Sashe 26
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani lokacin idan Rayyan ya kai mata wani dukan har a zuciyar shi yake jin zafin, amman daya kirata zata sake dawowa. Zaka rantse da Allah rashin kirkin da Rayyan yake mata take so. Bashi da inda yake jin sauki-sauki sai wajen Aisha. Yanzun ma daya huta yayi la'asar wajenta zai tafi ko zuciyar shi zatayi sanyi-sanyi. Da ba kulolin abinci bane a hannun shi sam ba zai karasa inda suke ba, ya koyawa kan shi nisanta da Layla, musamman in tana tare da Rayyan haka. Numfashi yaja yana fitarwa, duk wani karfin hali da zai iya ya tattaro yana takawa har inda take tsaye a bakin kofa, kafin yaga Rayyan da yake tattaro shara.
"Hamma Bilal..."
Layla ta fadi cikin sigar gaisuwa batare da ta kalle shi ba
"Layla..."
Ya amsa a sanyaye, yana shirin karawa da tambayar lafiyarta Rayyan ya dago, da bayan hannun shi ya kai ma Layla wani duka da yasa Bilal runtsa idanuwan shi kamar a kan shi hannun zai sauka, ya bude su a hankali yana ganin Layla da ta kauce tana kara turo baki
"Nace bai sharu ba kika tsaya gardama dani... Uban meye wannan?"
Ya karasa maganar yana nuna mata wata kasa da batasan daga inda ya sharota ba, saboda har karkashin gadon dakin nasu sai da ta share, kujerar shi da teburi kuwa daga su tayi ta ajiye a gefe, sif din kayan su har samanta sai da ta taka kujera ta share, haka ta sake takawa ta gogo daga saman zuwan jiki, tasan halin shi, dan yatsa zaisa ya dangwalo yaga ko da kura babu
"Wallahi shara hudu nayi Hamma"
Ta furta a gajiye, Rayyan din najan wani tsaki
"Ba abinda kika iya sai shirme..."
Ya fadi yana saka abin kwashe shara ya tattare kasar ya mika mata, karba tayi tana juyawa, shima cikin dakin ya shiga. Inda Bilal ya rufa mishi baya yana samarwa kulolin da suke hannun shi mazauni a tsakar dakin. Rayyan links din jikin rigar shi yake cirewa, dan manyan kayane a jikin shi, wani yadi ruwan kwai da ya sake fito da hasken fatar shi
"Ayya na tambayar ka"
Bilal ya fadi badan ya tsammaci amsa daga wajen Rayyan din ba, bai bashi amsar ba kuwa ya wuce yana nufar bandaki, dan ruwa kawai yake son watsawa. Tun da safe kafin su taho yace Layla ta bude dakin ta share musu. Yana saka kafar shi yaji kamar ya taka kasa. Wayarta da ta saukaka mishi komai yanzun ya kira
"Baki share dakin nan ba Layla"
Ya furta bayan ta daga, kafin ta amsa shi ya dora da
"Ki zo yanzun"
Gardamar da ta tsaya mishi da rantse-rantse yasa shi cewa ta dauko mishi tsintsiya. Sanda ta kira shi take fada mishi taci jarabawar aji shidda wato WAEC mamaki ya dingayi yanda rayuwar take wani irin sauri.
"Wayar waye wannan din?"
Shine tambayar da yayi mata a madadin tayata murnar cin jarabawar da ta fada mishi tayi
"Wayata ce, Abbu ya bani saboda naci exams dina"
Yanayin muryarta yasa shi gane ta turo bakinta ne take mishi magana
"Saina fasa bakin ki kina mun magana haka"
Shiru tayi, ya kashe wayar daga bangaren shi, kusan kullum sai ta kira shi, yana dagawa kuma gaisuwar shi itace
"Lafiya? Ko maitar ce ta motsa? Me yasa kike kirana?"
Amman ranar duk da bata kira shi ba, haka zai saka wayar a gaba yai ta kallo, ko yana aji wayar na silent, rabin hankalin shi yana kan darasin da ake musu, rabin hankalin shi na kan wayar. Ranar kuma saiya nemi dalilin da zai kirata, ko yace ta duba dakin su taga ko wani takalman shi ruwan kasa suna nan, ko kuma wata takarda da yasan babu ita sam-sam. Kawai yana dai son yaji muryarta ne. Yana fitowa daga wanka ya samu har filattai Bilal ya kawo, sai da ya samu riga da wando marassa nauyi ya saka a jikin shi ya feshe da turare kamar zai fita wani waje. Sai daya zauna yake jin gajiya sosai.
Filattan ya mika hannu ya dauka yana tashi tsaye. Inda ruwan leda yake jingine ya karasa ya fasa yana daukar guda daya. Bandaki ya shiga ya kara dauraye filattan ya dawo ya dauki cokulla suma ya dauraye. Bilal na kallon shi harya gama, da kan shi ya bude kulolin, wake da shinkafa ne, sai miyar kaji da kamshinta ya cika dakin.
"In zuba maka ko saika yi wanka?"
Rayyan ya bukata yana kallon Bilal
"Ka zuba mun"
Kai Rayyan ya girgiza
"Jikin ka baya maka danqo?"
Wani irin kallo Bilal yayi mishi
"Da ruwan sikari nayi wanka da safe? Ko motar sikari muka shigo?"
Murmushi Rayyan yayi da yake wahala kagani a fuskar shi. Amman sam jikin shi baya mishi dadi rana ta fito ta fadi bai cakar da Bilal din ba, bai ga hawaye a fuskar Layla ba, ko basa tare yana son yaji muryarta ta canza ta cikin waya alamar ta kwade shi a cikin tunaninta yafi a kirga
"Daga tambaya?"
Ya fadi yana mayar da hankalin shi kan abincin da yake zubawa a filet
"Akan me jikina zaiyi danqo to?"
Shiru Rayyan din yayi yana kyale shi, yana gama zuba abincin ya mayar da kulolin ya rufe, nashi filet din ya dauka yana gyara zaman shi kan kujera saboda yunwa yakeji ta fitar hankali, ko karin safe baiyi ba. Biscuit ne leda daya a cikin shi duk ranar. Bilal ya riga shi gama cin abincin, yana kallon shi ya wuce bandaki yayo wanka ya fito. Shadda ya saka a jikin shi harda hula, kafin wani lokaci ya fito das da shi. Wata leda Rayyan din yaga Bilal ya bude jakar shi ya zaro
"Na fita..."
Ya furta a hankali yana wucewa ya zira takalman daya fito dasu. Bangaren Ayya ya shiga yana samunta a zaune
"Sai ina haka? Anata baza kamshi"
Dariya yayi a kunyace
"Zan dan fita ne Ayya... Amman kafin Magriba in shaa Allah zan dawo, idan ba inda zakije da motar ki..."
Kafin ya karasa maganar ta katse shi da fadin
"Kaje ka dauki mukullin yana kan gado..."
Murmushin godiya yayi mata yana cire takalman shi ya wuce har can cikin dakin nata ya dauko, ya fito ne tace
"Ka gaishe ta"
Cike da kunya yace
"Ayya..."
Dariya tayi sosai, shima dariyar yayi yana wucewa har wajen motar Ayyar daya bude ya shiga. Saboda ita ya koyi tuqi tunda ta siyi motar da shiya fara sanin zata siyeta dan tare ma sukaje. Sai da ya tsaya yayi la'asar a hanya kafin ya nufi Kinkinau inda gidansu Aisha yake, har harabar gidan aka bude mishi ya shigar da motar yana fitowa, tsaye yayi a wajen ya kira wayarta. Daga inda yake tsaye yana hango ta tana saka hijabinta a bakin kofar da zata hadaka da cikin gidansu, kamar ta kasa jira ta saka daga cikin gida saboda zumudin da takeyi na son ganin shi.
"Allah ji nake kamar na dade banganka ba"
Ta furta bayan sun gaisa, dariyar shi yayi, yana kallon yanda sosai kominta yake mishi kamar Layla, har shigen yanda take magana, yanzun girma yasa yana ganin banbanci sosai a tsakanin su. Saboda tunda yake da Aisha zai kirga ranakun da ya taba ganin kalar kayanta, saboda hijabai take sakawa, hijabanta kuma masu hannune dogaye sosai har suna share titi, inba ranakun da ta saka abaya ba, ya hangi kala kalar kayan nata ta kasa. Layla kuwa hijabi wahala take mata, ranaku dai-daine zaka ganta da hijabi, ko in zataje islamiyya ko kuma tana idar da sallah ta fito daga daki kafin ta cire.
Yana son kalar shigar Aisha, saboda tattare take da mutunci na gaske, yanda Layla take saka kananun kaya ko skirt din da take tafiya dakyar a cikin shi yakan mishi tsaye a rai. Musamman idan yaga fita zatayi a hakan, zaita tunanin tarin mazan da zasu ganta da wannan shigar. Sai yaga har wani haske ke gilmawa ta cikin idanuwan shi saboda kishin da yakan taso mishi. Amman ita ko a jikinta, hannuwa Aisha ta tafa a saitin fuskar shi, tana saka shi ware mata idanuwan shi da sukafi komai yi mata kyau a tattarr da shi
"Tunanin me kakeyi?"
Kafadu yadan daga mata yanayin murmushi
"Kinyi kyau"
Ya furta a madadin tambayar da tayi mishi, kanta ta saddar kasa cikin jin kunyar shi
"Kaima kayi kyau ai"
Kai ya girgiza mata
"Idan banyi kyau bama ke ba zaki gani ba"
Dariya tayi sosai, akwai gaskiya a al'amarin shi, kullum kyau yake mata, tun bata da hankali har yanzun da tayi, soyayyar da take mishi mai girma ce, ba zata taba barinta taga wani aibu a tattare da shi ba. Yau ko da wani ne zai kawo mata zance marar kyau akan Bilal tana da yakinin zuciyarta ba zata taba aminta ba, ita bata ma yarda da yanda Ummi yayarta take cewa Rayyan yafi Bilal dinta kyau. Rayyan da ko fara'a bayayi, Bilal kuwa ko hada idanuwa kukayi zai maka murmushi. Ko kamar da ake cewa sunyi ita bata gani, nesa ba kusa ba Bilal yafi mata Rayyan kyau.
"Son da kike maine Allah. Amman Rayyan yana mun kyau tun muna makaranta"
Ummi ta fadi, haushima taji ta tashi tabar mata wajen. Da aji daya Ummi ta wuce ta, ita tun waccen shekarar ta zana jarabawa, jamb ce bataci ba, kuma ta nace sai ABU zataje. Ita Aisha bata taba tunanin zuwa wata ABU ba, dan duk kawayenta BUK suka nema. Saboda Bilal, dan ta samu damar ganin shi kullum ta biyewa Ummi suka nemi gurbin karatu a ABU din wannan shekarar tunda ita tayi sa'ar cinye jarabawar ta jamb.
"Sanda zan bar Zaria fa lokacin zaki shiga aji uku, haka ni zan dawo gida ki barni da kewar ki"
Cewar Bilal da ta fada mishi inda ta cike
"Zaka gane yanda nake ji duk idan kazo zaka koma"
Dariya yayi sosai
"Ramawa kike sonyi shisa kika zabi Zaria kenan ko?"
Ya tambaya yana sata dariya itama. Yanzun ma hira sukeyi, Aisha ce kawai take rike shi da hira haka har baya sanin lokaci yaja. Mamakin jin kiran magriba da akeyi sukayi
"Aisha kingani ko? Nace ma Ayya kafin Magriba zan koma"
Yanayin yanda yai maganar ya sata yin dariya
"Hamma Bilal..."
Layla ta fadi cikin sigar gaisuwa batare da ta kalle shi ba
"Layla..."
Ya amsa a sanyaye, yana shirin karawa da tambayar lafiyarta Rayyan ya dago, da bayan hannun shi ya kai ma Layla wani duka da yasa Bilal runtsa idanuwan shi kamar a kan shi hannun zai sauka, ya bude su a hankali yana ganin Layla da ta kauce tana kara turo baki
"Nace bai sharu ba kika tsaya gardama dani... Uban meye wannan?"
Ya karasa maganar yana nuna mata wata kasa da batasan daga inda ya sharota ba, saboda har karkashin gadon dakin nasu sai da ta share, kujerar shi da teburi kuwa daga su tayi ta ajiye a gefe, sif din kayan su har samanta sai da ta taka kujera ta share, haka ta sake takawa ta gogo daga saman zuwan jiki, tasan halin shi, dan yatsa zaisa ya dangwalo yaga ko da kura babu
"Wallahi shara hudu nayi Hamma"
Ta furta a gajiye, Rayyan din najan wani tsaki
"Ba abinda kika iya sai shirme..."
Ya fadi yana saka abin kwashe shara ya tattare kasar ya mika mata, karba tayi tana juyawa, shima cikin dakin ya shiga. Inda Bilal ya rufa mishi baya yana samarwa kulolin da suke hannun shi mazauni a tsakar dakin. Rayyan links din jikin rigar shi yake cirewa, dan manyan kayane a jikin shi, wani yadi ruwan kwai da ya sake fito da hasken fatar shi
"Ayya na tambayar ka"
Bilal ya fadi badan ya tsammaci amsa daga wajen Rayyan din ba, bai bashi amsar ba kuwa ya wuce yana nufar bandaki, dan ruwa kawai yake son watsawa. Tun da safe kafin su taho yace Layla ta bude dakin ta share musu. Yana saka kafar shi yaji kamar ya taka kasa. Wayarta da ta saukaka mishi komai yanzun ya kira
"Baki share dakin nan ba Layla"
Ya furta bayan ta daga, kafin ta amsa shi ya dora da
"Ki zo yanzun"
Gardamar da ta tsaya mishi da rantse-rantse yasa shi cewa ta dauko mishi tsintsiya. Sanda ta kira shi take fada mishi taci jarabawar aji shidda wato WAEC mamaki ya dingayi yanda rayuwar take wani irin sauri.
"Wayar waye wannan din?"
Shine tambayar da yayi mata a madadin tayata murnar cin jarabawar da ta fada mishi tayi
"Wayata ce, Abbu ya bani saboda naci exams dina"
Yanayin muryarta yasa shi gane ta turo bakinta ne take mishi magana
"Saina fasa bakin ki kina mun magana haka"
Shiru tayi, ya kashe wayar daga bangaren shi, kusan kullum sai ta kira shi, yana dagawa kuma gaisuwar shi itace
"Lafiya? Ko maitar ce ta motsa? Me yasa kike kirana?"
Amman ranar duk da bata kira shi ba, haka zai saka wayar a gaba yai ta kallo, ko yana aji wayar na silent, rabin hankalin shi yana kan darasin da ake musu, rabin hankalin shi na kan wayar. Ranar kuma saiya nemi dalilin da zai kirata, ko yace ta duba dakin su taga ko wani takalman shi ruwan kasa suna nan, ko kuma wata takarda da yasan babu ita sam-sam. Kawai yana dai son yaji muryarta ne. Yana fitowa daga wanka ya samu har filattai Bilal ya kawo, sai da ya samu riga da wando marassa nauyi ya saka a jikin shi ya feshe da turare kamar zai fita wani waje. Sai daya zauna yake jin gajiya sosai.
Filattan ya mika hannu ya dauka yana tashi tsaye. Inda ruwan leda yake jingine ya karasa ya fasa yana daukar guda daya. Bandaki ya shiga ya kara dauraye filattan ya dawo ya dauki cokulla suma ya dauraye. Bilal na kallon shi harya gama, da kan shi ya bude kulolin, wake da shinkafa ne, sai miyar kaji da kamshinta ya cika dakin.
"In zuba maka ko saika yi wanka?"
Rayyan ya bukata yana kallon Bilal
"Ka zuba mun"
Kai Rayyan ya girgiza
"Jikin ka baya maka danqo?"
Wani irin kallo Bilal yayi mishi
"Da ruwan sikari nayi wanka da safe? Ko motar sikari muka shigo?"
Murmushi Rayyan yayi da yake wahala kagani a fuskar shi. Amman sam jikin shi baya mishi dadi rana ta fito ta fadi bai cakar da Bilal din ba, bai ga hawaye a fuskar Layla ba, ko basa tare yana son yaji muryarta ta canza ta cikin waya alamar ta kwade shi a cikin tunaninta yafi a kirga
"Daga tambaya?"
Ya fadi yana mayar da hankalin shi kan abincin da yake zubawa a filet
"Akan me jikina zaiyi danqo to?"
Shiru Rayyan din yayi yana kyale shi, yana gama zuba abincin ya mayar da kulolin ya rufe, nashi filet din ya dauka yana gyara zaman shi kan kujera saboda yunwa yakeji ta fitar hankali, ko karin safe baiyi ba. Biscuit ne leda daya a cikin shi duk ranar. Bilal ya riga shi gama cin abincin, yana kallon shi ya wuce bandaki yayo wanka ya fito. Shadda ya saka a jikin shi harda hula, kafin wani lokaci ya fito das da shi. Wata leda Rayyan din yaga Bilal ya bude jakar shi ya zaro
"Na fita..."
Ya furta a hankali yana wucewa ya zira takalman daya fito dasu. Bangaren Ayya ya shiga yana samunta a zaune
"Sai ina haka? Anata baza kamshi"
Dariya yayi a kunyace
"Zan dan fita ne Ayya... Amman kafin Magriba in shaa Allah zan dawo, idan ba inda zakije da motar ki..."
Kafin ya karasa maganar ta katse shi da fadin
"Kaje ka dauki mukullin yana kan gado..."
Murmushin godiya yayi mata yana cire takalman shi ya wuce har can cikin dakin nata ya dauko, ya fito ne tace
"Ka gaishe ta"
Cike da kunya yace
"Ayya..."
Dariya tayi sosai, shima dariyar yayi yana wucewa har wajen motar Ayyar daya bude ya shiga. Saboda ita ya koyi tuqi tunda ta siyi motar da shiya fara sanin zata siyeta dan tare ma sukaje. Sai da ya tsaya yayi la'asar a hanya kafin ya nufi Kinkinau inda gidansu Aisha yake, har harabar gidan aka bude mishi ya shigar da motar yana fitowa, tsaye yayi a wajen ya kira wayarta. Daga inda yake tsaye yana hango ta tana saka hijabinta a bakin kofar da zata hadaka da cikin gidansu, kamar ta kasa jira ta saka daga cikin gida saboda zumudin da takeyi na son ganin shi.
"Allah ji nake kamar na dade banganka ba"
Ta furta bayan sun gaisa, dariyar shi yayi, yana kallon yanda sosai kominta yake mishi kamar Layla, har shigen yanda take magana, yanzun girma yasa yana ganin banbanci sosai a tsakanin su. Saboda tunda yake da Aisha zai kirga ranakun da ya taba ganin kalar kayanta, saboda hijabai take sakawa, hijabanta kuma masu hannune dogaye sosai har suna share titi, inba ranakun da ta saka abaya ba, ya hangi kala kalar kayan nata ta kasa. Layla kuwa hijabi wahala take mata, ranaku dai-daine zaka ganta da hijabi, ko in zataje islamiyya ko kuma tana idar da sallah ta fito daga daki kafin ta cire.
Yana son kalar shigar Aisha, saboda tattare take da mutunci na gaske, yanda Layla take saka kananun kaya ko skirt din da take tafiya dakyar a cikin shi yakan mishi tsaye a rai. Musamman idan yaga fita zatayi a hakan, zaita tunanin tarin mazan da zasu ganta da wannan shigar. Sai yaga har wani haske ke gilmawa ta cikin idanuwan shi saboda kishin da yakan taso mishi. Amman ita ko a jikinta, hannuwa Aisha ta tafa a saitin fuskar shi, tana saka shi ware mata idanuwan shi da sukafi komai yi mata kyau a tattarr da shi
"Tunanin me kakeyi?"
Kafadu yadan daga mata yanayin murmushi
"Kinyi kyau"
Ya furta a madadin tambayar da tayi mishi, kanta ta saddar kasa cikin jin kunyar shi
"Kaima kayi kyau ai"
Kai ya girgiza mata
"Idan banyi kyau bama ke ba zaki gani ba"
Dariya tayi sosai, akwai gaskiya a al'amarin shi, kullum kyau yake mata, tun bata da hankali har yanzun da tayi, soyayyar da take mishi mai girma ce, ba zata taba barinta taga wani aibu a tattare da shi ba. Yau ko da wani ne zai kawo mata zance marar kyau akan Bilal tana da yakinin zuciyarta ba zata taba aminta ba, ita bata ma yarda da yanda Ummi yayarta take cewa Rayyan yafi Bilal dinta kyau. Rayyan da ko fara'a bayayi, Bilal kuwa ko hada idanuwa kukayi zai maka murmushi. Ko kamar da ake cewa sunyi ita bata gani, nesa ba kusa ba Bilal yafi mata Rayyan kyau.
"Son da kike maine Allah. Amman Rayyan yana mun kyau tun muna makaranta"
Ummi ta fadi, haushima taji ta tashi tabar mata wajen. Da aji daya Ummi ta wuce ta, ita tun waccen shekarar ta zana jarabawa, jamb ce bataci ba, kuma ta nace sai ABU zataje. Ita Aisha bata taba tunanin zuwa wata ABU ba, dan duk kawayenta BUK suka nema. Saboda Bilal, dan ta samu damar ganin shi kullum ta biyewa Ummi suka nemi gurbin karatu a ABU din wannan shekarar tunda ita tayi sa'ar cinye jarabawar ta jamb.
"Sanda zan bar Zaria fa lokacin zaki shiga aji uku, haka ni zan dawo gida ki barni da kewar ki"
Cewar Bilal da ta fada mishi inda ta cike
"Zaka gane yanda nake ji duk idan kazo zaka koma"
Dariya yayi sosai
"Ramawa kike sonyi shisa kika zabi Zaria kenan ko?"
Ya tambaya yana sata dariya itama. Yanzun ma hira sukeyi, Aisha ce kawai take rike shi da hira haka har baya sanin lokaci yaja. Mamakin jin kiran magriba da akeyi sukayi
"Aisha kingani ko? Nace ma Ayya kafin Magriba zan koma"
Yanayin yanda yai maganar ya sata yin dariya