Sashe 89
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ko faduwa tayi yaga jini duk wani abu da yake kwance a tare da shi saiya ta shi. Yana son Layla, daga baya yasan soyayyar su Ayya, amman son da yake yiwa Nur daban ne, bai san ko dan ita yake gani tana rage mishi kewar Bilal ba, ko rike ta yayi yakan ji wani kusanci da Bilal na ban mamaki. Bai san lokacin da ya daina duba hanyar dawowar Bilal ba, rana daya ya tashi yaji zuciyar shi tayi wani sanyi da yake tare da hakuri, sanyin da yazo mishi da daukar kaddara. Yayi kuka dai ranar, sosai yayi kuka a jikin Layla, kukan da bai bari zuciyar shi tayi mishi ba saboda yana saka ran dawowar Bilal din.
Abinda ya zame mishi jiki shine tura kudi a account din Bilal, duk da yana da wani bankin da yake ajiya, duk yanda yaso ya daina saiya kasa, daga safiyar da aka biya albashi zuwa yamma sai ya kasa samun natsuwa idan bai tura ba, a lokutta irin ranar yakan ji daman ace yaga gawar Bilal, da ya dibi kasa ya zuba a kabarin shi, da tuni ya aminta da rashin shi. Amman har abada akwai bangaren shi da ba zai taba daina jin kamar Bilal din yana da rai ba.
"Layla ki kira mun Bilya a wayata, ki saka mun a speaker..."
Rayyan ya fadi yana gyarawa Nur madaurin takalmin ta
"Mota na mun wata kara tun jiya, mutuwa tayi jiya fa a hanya, dakyar ma ta tashi, in munje gida sai yazo ya dauka"
Wayar tashi Layla ta dauko can karshen gado
"Yaushe screen dinka ya kara fashewa?"
Ta bukata
"Nur ta fado da ita shekaranjiya"
Kai kawai Layla ta girgiza, idan tace ya daina bata wayar shi ba zaiji ba. Tunda yana da kudin sake screen. Tana jin dadin yanda bako da yaushe soyayyar yarinyar take rufe mishi ido ba. Kusan tama fi tsoron shi duk da baya dukanta, yana mata ihun da ba ita ba har Layla sai ta tsorata.
"Na ga karamar wayar ka, bayan gado ta fada...mantawa nayi tun jiya... Na saka ta caji tana falo..."
Layla ta fadi tana duba contacts din shi, amsa ta yayi hakan yasa ta daga kai ta kalle shi, da yake suna ne ta fara rubutawa ta saka "Bil..." bata karasa ba sai ta kira lambar farko data fito, ta amsa Rayyan ta mayar da hankalin ta kan screen din, zuciyarta na wata irin dokawa. Jikinta har rawa yake lokacin da ta kashe kiran ganin lambar Bilal, wajen kiran ta shiga ta goge kar Rayyan ma ya gani. Kafin ta kira mishi Bilya din, sai da ta fara ringing sannan ta karasa ta mikawa Rayyan din. Mayafin ta, jaka da sauran tarkacen da zasu bukata ta dauka suka fice daga gidan.
Sosai suka bata lokaci akan hanya saboda Rayyan yayi kwana ya tsaya siyawa Nur mangoron da tunda ta hango shi ta cikin motar take zillo tana dukan gilashin kamar zata fita ta dauka
"Daada...ina so, ina so"
Take fadi tana sake maimaitawa
"Dan ubanki sai kin fasa mun kunne ne?"
Cewar Layla tana juyawa ta harari Nur din da take sake ziro kai tana kiran
"Daada"
Kamar yanda take cewa Rayyan, duk yanda Layla taso ta gyara mata ya koma "Daddy" taki. Harta hakura ta kyaleta.
"Da ni nace ka tsaya a siya mangoro babu surutun da ba zakayi mun ba"
Layla ta fadi cikin sigar mitar da Rayyan bai ko kulata ba. Bayan motar ya ajiyewa Nur ledar yana fadin
"Karki taba sai munje gidan Ayya sai a wanke a yanka"
Kai ta daga mishi tana murmushin jin dadi. Da suka karasa ma, Rayyan bai shigar da motar ba tunda Bilya zai zo ya dauka. Anan kofar gida ya ajiye ta, shi ya fara fita ya bude bayan ya taimakawa Nur yana sauko da ita, ledar mangoron ya dauka, kiciniyar da zata fara yi da shi yasa ya sakar mata yana kallon ta, ganin zata fadi yasa shi karba ya zare guda daya a ciki ya bata ta rungume shi kamar ta rike jariri. Dariya yayi kawai yana rufe motar. Tare suka shiga gidan, Nur na rugawa da gudu ta nufi bangaren Ayya, shi baima karasa ba yaga Bilya na kiran shi, dagawa yayi yana sakawa a kunnen shi
"Gani a kofar gida yallabai"
Batare da Rayyan ya amsa ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana juyawa. A can gefe ya hango Bilya da yana ganin shi ya fara takowa, sake gaisawa sukayi Rayyan ya mika mishi mukullin motar, yana fada mishi abinda yaji tana yi
"Dan Allah ka duba min kafin anjima in dai ba wata matsala bace babba"
Rayyan ya fadi, saboda gabaki daya satin da zai kama aikin dare gare shi, yafi jin dadi ace da motar shi, gashi yasan halin Bilya, ya iya gyara ga ba ha'inci, amman akwai shiririta.
"In shaa Allah zan kiraka dana duba"
Sallama suka yi, ya tsaya duba text din MTN da suka cire mishi har naira dari na wani caller tune da bai san lokacin da ya shiga tsarin ba. Karamin tsaki yaja kawai, yana tura musu sakon da zai bashi damar fita daga tsarin, matsalar shi da su kenan. Sai su fara cire maka kudin da babu dalili. Sakon Bappa ya amsa ta manhajar WhatsApp, shima Allah ya kama shi, addu'ar Baba taci, sosai yaso ya sake gudu yabar kasar, yanzun gashi nan da matar shi harda yaro daya. Sai dai yaki garin Kano sam, a Kaduna yayi zaman shi, in dai ya shigo sai dai ziyara, zumunci mai karfi ne a tsakanin su, duk da Rayyan ba zai kira matar Bappan da Layla kawaye ba.
Sukan gaisa dai idan sun shigo gari da Bappa din, da ta haihu kuma Layla taje ranar suna ta dawo washegari. Iya wannan din ya ishi su biyun, dan suna zumunci babu inda ya zamana dole matan su ma suyi. Juyawa Rayyan yayi bayan ya saka wayar a aljihun shi, ya kama kofar gidan zai tura kenan yaji kamar iska ta dibo mishi muryar da take cikin kan shi ta fito da ita waje tana dukan kunnuwan shi da muryar
"Hamma..."
Sai da ya runtsa idanuwan shi kafin ya bude su yana tura kofar
"Hamma..."
Aka sake kiran shi cikin muryar da wannan karin ba kunnuwan shi kawai ta daka ba, har da zuciyar shi. Idanuwan shi ya sake runtsawa a hankali ya furta
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Saboda ya bawa shekara wajen biyu baya rabon daya shiga cikin wannan yanayin, ba zai koma ba, ba zai koma lokuttan da yake jin kamar takun tafiyar Bilal da baisan yana da sauti ba sai bayan ya rasa shi, ba zai koma lokacin da yake neman fuskar Bilal a cikin duk wani taro da zai gani, a masallacin juma'a, har a wajen jana'iza idan ya samu halarta. Lokuttan da muryoyin mutane da yawa a cikin gidan su take mishi kama da ta Bilal, lokuttan da zai iya rantsewa ba'a cikin kan shi kawai yakan ji muryar Bilal ba. Yana da yarinya yanzun, yana da Nur, zaiyi duk wani kokarin ganin bai rabu da nutsuwar da yake tare da ita ba koya ne.
Saboda tana bukatar shi da duka wata natsuwa da yake da ita. Ba yanzun ba kawai, har lokuttan da zasu zo a gaba, lokuttan da ko tunanin su yayi sai kirjin shi ya dauki zafi, tana bukatar tsayayyen uba da zata rugo wajen shi da dukkan tambayoyin da mutane zasu saka tayi mishi, ba zai bari rashin Bilal ya raunana shi ba. Kafar shi ya daga ya saka guda daya a cikin gidan yaji an dafa mishi kafada
"Hamma"
Wannan karin da rauni muryar ta fito tana tsinka abubuwan da Rayyan bai san suna hade a jikin shi ba, kafin zuciyar shi ta fara dokawa cikin sautin da yake ji har cikin kunnuwan shi, a hankali ya juyo yana fara sauke idanuwan shi kan fuskar Bilal, yawu yake tattarawa yana so ya hadiye ko zai jika makoshin shi da yake ji a bushe, ya bude bakin shi yafi sau biyar yana mayar da shi ya rufe
"Hamma ni ne"
Bilal ya sake fadi, Rayyan bai yarda ba, ko yaushe zai iya farkawa, wani zai iya zuwa ya tashe shi abinda yake faruwa ya zamana mafarki. Hannun shi ya daga yana kaiwa fuskar Bilal ya taba, ba zai tuna ko ya yanayin Bilal yake a duk mafarkan shi ba, sake taba fuskar yayi, wannan karin samu yayi ya gyara tsayuwar shi ya saka duka hannuwan shi biyu yana taba fuskar Bilal din yana son tabbatar da cewa shine a tsaye a gaban shi ba mafarki yake yi ba
"Ni ne, ni ne Hamma"
Bilal ya sake fadi muryar shi na karyewa sosai, wani irin numfashi Rayyan yaja yana sauke shi hadi dayin dariya mai sauti, dariyar da ta saka yaji idanuwan shi sun cika taf da hawaye, dariya ce da babu wani nishadi a tare da ita, wani abu yake so ya fadi amman ya kasa
"Kace wani abu Hamma... Dan Allah kayi magana"
Dariyar Rayyan ya sake yi, yana kai hannuwa ya share kwallar da yake ji a cikin idanuwan shi, juyawa kawai yayi ya tura kofar wannan karin yana shigewa cikin gidan, yana jin Bilal na bin bayan shi, juyawa yayi ya daga mishi hannu cikin alamar da take nuna ya daina bin shi, kafin ya sake juyawa yaci gaba da tafiya, ko hanya baya gani sosai saboda idanuwan shi da suke cike taf da hawaye. Sake juyowa yayi wannan karin duka hannayen shi biyu ya saka ya hankade Bilal din
"Hamma"
Bilal ya kira yana dafe kirjin shi inda Rayyan din ya hankade yana dorawa da
"Kayi hakuri..."
Na shi idanuwan cike da hawaye shima, sai da Rayyan ya dan duqa saboda yanda yake jin numfashin shi kamar baya kaiwa kirjin shi, kafin ya mike tsaye sosai yana kallon Bilal
"Ba kwanaki ba, ba satika ba, Bilal ba wata daya ba. Shekaru, shekaru fa... Shekaru zaka dora akan kalmar hakuri?"
Abinda ya zame mishi jiki shine tura kudi a account din Bilal, duk da yana da wani bankin da yake ajiya, duk yanda yaso ya daina saiya kasa, daga safiyar da aka biya albashi zuwa yamma sai ya kasa samun natsuwa idan bai tura ba, a lokutta irin ranar yakan ji daman ace yaga gawar Bilal, da ya dibi kasa ya zuba a kabarin shi, da tuni ya aminta da rashin shi. Amman har abada akwai bangaren shi da ba zai taba daina jin kamar Bilal din yana da rai ba.
"Layla ki kira mun Bilya a wayata, ki saka mun a speaker..."
Rayyan ya fadi yana gyarawa Nur madaurin takalmin ta
"Mota na mun wata kara tun jiya, mutuwa tayi jiya fa a hanya, dakyar ma ta tashi, in munje gida sai yazo ya dauka"
Wayar tashi Layla ta dauko can karshen gado
"Yaushe screen dinka ya kara fashewa?"
Ta bukata
"Nur ta fado da ita shekaranjiya"
Kai kawai Layla ta girgiza, idan tace ya daina bata wayar shi ba zaiji ba. Tunda yana da kudin sake screen. Tana jin dadin yanda bako da yaushe soyayyar yarinyar take rufe mishi ido ba. Kusan tama fi tsoron shi duk da baya dukanta, yana mata ihun da ba ita ba har Layla sai ta tsorata.
"Na ga karamar wayar ka, bayan gado ta fada...mantawa nayi tun jiya... Na saka ta caji tana falo..."
Layla ta fadi tana duba contacts din shi, amsa ta yayi hakan yasa ta daga kai ta kalle shi, da yake suna ne ta fara rubutawa ta saka "Bil..." bata karasa ba sai ta kira lambar farko data fito, ta amsa Rayyan ta mayar da hankalin ta kan screen din, zuciyarta na wata irin dokawa. Jikinta har rawa yake lokacin da ta kashe kiran ganin lambar Bilal, wajen kiran ta shiga ta goge kar Rayyan ma ya gani. Kafin ta kira mishi Bilya din, sai da ta fara ringing sannan ta karasa ta mikawa Rayyan din. Mayafin ta, jaka da sauran tarkacen da zasu bukata ta dauka suka fice daga gidan.
Sosai suka bata lokaci akan hanya saboda Rayyan yayi kwana ya tsaya siyawa Nur mangoron da tunda ta hango shi ta cikin motar take zillo tana dukan gilashin kamar zata fita ta dauka
"Daada...ina so, ina so"
Take fadi tana sake maimaitawa
"Dan ubanki sai kin fasa mun kunne ne?"
Cewar Layla tana juyawa ta harari Nur din da take sake ziro kai tana kiran
"Daada"
Kamar yanda take cewa Rayyan, duk yanda Layla taso ta gyara mata ya koma "Daddy" taki. Harta hakura ta kyaleta.
"Da ni nace ka tsaya a siya mangoro babu surutun da ba zakayi mun ba"
Layla ta fadi cikin sigar mitar da Rayyan bai ko kulata ba. Bayan motar ya ajiyewa Nur ledar yana fadin
"Karki taba sai munje gidan Ayya sai a wanke a yanka"
Kai ta daga mishi tana murmushin jin dadi. Da suka karasa ma, Rayyan bai shigar da motar ba tunda Bilya zai zo ya dauka. Anan kofar gida ya ajiye ta, shi ya fara fita ya bude bayan ya taimakawa Nur yana sauko da ita, ledar mangoron ya dauka, kiciniyar da zata fara yi da shi yasa ya sakar mata yana kallon ta, ganin zata fadi yasa shi karba ya zare guda daya a ciki ya bata ta rungume shi kamar ta rike jariri. Dariya yayi kawai yana rufe motar. Tare suka shiga gidan, Nur na rugawa da gudu ta nufi bangaren Ayya, shi baima karasa ba yaga Bilya na kiran shi, dagawa yayi yana sakawa a kunnen shi
"Gani a kofar gida yallabai"
Batare da Rayyan ya amsa ba ya sauke wayar daga kunnen shi yana juyawa. A can gefe ya hango Bilya da yana ganin shi ya fara takowa, sake gaisawa sukayi Rayyan ya mika mishi mukullin motar, yana fada mishi abinda yaji tana yi
"Dan Allah ka duba min kafin anjima in dai ba wata matsala bace babba"
Rayyan ya fadi, saboda gabaki daya satin da zai kama aikin dare gare shi, yafi jin dadi ace da motar shi, gashi yasan halin Bilya, ya iya gyara ga ba ha'inci, amman akwai shiririta.
"In shaa Allah zan kiraka dana duba"
Sallama suka yi, ya tsaya duba text din MTN da suka cire mishi har naira dari na wani caller tune da bai san lokacin da ya shiga tsarin ba. Karamin tsaki yaja kawai, yana tura musu sakon da zai bashi damar fita daga tsarin, matsalar shi da su kenan. Sai su fara cire maka kudin da babu dalili. Sakon Bappa ya amsa ta manhajar WhatsApp, shima Allah ya kama shi, addu'ar Baba taci, sosai yaso ya sake gudu yabar kasar, yanzun gashi nan da matar shi harda yaro daya. Sai dai yaki garin Kano sam, a Kaduna yayi zaman shi, in dai ya shigo sai dai ziyara, zumunci mai karfi ne a tsakanin su, duk da Rayyan ba zai kira matar Bappan da Layla kawaye ba.
Sukan gaisa dai idan sun shigo gari da Bappa din, da ta haihu kuma Layla taje ranar suna ta dawo washegari. Iya wannan din ya ishi su biyun, dan suna zumunci babu inda ya zamana dole matan su ma suyi. Juyawa Rayyan yayi bayan ya saka wayar a aljihun shi, ya kama kofar gidan zai tura kenan yaji kamar iska ta dibo mishi muryar da take cikin kan shi ta fito da ita waje tana dukan kunnuwan shi da muryar
"Hamma..."
Sai da ya runtsa idanuwan shi kafin ya bude su yana tura kofar
"Hamma..."
Aka sake kiran shi cikin muryar da wannan karin ba kunnuwan shi kawai ta daka ba, har da zuciyar shi. Idanuwan shi ya sake runtsawa a hankali ya furta
"Inalillahi wa ina ilaihi raji'un"
Saboda ya bawa shekara wajen biyu baya rabon daya shiga cikin wannan yanayin, ba zai koma ba, ba zai koma lokuttan da yake jin kamar takun tafiyar Bilal da baisan yana da sauti ba sai bayan ya rasa shi, ba zai koma lokacin da yake neman fuskar Bilal a cikin duk wani taro da zai gani, a masallacin juma'a, har a wajen jana'iza idan ya samu halarta. Lokuttan da muryoyin mutane da yawa a cikin gidan su take mishi kama da ta Bilal, lokuttan da zai iya rantsewa ba'a cikin kan shi kawai yakan ji muryar Bilal ba. Yana da yarinya yanzun, yana da Nur, zaiyi duk wani kokarin ganin bai rabu da nutsuwar da yake tare da ita ba koya ne.
Saboda tana bukatar shi da duka wata natsuwa da yake da ita. Ba yanzun ba kawai, har lokuttan da zasu zo a gaba, lokuttan da ko tunanin su yayi sai kirjin shi ya dauki zafi, tana bukatar tsayayyen uba da zata rugo wajen shi da dukkan tambayoyin da mutane zasu saka tayi mishi, ba zai bari rashin Bilal ya raunana shi ba. Kafar shi ya daga ya saka guda daya a cikin gidan yaji an dafa mishi kafada
"Hamma"
Wannan karin da rauni muryar ta fito tana tsinka abubuwan da Rayyan bai san suna hade a jikin shi ba, kafin zuciyar shi ta fara dokawa cikin sautin da yake ji har cikin kunnuwan shi, a hankali ya juyo yana fara sauke idanuwan shi kan fuskar Bilal, yawu yake tattarawa yana so ya hadiye ko zai jika makoshin shi da yake ji a bushe, ya bude bakin shi yafi sau biyar yana mayar da shi ya rufe
"Hamma ni ne"
Bilal ya sake fadi, Rayyan bai yarda ba, ko yaushe zai iya farkawa, wani zai iya zuwa ya tashe shi abinda yake faruwa ya zamana mafarki. Hannun shi ya daga yana kaiwa fuskar Bilal ya taba, ba zai tuna ko ya yanayin Bilal yake a duk mafarkan shi ba, sake taba fuskar yayi, wannan karin samu yayi ya gyara tsayuwar shi ya saka duka hannuwan shi biyu yana taba fuskar Bilal din yana son tabbatar da cewa shine a tsaye a gaban shi ba mafarki yake yi ba
"Ni ne, ni ne Hamma"
Bilal ya sake fadi muryar shi na karyewa sosai, wani irin numfashi Rayyan yaja yana sauke shi hadi dayin dariya mai sauti, dariyar da ta saka yaji idanuwan shi sun cika taf da hawaye, dariya ce da babu wani nishadi a tare da ita, wani abu yake so ya fadi amman ya kasa
"Kace wani abu Hamma... Dan Allah kayi magana"
Dariyar Rayyan ya sake yi, yana kai hannuwa ya share kwallar da yake ji a cikin idanuwan shi, juyawa kawai yayi ya tura kofar wannan karin yana shigewa cikin gidan, yana jin Bilal na bin bayan shi, juyawa yayi ya daga mishi hannu cikin alamar da take nuna ya daina bin shi, kafin ya sake juyawa yaci gaba da tafiya, ko hanya baya gani sosai saboda idanuwan shi da suke cike taf da hawaye. Sake juyowa yayi wannan karin duka hannayen shi biyu ya saka ya hankade Bilal din
"Hamma"
Bilal ya kira yana dafe kirjin shi inda Rayyan din ya hankade yana dorawa da
"Kayi hakuri..."
Na shi idanuwan cike da hawaye shima, sai da Rayyan ya dan duqa saboda yanda yake jin numfashin shi kamar baya kaiwa kirjin shi, kafin ya mike tsaye sosai yana kallon Bilal
"Ba kwanaki ba, ba satika ba, Bilal ba wata daya ba. Shekaru, shekaru fa... Shekaru zaka dora akan kalmar hakuri?"