Sashe 54
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rayyan ya sake kira, amman yaki yin wani kwakkwaran motsi, bawai ciwo bane Bilal bayayi, har yini sun tabayi a asibitin makaranta aka kara mishi ruwa, amman zuwa tara na dare kamar ma baiyi jinya ba, haka yake hidimar shi, bai taba ganin shi cikin hali irin wannan ba. Tunanin zuwa asibitine yazo ran shi, amman bai taba raina karfin shi ba sai da ya daga Bilal dan ya dauke shi yaji kafafuwan shi banda rawa babu abinda sukeyi, a hankali ya mayar da Bilal din ya kwantar, dakyar ya karasa mikewa yana fita daga dakin, ba zaice ga sanda ya cire takalman shi ba, sai da ya taka tsakar gidan su yabi takan ruwan da yaji har tsakiyar kan shi sannan ya gane babu takalma a kafafuwan shi. Abinda ko a daki da wahala ka same shi babu su, akwai wanda yake ajiyewa dan yawo a cikin daki kawai.
Yakan ce Bilal din na tako kasa ya shigo musu da ita, ko idan wani a cikin abokan shi yazo neman shi yana shigowa da kasa, shikuma bayaso ya taka kafar shi yaji kasa a cikinta ko ya take
"Kai da za'a saka a cikin kasa Hamma wanne gudunta kakeyi kuma?"
Bilal ya taba fada mishi, ya saka shi kwanaki maganar na mishi yawo, shisa ya daina cewa komai kan shigowa da kasar, amman zai iya sharewa sau goma, kuma da takalma a kafar shi in yana zaune, ko safa wasu lokuttan. Amman yau bashida wannan lokacin, Abdul kamar yanda yaji Bilal din na kira yaci karo da shi
"Rayyan"
Abdul din ya fadi cikin gaisuwa
"Ka taimaka mun, Bilal bashi da lafiya"
Rayyan ya fadi cikin wani yanayi yana dorawa da
"Zan kai shi asibiti..."
Cikin tashin hankali Abdul yace
"Subhanallah... Bilal din? Yana ina?"
Dan dazun nan suke maganar sun ga motar shi yayi parking, amman har daki Sulaiman yace ya kwankwasa yaji shiru ba ayi magana ba, kuma sun nemi wayar Bilal din a kashe, sunata mamakin inda ya shiga tun safiyar jiya, saboda shi din na mutane ne, kuma anyi wasan kwallo mai zafi, an lashe club din Barcelona da Bilal din yake bi, sunata neman shi ayi adawa. Amman shiru bai leqo su ba, har Abdul din yake cewa
"Su fa yan Barca haka suke, in su suka ci su addabi kowa, amman basa daukar dabi duk idan aka cinye su"
Anata dariya da fadin yanda Bilal ya san bambanci dabi irin na kwallon, da kuma yanda baya taba bari gardamar tayi nisan da zai zamana wani yaji babu dadi, in an matsa mishi da yawa yakan ce
"Ai shikenan, ku bani panadol in watsa ko zanji dama-dama"
Shikenan gardamar sai tazo karshe a kama dariya kuma. Kaf gidan babu wanda zaice ga rana daya da Bilal yayi mishi wani abu. Yanzun ma hanyar dakin su Rayyan ya nunawa Abdul da hannu yana juyawa. Har ya fara bin shi yayi tunanin kiran sauran yan gidan, in har yau Rayyan ya tsaya yayi magana mai tsayi da shi Bilal din na cikin yanayi sosai. Kafin kace me, kusan duk wanda yake gidan a lokacin ya fito sun nufi dakin su Bilal din har babu wajen da wasu zasu tsaya, Abdul da Rayyan ne suka kama shi, baima san duniyar da yake ba, daya daga cikin su ya dauki mukullin motar daya gani ajiye kan tebir suka fita da shi, sai dai su shidda suka iya tafiya asibitin duk kuwa tarin mutanen da suke son binsu.
Motar babu waje, mutum biyune a baya, sai Bilal na ukku da suka saka a tsakiya. Har Rayyan daya shiga gaba zai kulle kofar yaga wani da zai iya kirga ranakun da magana ta taba hadasu ya kutso, dole ya matsa mishi ya shiga ya rufo suka tafi. Babu fadan da ba'ayi musu ba a asibitin, da yake na kudi kawai suka nufa a maimakon na makaranta. Nan da nan aka fara bawa Bilal din taimakon gaggawa, Rayyan yaso tsayawa cikin dakin, amman bayason yin gardama da likitocin a bata lokaci wajen bawa Bilal taimako. Daga shi sai Sulaiman aka bari dan sauran da suka tabbatar Bilal din ya samu taimako duk sai suka tafi, da zasu barwa Rayyan motar ya girgiza musu kai
"Ban iya tuqi ba, ku tafi da ita kawai..."
Yana kula da kallon mamakin da sukeyi mishi, babu dai wanda ya furta komai. Da gaske yau yaga ranar mutane da Bilal kan fada mishi, wajen dubu sha biyar aka bukata tashin farko, shi kuma dubu uku da dari biyune a jikin shi tunda jirgi ya biyo, sai dai jakar shi na goye a bayan shi har lokacin. Akwai kuma ATM din shi a ciki, kudin duk ya kwashe ya biya jirgi, sauran dubu takwas a ciki. Kafin yayi wani yunkuri ma su Abdul sun harhada kudin hannun shi, shima saiya kara da dubu ukkun aka bayar.
Zaune suke a dakin shiru daga shi har Sulaiman din suna kallon Bilal, har sai wajen karfe tara na dare, Abdul shi kadai ya dawo, ya kawo musu darduma da kaya guda biyu dan su ya fara gani baisan kona waye a ciki ba. Harda brush ya dauko musu da McLean ya taho da shi. Tare suka mike da Sulaiman suna fadin
"Allah ya kara sauqi yasa kaffara ne, zamu dawo da safe in shaa Allah"
Kai Rayyan ya jinjina
"Mungode...nagode sosai. Nagode"
Murmushi Abdul yayi
"Haba maza ai ana tare"
Ya fadi suna danyin dariya, sosai Rayyan yaso yayi murmushi amman baya cikin yanayin. Kai kawai ya iya jinjina musu, suna ficewa daga dakin. Mikewa yayi shima ya shiga bandaki ya dauro alwala, magariba da isha'i yayi, yau Bilal kawai yaiwa addu'a ya tashi ya dawo yana jan kujerar sosai ya matsa kusa da gadon Bilal din
"Me ya same ka haka Bilal?"
Yayi tambayar a zuciyar shi yana sauke numfashi, saboda likita yace mishi jinin Bilal din yayi wani irin hawa. Har sai da yaji tsoro da yaga takardar. Kwata-kwata Layla ta makale a wani waje cikin kan shi saboda Bilal ya danneta, sai yanzun ne ta fado mishi, wani sabon tashin hankalin na dirar masa, watakila itama bata da lafiyar. Ya laluba wayar shi baiji ta ba, saiya kula cikin kayan da Abdul ya kawo harda wayoyin su shi da Bilal da cajar waya ya hado. Shikam zuwa yanzun baisan kalar godiyar da zai musu ba, sai dai in Bilal ya tashi shi zaifi sanin abinda ya kamata.
Wayar Bilal ya tashi ya saka a caji dan yaganta a kashe, aikam cajin ne babu. Sai da yaga ta dauka sannan ya dawo ya zauna. Gwada lambar Layla yayi inda yai nasara ta shiga, har ta kusa yankewa sannan aka daga, wani irin numfashi ya sauke
"Layla..."
Ya kira daga lungun zuciyar shi, yanajin kamar yabi ta cikin wayar ya leqa inda take yaga lafiyar ta.
"Layla..."
Ya sake kira, muryarta can kasa ta amsa
"Hamma"
Lumshe idanuwan shi yayi yanajin yanda zuciyar shi ke rawa, nutsuwar da ta kwace mishi yake nema koya take, iya wadda zai samu karfin yi mata magana yaji inda ta shiga haka. Amman ya kasa samu
"Hamma ban da lafiya"
Layla ta fadi ta dayan bangaren, cikin wani mawuyacin yanayi da ya saka Rayyan din mikewa, sai dai ya kasa kara yin motsi saboda Bilal da yake gani a kwance shima, tunani yake ko akwai hanyar da zaibi ya raba kan shi gida biyu yabar daya anan asibitin dayan kuma yaje wajen Layla, dan sai yake jin kamar kuka take kokarin dannewa, zuciyar shi ciwo takeyi, ciwon daya kama ta nan take, dakyar ya iya cewa
"Kina ina? Me ya same ki? Waye a wajen ki?"
Ya kusa dakika biyar kafin ta amsa shi
"Bani da lafiya Hamma..."
Ta sake maimaitawa kamar bataji tambayoyin da yayi mata ba, wannan karin yaji sautin kukanta da ya kara mishi ciwon da zuciyar shi takeyi, dan baisan yanda zaiyi ba, baisan wa zai kira ya taimaka mishi ba. Ya bude baki zai sake yin magana ta riga shi da fadin
"Anisa...muna asibiti tun da safe. Hamma kana ina?"
Numfashi Rayyan ya sauke, a muryarta yake jin yanda take bukatar shi
"Ina asibiti, Bilal ba shi da lafiya. Me yasa zaku min haka Layla? Ya kuke so inyi? Ya zakuyi rashin lafiya lokaci daya?"
Ya karasa maganar yana bi da rokon yafiyar Allah dan yaji kamar yayi sabo, kamar yana kokarin dora ayar tambaya akan abinda basu da zabi a kai. Amman da gaske baisan yanda zaiyi ba
"Ki ba Anisa waya..."
Ya fadi muryar shi na fitowa da gajiyar da yake ji har cikin zuciyar shi
"Hello..."
Yaji muryar Anisa cikin kunnen shi
"Anisa ya jikin nata? Me suka ce yana damun ta?"
A nutse Anisa ta ce
"Zazzabi ne mai zafi, sai sunce tana bukatar samun hutu saboda jininta ya hau, sun mata allurar baccine tun da safe, sai yanzun ba dadewa ta tashi, gashi na hada mata shayi zata sha, likita yace za'a karayin wata allurar dan ta kara samun bacci... Da sauki ba kamar yanda muka zo ba"
Tunda ta fara magana yake saurarenta da dukkan nutsuwar shi, amman ya kasa gane yanda za ayi ace yarinya karama kamar Layla da yanzun ne zata cika shekara ashirin a duniya tana da hawan jini, ina ta samo shi? Tunanin me takeyi? Ko yace tunanin me sukeyi daga ita har Bilal da za ace suna da hawan jini haka. Lafiya kalau ya tafi yabar su duka, amman yanzun ya dawo lokaci daya duk sun kwanta. Gara Layla yaji muryarta, ta tashi, amman Bilal har yanzun ko motsi baiyi ba. A ina zasu sami hawan jini?
"Nagode Anisa.. Dan Allah ki zauna da ita kafin gobe, ina asibiti wajen Bilal, shima bashi da lafiya"
Ya karasa yana jin kirjin shi na zafi
"In shaa Allah...Allah ya basu lafiya"
Amsawa yayi da
"Amin"
Kafin ta mikawa Layla wayar
"Hamma..."
Ta kira shi tana saka shi jin kamar yayi fuka fuki zuwa inda take
"Kiyi hakuri Layla, Bilal ko motsi baiyi ba har yanzun... Ba zan iya barin shi ba, ba zan iya barin shi inzo wajen ki ba, dan Allah ki kula da kanki, ki sha tea din idan Anisa ta hada, ki kwanta ki huta kinji"
Yakan ce Bilal din na tako kasa ya shigo musu da ita, ko idan wani a cikin abokan shi yazo neman shi yana shigowa da kasa, shikuma bayaso ya taka kafar shi yaji kasa a cikinta ko ya take
"Kai da za'a saka a cikin kasa Hamma wanne gudunta kakeyi kuma?"
Bilal ya taba fada mishi, ya saka shi kwanaki maganar na mishi yawo, shisa ya daina cewa komai kan shigowa da kasar, amman zai iya sharewa sau goma, kuma da takalma a kafar shi in yana zaune, ko safa wasu lokuttan. Amman yau bashida wannan lokacin, Abdul kamar yanda yaji Bilal din na kira yaci karo da shi
"Rayyan"
Abdul din ya fadi cikin gaisuwa
"Ka taimaka mun, Bilal bashi da lafiya"
Rayyan ya fadi cikin wani yanayi yana dorawa da
"Zan kai shi asibiti..."
Cikin tashin hankali Abdul yace
"Subhanallah... Bilal din? Yana ina?"
Dan dazun nan suke maganar sun ga motar shi yayi parking, amman har daki Sulaiman yace ya kwankwasa yaji shiru ba ayi magana ba, kuma sun nemi wayar Bilal din a kashe, sunata mamakin inda ya shiga tun safiyar jiya, saboda shi din na mutane ne, kuma anyi wasan kwallo mai zafi, an lashe club din Barcelona da Bilal din yake bi, sunata neman shi ayi adawa. Amman shiru bai leqo su ba, har Abdul din yake cewa
"Su fa yan Barca haka suke, in su suka ci su addabi kowa, amman basa daukar dabi duk idan aka cinye su"
Anata dariya da fadin yanda Bilal ya san bambanci dabi irin na kwallon, da kuma yanda baya taba bari gardamar tayi nisan da zai zamana wani yaji babu dadi, in an matsa mishi da yawa yakan ce
"Ai shikenan, ku bani panadol in watsa ko zanji dama-dama"
Shikenan gardamar sai tazo karshe a kama dariya kuma. Kaf gidan babu wanda zaice ga rana daya da Bilal yayi mishi wani abu. Yanzun ma hanyar dakin su Rayyan ya nunawa Abdul da hannu yana juyawa. Har ya fara bin shi yayi tunanin kiran sauran yan gidan, in har yau Rayyan ya tsaya yayi magana mai tsayi da shi Bilal din na cikin yanayi sosai. Kafin kace me, kusan duk wanda yake gidan a lokacin ya fito sun nufi dakin su Bilal din har babu wajen da wasu zasu tsaya, Abdul da Rayyan ne suka kama shi, baima san duniyar da yake ba, daya daga cikin su ya dauki mukullin motar daya gani ajiye kan tebir suka fita da shi, sai dai su shidda suka iya tafiya asibitin duk kuwa tarin mutanen da suke son binsu.
Motar babu waje, mutum biyune a baya, sai Bilal na ukku da suka saka a tsakiya. Har Rayyan daya shiga gaba zai kulle kofar yaga wani da zai iya kirga ranakun da magana ta taba hadasu ya kutso, dole ya matsa mishi ya shiga ya rufo suka tafi. Babu fadan da ba'ayi musu ba a asibitin, da yake na kudi kawai suka nufa a maimakon na makaranta. Nan da nan aka fara bawa Bilal din taimakon gaggawa, Rayyan yaso tsayawa cikin dakin, amman bayason yin gardama da likitocin a bata lokaci wajen bawa Bilal taimako. Daga shi sai Sulaiman aka bari dan sauran da suka tabbatar Bilal din ya samu taimako duk sai suka tafi, da zasu barwa Rayyan motar ya girgiza musu kai
"Ban iya tuqi ba, ku tafi da ita kawai..."
Yana kula da kallon mamakin da sukeyi mishi, babu dai wanda ya furta komai. Da gaske yau yaga ranar mutane da Bilal kan fada mishi, wajen dubu sha biyar aka bukata tashin farko, shi kuma dubu uku da dari biyune a jikin shi tunda jirgi ya biyo, sai dai jakar shi na goye a bayan shi har lokacin. Akwai kuma ATM din shi a ciki, kudin duk ya kwashe ya biya jirgi, sauran dubu takwas a ciki. Kafin yayi wani yunkuri ma su Abdul sun harhada kudin hannun shi, shima saiya kara da dubu ukkun aka bayar.
Zaune suke a dakin shiru daga shi har Sulaiman din suna kallon Bilal, har sai wajen karfe tara na dare, Abdul shi kadai ya dawo, ya kawo musu darduma da kaya guda biyu dan su ya fara gani baisan kona waye a ciki ba. Harda brush ya dauko musu da McLean ya taho da shi. Tare suka mike da Sulaiman suna fadin
"Allah ya kara sauqi yasa kaffara ne, zamu dawo da safe in shaa Allah"
Kai Rayyan ya jinjina
"Mungode...nagode sosai. Nagode"
Murmushi Abdul yayi
"Haba maza ai ana tare"
Ya fadi suna danyin dariya, sosai Rayyan yaso yayi murmushi amman baya cikin yanayin. Kai kawai ya iya jinjina musu, suna ficewa daga dakin. Mikewa yayi shima ya shiga bandaki ya dauro alwala, magariba da isha'i yayi, yau Bilal kawai yaiwa addu'a ya tashi ya dawo yana jan kujerar sosai ya matsa kusa da gadon Bilal din
"Me ya same ka haka Bilal?"
Yayi tambayar a zuciyar shi yana sauke numfashi, saboda likita yace mishi jinin Bilal din yayi wani irin hawa. Har sai da yaji tsoro da yaga takardar. Kwata-kwata Layla ta makale a wani waje cikin kan shi saboda Bilal ya danneta, sai yanzun ne ta fado mishi, wani sabon tashin hankalin na dirar masa, watakila itama bata da lafiyar. Ya laluba wayar shi baiji ta ba, saiya kula cikin kayan da Abdul ya kawo harda wayoyin su shi da Bilal da cajar waya ya hado. Shikam zuwa yanzun baisan kalar godiyar da zai musu ba, sai dai in Bilal ya tashi shi zaifi sanin abinda ya kamata.
Wayar Bilal ya tashi ya saka a caji dan yaganta a kashe, aikam cajin ne babu. Sai da yaga ta dauka sannan ya dawo ya zauna. Gwada lambar Layla yayi inda yai nasara ta shiga, har ta kusa yankewa sannan aka daga, wani irin numfashi ya sauke
"Layla..."
Ya kira daga lungun zuciyar shi, yanajin kamar yabi ta cikin wayar ya leqa inda take yaga lafiyar ta.
"Layla..."
Ya sake kira, muryarta can kasa ta amsa
"Hamma"
Lumshe idanuwan shi yayi yanajin yanda zuciyar shi ke rawa, nutsuwar da ta kwace mishi yake nema koya take, iya wadda zai samu karfin yi mata magana yaji inda ta shiga haka. Amman ya kasa samu
"Hamma ban da lafiya"
Layla ta fadi ta dayan bangaren, cikin wani mawuyacin yanayi da ya saka Rayyan din mikewa, sai dai ya kasa kara yin motsi saboda Bilal da yake gani a kwance shima, tunani yake ko akwai hanyar da zaibi ya raba kan shi gida biyu yabar daya anan asibitin dayan kuma yaje wajen Layla, dan sai yake jin kamar kuka take kokarin dannewa, zuciyar shi ciwo takeyi, ciwon daya kama ta nan take, dakyar ya iya cewa
"Kina ina? Me ya same ki? Waye a wajen ki?"
Ya kusa dakika biyar kafin ta amsa shi
"Bani da lafiya Hamma..."
Ta sake maimaitawa kamar bataji tambayoyin da yayi mata ba, wannan karin yaji sautin kukanta da ya kara mishi ciwon da zuciyar shi takeyi, dan baisan yanda zaiyi ba, baisan wa zai kira ya taimaka mishi ba. Ya bude baki zai sake yin magana ta riga shi da fadin
"Anisa...muna asibiti tun da safe. Hamma kana ina?"
Numfashi Rayyan ya sauke, a muryarta yake jin yanda take bukatar shi
"Ina asibiti, Bilal ba shi da lafiya. Me yasa zaku min haka Layla? Ya kuke so inyi? Ya zakuyi rashin lafiya lokaci daya?"
Ya karasa maganar yana bi da rokon yafiyar Allah dan yaji kamar yayi sabo, kamar yana kokarin dora ayar tambaya akan abinda basu da zabi a kai. Amman da gaske baisan yanda zaiyi ba
"Ki ba Anisa waya..."
Ya fadi muryar shi na fitowa da gajiyar da yake ji har cikin zuciyar shi
"Hello..."
Yaji muryar Anisa cikin kunnen shi
"Anisa ya jikin nata? Me suka ce yana damun ta?"
A nutse Anisa ta ce
"Zazzabi ne mai zafi, sai sunce tana bukatar samun hutu saboda jininta ya hau, sun mata allurar baccine tun da safe, sai yanzun ba dadewa ta tashi, gashi na hada mata shayi zata sha, likita yace za'a karayin wata allurar dan ta kara samun bacci... Da sauki ba kamar yanda muka zo ba"
Tunda ta fara magana yake saurarenta da dukkan nutsuwar shi, amman ya kasa gane yanda za ayi ace yarinya karama kamar Layla da yanzun ne zata cika shekara ashirin a duniya tana da hawan jini, ina ta samo shi? Tunanin me takeyi? Ko yace tunanin me sukeyi daga ita har Bilal da za ace suna da hawan jini haka. Lafiya kalau ya tafi yabar su duka, amman yanzun ya dawo lokaci daya duk sun kwanta. Gara Layla yaji muryarta, ta tashi, amman Bilal har yanzun ko motsi baiyi ba. A ina zasu sami hawan jini?
"Nagode Anisa.. Dan Allah ki zauna da ita kafin gobe, ina asibiti wajen Bilal, shima bashi da lafiya"
Ya karasa yana jin kirjin shi na zafi
"In shaa Allah...Allah ya basu lafiya"
Amsawa yayi da
"Amin"
Kafin ta mikawa Layla wayar
"Hamma..."
Ta kira shi tana saka shi jin kamar yayi fuka fuki zuwa inda take
"Kiyi hakuri Layla, Bilal ko motsi baiyi ba har yanzun... Ba zan iya barin shi ba, ba zan iya barin shi inzo wajen ki ba, dan Allah ki kula da kanki, ki sha tea din idan Anisa ta hada, ki kwanta ki huta kinji"