba. Ka dinga murmushi dan Allah in zaka gaisa da mutane, ka dan saki fuska ba kamar an maka dole ba"
Bilal saiya dinga mishi magana kamar baisan dolen akayi mishi yake gaisawa da su ba. Hakkin musulunci kawai yake saukewa. Kamar barawo haka yake sanda wajen shiga gidan, sam baya so wani ya gan shi. Kusan da gudu ya karasa dakin su yana daga labulen ya shiga da sauri
"Subhanallah..."
Bilal da yake zaune ya bude kular abinci ya fadi, dan sosai Rayyan din ya bashi tsoro
"Assalamu alaikum..."
Cewar Rayyan, amsawa Bilal din yayi yana girgiza kai kawai. Taliya ce da miya sai soyayyen dankalin turawa, rabon su da dora tukunya a wuta harya manta, sai dai ko in sunyi marmarin shan shayi zasu dafa, amman Aysha na musu kokari matuka ta fannin abinci tunda tazo makarantar. Bilal baiyi mishi tayin abinci ba, tunda yasan sai yayi wanka, aikam ficewa daga dakin Rayyan yayi. Sai bayan yayo wankan ya dawo ya sake kayane ya zauna yana mayar da numfashi Bilal yace
"Abinci fa?"
Kai Rayyan din ya girgiza mishi
"Babu abinda kaci fa duk yau"
Tunda tare suka fita, kuma yasan babu abinda Rayyan din zaici a waje banda biskit, idan ya samu kalar wanda yakeci din kenan.
"Zanci sai anjima"
Rayyan ya furta yana kwanciya kan katifar da yake zaune a gefe, sai yaji wani dadi a ran shi daya kwanta din, kamar gajiyar daya kwaso ta dan sake shi. Wayar shi da Bilal ya janyone yaga yau din Alhamis, numfashi ya sauke
"Azumi kakeyi ko?"
Ya tambaya
"Me yasa baka gajiya da surutu? Dan Allah ka kyaleni ni"
Rayyan yayi maganar cikin alamar gajiya. Murmushi kawai Bilal din yayi. Bai taba gane azumin alhamis da litinin baya wuce Rayyan ba sai wannan dawowar da sukayi. Sai yake tuna ranakun da Rayyan din zai wuni baici komai ba, duk surutun da zai mishi. Sai sun dawo sallar Magriba tukunna, ko in yayo alwala ya shigo daki an kira, Bilal zai ga ya sha ruwa, ko yaci dabino. To bai taba kawo komai a ran shi ba, tunda Rayyan na da shan ruwa, kuma dabino kamar biskit ne a wajen shi, da wahala ka raba jakar shi da su, ko cikin kayan shi ka duba zaka samu.
Zurfin ciki irin na Rayyan baya gajiya da bashi mamaki, shima ranar alhamis din daya san azumi Rayyan yakeyi, alhamis din kuma daya tabbatar da abinda ya dade da sani, wajen Rayyan din yaje daga nasu bangaren, ya same shi a can karkashin wata bishiya, inda yake shimfida darduma ya zauna idan basu da darasi ba kuma yason komawa gida. Tunda wani lokaci ko baiyi niyya ba idan ya zauna cikin aji sai an sami wani mayen yayi mishi magana. Ko mintina biyar da isa baiyi ba sai ga Layla da tun daga nesa take fadin
"Hamma Rayyann!"
Tana daga mishi hannu da fara'a a fuskarta, yana kallon Rayyan din ya lumshe idanuwan shi yana bude su a kan Layla da take karasowa, doguwar rigace ta atamfa a jikinta, dinkin da ake kira "Fitted gown" a turance, dan tabi jikinta sosai, sai mayafi data dan rataya a wuyanta, ga dauri ta kafa, fuskarta da kwalliya marar nauyi. Da wahala ta wuce ka baka sake kallonta ba, kafin kaga idanuwanta jikinta ne zai fara jan hankalinka, balle kuma idan ka tsayar da hankalinka akan fuskarta da take da wani irin kyau mai sanyi. Dan Bilal sai da yaji jikin shi ya dauki dumi, hakanne yasa shi sauke idanuwan shi daga kanta
"Hamma..."