Sashe 22
Martabar Mu Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Hoton Layla, ba wasu kaya bane a jikinta ranar, uniform din islamiyya ne da hijabin take ruwan kasa mai cizawa, tana tsaye nesa da gida kadan ita da Farida, da littafi a hannun Farida din da alama suna duba wani abune, gefen fuskarta kawai yagani, sai yayi mishi kyau sosai, yanayin ta a hakan, da ta kare mishi idanuwanta. Tun ranar hoton yake manne a cikin kanshi, kamar yana son ya fito da shi fili kafin ya bace, ya kyale shine da nufin idanuwanta su tarwatsa mishi hoton, sai dai a satin ta saka idanuwan shi cikin nata yafi a kirga, amman tana barin wajen sai hoton ya dawo mishi, shisa yau yake son fito da shi, yana da tabbacin ba zai gamu a ranar ba, amman zak fito da taswirar, sai yayi sauran aikin ko idan ya koma ne. Ko ba komai zai sami abinyi kafin kewarta ta danne shi.
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 17, 2020
09
Shi sam baiga dalilin da Haris zaice tare zasu koma makaranta ba. Ya fahimci zumudin da Bilal yakeyi, duk da baiji shi ba sam a tafiyar farko da zaiyi. Yanzun ne yake jin dadi da Bilal din zai kasance makaranta daya da shi. Amman yana da tabbacin surutun da zasu dingayi shi da Haris kafin su sauka Zaria kan shi yayi ciwo. Shisa ya zabi yau din a matsayin ranar da zai koma, kawai saboda Haris yace zaiyi gaba, amman ya nace ya zauna jiran shi.
Yau ma tunda ya tashi yake jan jiki, duk da hakan na da alaka da hankalin shi gabaki daya da yake kan Layla. Sam baiji motsin ta ba, ya dade a bakin kofa da safe yana ganin shige da ficen yaran gidan har suka tafi makaranta, amman bai ganta ba, yaso ya tambayi wani ko jikin ne yasa bata fito ba, amman gaisuwar da suka dinga mishi ce tasa bakin shi yin nauyi saboda surutun har ya fara hawar mishi kai. Haka ya gaji ya koma, ga kasa da baisan waya shigo da ita dakin ba, sai da ya kara sharewa sau biyu tukunna yaji ya taka tsakar dakin da ya sha tayal ya mishi dai-dai.
"Kai fa muke jira... Kana ganin har biyu ta wuce, dare kake so muyi?"
Bilal ya fadi yana shigowa dakin, kafafuwan shi Rayyan ya bi da kallo
"Kai ka shigo da kasa, ban san sau nawa zance ka dinga cire takalminka a bakin kofa ba, har takalmi na siyo na yawo a daki, amman baka amfani da naka"
Numfashi Bilal ya sauke, yana zare takalman daga kafar shi, ya saka hannu ya dauka yana fitar dasu bakin kofa, kwana biyu da Rayyan din baya nan wannan ka'idojin na shi duk ya manta su, karasawa yayi ya zauna gefen gado
"Yanzun ba zaka wanke hannun ka ba, ka taba takalmi haka zaka kama kofi, yasa na daina hada kofuna da kai"
Numfashi mai nauyi Bilal yaja yana fitar wa
"Hamma ka sama mun lafiya, hannun ka ne ko nawa? Maganar da ake so kayi ba ita zakayi ba, sai kace bakin ka ya gaji da magana, amman baya taba gajiyawa kan tsegumi"
Duk surutun shi sama-sama Rayyan din yake ji, hankalin shi yayi nisa wajen tunanin ina da ina takalman Bilal din suka taka, wacce kazantar ya kwaso da su ya kuma saka hannu ya damuka, wannan matsalar shi ce kamar yanda ya fada, amman Rayyan din bayason yaje ya taba mishi wani abu da wannan hannun nashi daya dauki takalma. Ya dauka surutu da mutane ne abinda yafi tsana a zamantakewa, sai da ya fara girma yagane kazanta ce abinda yafi tsana, tsantsanin da yake da shi ba karami bane ba.
Lokutta da dama baka raba shi da karance-karance kan kwayoyin cutukan da suke rayuwa da mutane a mu'amalar yau da kullum. Yana son lafiyar shi, yana bala'in ririta lafiyar shi, tana jerin abu na farko da yake roka a dukkan addu'ar shi, shisa yake kara taka tsantsan idan ya tsare da iyawar shi, Allah saiya taimake shi. Dan ya kula mutane basu da wani buri daya wuce su ja mishi amai da gudawa. Haka shekaranjiya da suka dawo daga masallaci Bilal ya siyi wani rake, kuma har yake mishi tayi, tun suna hanya ya fara gabza kamar bashi da hankali.
"Ka tashi dan Allah ka shirya mu tafi"
Bilal din ya fadi yaba dorawa da
"Hamma..."
Ganin da yayi kamar Rayyan din baya jin shi, sai lokacin ya kalle shi
"Meye? Karka dameni, kuyi gaba da Hamma Haris mana, dole sai kun tafi dani?"
Ya karasa maganar yana mikewa, shi ya gama shiryawa, Layla ce baigani ba
"Ni na gama shiryawa, ka tashi..."
Rayyan ya furta kamar an mishi dole, mikewar yayi, kafin yai wani motsi Haris ya daga labulen dakin tare da yin sallama, idanuwan shi ya tsayar kan Bilal dan yasan ko Rayyan yayi wa magana kai tsaye ba lallai ya amsa shi ba
"Kun gama? Yamma nayi"
Kai Bilal ya daga mishi
"Yanzun zan kiraka daman"
Rayyan kuma Haris din yake kallo, muryar shi can kasan makoshi yace
"Hamma..."
Daga Haris din har Bilal kallon shi sukayi a tare, fuskokin su dauke da mamaki
"Layla fa?"
Ya furta har lokacin muryar shi daga kasan makoshi ta fito, kamar maganar na mishi wahalar gaske
"Bata da lafiya, ko makaranta bata je ba, tana ta amai jiya da dare, sai da sukaje asibiti da...."
Daga kan kalmar bata da lafiya bayajin wani abu ya kara zuwa kwakwalwar shi, zantukan duk da Haris yakeyi iya kunnuwan shi suka tsaya lokacin daya fara takawa, wuce Haris din da yayi a bakin kofa ya katse mishi maganar da yakeyi, takalma ya zira. A tsayin rayuwar shi ba zai iya tuna ranar karshe da ya taka bangaren Mami ba, ko Layla zai kira daga bakin kofa yake tsayawa ya kwala mata kira, idan bata nan Mami kan fito ko ta aiko a fada mishi bata nan, idan ita ta fito da kanta ta fadi juyawa yakeyi. Itama kamar tasan ba karamin taimako tayi mishi na saukakewa kanta yi mishi magana, haduwa hamsin in zasuyi zai matsa ta wuce ne, fuskarta ma baya kallo balle tasa ran zai gaisheta.
Inda sabo ta saba, a yaran dakin Ayya daga Khalifa sai Bilal ne suke gaishe da ita ko da yaushe, amman sauran sai randa suka ga dama, idan tayi musu magana dai suna amsawa, kuma babu wanda zatace ya taba mata rashin kunya. Amman ta kula ba ita kadai bace, kowane Rayyan baya kulawa, shisa bata taba kullatar shi ba. Amman yau babu wani tunani ya shiga dakin yana fadin
"Layla..."
Mami da take kitchen tana wanke-wanke sai da taji gabanta ya fadi, dan yau sai taji kamar a cikin dakinta Rayyan yayi magana, hakan ya sata tsame hannuwanta daga cikin ruwa tana fitowa, ganin shi tayi a tsaye, yau ya sauke idanuwan shi akan fuskarta
"Mami ina Layla?"
Ya furta, yana kara mata mamakin da takeyi, kafin ta iya cewa
"Tana dakinta"
Dan yau ikon Allah take gani muraran, bata taba jin sunanta a bakin shi ba, ta manta ranar karshe daya kalli fuskarta yayi magana da ita. Balle kuma ace ya taka dakin ta, amman yau Rayyan ne da kafafuwan shi a cikin dakinta, lallai kam abin babba ne. Shikam harya fara takawa yayi tunanin baisan inda dakin nata yake ba, juyowa yayi, Mami da tasan tambayar da zaiyi ta daga hannunta tana nuna mishi, baice komai ba ya nufi dakin.
"Allah Kai Ka san dai-dai..."
Mami ta furta a hankali tana komawa cikin kitchen dan karasa wanke-wanken ta. Tana barin Rayyan daya taka har kofar dakin da Mami ta nuna mishi yana Kwankwasawa
"Layla!"
Ya kira yana saka Layla da tun da ta farka cikin dare, magungunan da aka bata a asibiti suka saketa ta rasa abinda yake mata dadi a duniyar gabaki daya. A islamiyya ta sha cin karo da darussan da sukayi magana akan al'ada, menene ita al'adar da hukunce-hukuncen ta a tsari na addinin musulunci. Kuma tun da suke aji biyu a sakandire ta kanji wasu a ajin suna zancen. Sai dai babu wanda taji yana labarin ana shan irin wahalar da take sha tun jiya, mararta take ji tamkar wani ya saka shebir a ciki yana kwashe duk wani abu da bai mishi ba.
Ko numfashi dakyar take iya fitar da shi, bayanta da cinyoyinta a rike su. Har suna sakata tunanin ko jijiyoyin duk dayane suka fara daga bayan nata zuwa cikin cinyoyinta. Ciwo ne da bata taba sanin irin shi ba. Dan ita kabarta da zazzabi, shima sai Mami tayi da gaske zata zauna waje daya. Bata taba wata rashin lafiya da ta kwantar da ita waje daya haka ba. Tana juye-juye ne taji muryar Rayyan, dan kara dakuna fuska tayi dan a tunanin ta cikin kanta ne, dan ko dazun tayi tunanin harya wuce makaranta.
"Layla!!"
Ya kara fadi yana doka kofar fiye da sau daya kamar yanda yayi da farko, bata san lokacin da ta sauko daga kan gadon tana karasawa inda kofa take ba, kama hannun tayi ta murza tana bude mishi
"Hamma..."
Ta fadi cike da mamaki, da gaske shine
"Me ya same ki?"
Rayyan ya furta da damuwa kwance a fuskar shi, yanayin da ya dirar mishi da bakunta tunda ba sabawa yayi ba, idanuwanta ta sauke cikin nashi
"Ki daina kallona!"
Yai maganar a tsawace yana sakata sadda kanta kasa, idanuwanta na fara tara hawaye, nashi idanuwan Rayyan ya lumshe yana bude su a kanta, dai-dai lokacin da mararta tai wata irin murdawa, sai da ta rike kofar tana kiran sunan Allah, ba ita kadai ta rikice ba, hatta shi Rayyan din yanayinta ya ruda shi
"Wai me yake damun ki? Me asibiti suka ce yana damun ki? Kin sha magani?"
*
Littafina na siyarwa ne akan naira #300
Account details
3029530320
Lubabatu Sufyan
Polaris Bank
Whatsapp Number: 08074545149 (Domin tura shaidar biya)
1/30/21, 8:07 PM - 111: Nov 17, 2020
09
Shi sam baiga dalilin da Haris zaice tare zasu koma makaranta ba. Ya fahimci zumudin da Bilal yakeyi, duk da baiji shi ba sam a tafiyar farko da zaiyi. Yanzun ne yake jin dadi da Bilal din zai kasance makaranta daya da shi. Amman yana da tabbacin surutun da zasu dingayi shi da Haris kafin su sauka Zaria kan shi yayi ciwo. Shisa ya zabi yau din a matsayin ranar da zai koma, kawai saboda Haris yace zaiyi gaba, amman ya nace ya zauna jiran shi.
Yau ma tunda ya tashi yake jan jiki, duk da hakan na da alaka da hankalin shi gabaki daya da yake kan Layla. Sam baiji motsin ta ba, ya dade a bakin kofa da safe yana ganin shige da ficen yaran gidan har suka tafi makaranta, amman bai ganta ba, yaso ya tambayi wani ko jikin ne yasa bata fito ba, amman gaisuwar da suka dinga mishi ce tasa bakin shi yin nauyi saboda surutun har ya fara hawar mishi kai. Haka ya gaji ya koma, ga kasa da baisan waya shigo da ita dakin ba, sai da ya kara sharewa sau biyu tukunna yaji ya taka tsakar dakin da ya sha tayal ya mishi dai-dai.
"Kai fa muke jira... Kana ganin har biyu ta wuce, dare kake so muyi?"
Bilal ya fadi yana shigowa dakin, kafafuwan shi Rayyan ya bi da kallo
"Kai ka shigo da kasa, ban san sau nawa zance ka dinga cire takalminka a bakin kofa ba, har takalmi na siyo na yawo a daki, amman baka amfani da naka"
Numfashi Bilal ya sauke, yana zare takalman daga kafar shi, ya saka hannu ya dauka yana fitar dasu bakin kofa, kwana biyu da Rayyan din baya nan wannan ka'idojin na shi duk ya manta su, karasawa yayi ya zauna gefen gado
"Yanzun ba zaka wanke hannun ka ba, ka taba takalmi haka zaka kama kofi, yasa na daina hada kofuna da kai"
Numfashi mai nauyi Bilal yaja yana fitar wa
"Hamma ka sama mun lafiya, hannun ka ne ko nawa? Maganar da ake so kayi ba ita zakayi ba, sai kace bakin ka ya gaji da magana, amman baya taba gajiyawa kan tsegumi"
Duk surutun shi sama-sama Rayyan din yake ji, hankalin shi yayi nisa wajen tunanin ina da ina takalman Bilal din suka taka, wacce kazantar ya kwaso da su ya kuma saka hannu ya damuka, wannan matsalar shi ce kamar yanda ya fada, amman Rayyan din bayason yaje ya taba mishi wani abu da wannan hannun nashi daya dauki takalma. Ya dauka surutu da mutane ne abinda yafi tsana a zamantakewa, sai da ya fara girma yagane kazanta ce abinda yafi tsana, tsantsanin da yake da shi ba karami bane ba.
Lokutta da dama baka raba shi da karance-karance kan kwayoyin cutukan da suke rayuwa da mutane a mu'amalar yau da kullum. Yana son lafiyar shi, yana bala'in ririta lafiyar shi, tana jerin abu na farko da yake roka a dukkan addu'ar shi, shisa yake kara taka tsantsan idan ya tsare da iyawar shi, Allah saiya taimake shi. Dan ya kula mutane basu da wani buri daya wuce su ja mishi amai da gudawa. Haka shekaranjiya da suka dawo daga masallaci Bilal ya siyi wani rake, kuma har yake mishi tayi, tun suna hanya ya fara gabza kamar bashi da hankali.
"Ka tashi dan Allah ka shirya mu tafi"
Bilal din ya fadi yaba dorawa da
"Hamma..."
Ganin da yayi kamar Rayyan din baya jin shi, sai lokacin ya kalle shi
"Meye? Karka dameni, kuyi gaba da Hamma Haris mana, dole sai kun tafi dani?"
Ya karasa maganar yana mikewa, shi ya gama shiryawa, Layla ce baigani ba
"Ni na gama shiryawa, ka tashi..."
Rayyan ya furta kamar an mishi dole, mikewar yayi, kafin yai wani motsi Haris ya daga labulen dakin tare da yin sallama, idanuwan shi ya tsayar kan Bilal dan yasan ko Rayyan yayi wa magana kai tsaye ba lallai ya amsa shi ba
"Kun gama? Yamma nayi"
Kai Bilal ya daga mishi
"Yanzun zan kiraka daman"
Rayyan kuma Haris din yake kallo, muryar shi can kasan makoshi yace
"Hamma..."
Daga Haris din har Bilal kallon shi sukayi a tare, fuskokin su dauke da mamaki
"Layla fa?"
Ya furta har lokacin muryar shi daga kasan makoshi ta fito, kamar maganar na mishi wahalar gaske
"Bata da lafiya, ko makaranta bata je ba, tana ta amai jiya da dare, sai da sukaje asibiti da...."
Daga kan kalmar bata da lafiya bayajin wani abu ya kara zuwa kwakwalwar shi, zantukan duk da Haris yakeyi iya kunnuwan shi suka tsaya lokacin daya fara takawa, wuce Haris din da yayi a bakin kofa ya katse mishi maganar da yakeyi, takalma ya zira. A tsayin rayuwar shi ba zai iya tuna ranar karshe da ya taka bangaren Mami ba, ko Layla zai kira daga bakin kofa yake tsayawa ya kwala mata kira, idan bata nan Mami kan fito ko ta aiko a fada mishi bata nan, idan ita ta fito da kanta ta fadi juyawa yakeyi. Itama kamar tasan ba karamin taimako tayi mishi na saukakewa kanta yi mishi magana, haduwa hamsin in zasuyi zai matsa ta wuce ne, fuskarta ma baya kallo balle tasa ran zai gaisheta.
Inda sabo ta saba, a yaran dakin Ayya daga Khalifa sai Bilal ne suke gaishe da ita ko da yaushe, amman sauran sai randa suka ga dama, idan tayi musu magana dai suna amsawa, kuma babu wanda zatace ya taba mata rashin kunya. Amman ta kula ba ita kadai bace, kowane Rayyan baya kulawa, shisa bata taba kullatar shi ba. Amman yau babu wani tunani ya shiga dakin yana fadin
"Layla..."
Mami da take kitchen tana wanke-wanke sai da taji gabanta ya fadi, dan yau sai taji kamar a cikin dakinta Rayyan yayi magana, hakan ya sata tsame hannuwanta daga cikin ruwa tana fitowa, ganin shi tayi a tsaye, yau ya sauke idanuwan shi akan fuskarta
"Mami ina Layla?"
Ya furta, yana kara mata mamakin da takeyi, kafin ta iya cewa
"Tana dakinta"
Dan yau ikon Allah take gani muraran, bata taba jin sunanta a bakin shi ba, ta manta ranar karshe daya kalli fuskarta yayi magana da ita. Balle kuma ace ya taka dakin ta, amman yau Rayyan ne da kafafuwan shi a cikin dakinta, lallai kam abin babba ne. Shikam harya fara takawa yayi tunanin baisan inda dakin nata yake ba, juyowa yayi, Mami da tasan tambayar da zaiyi ta daga hannunta tana nuna mishi, baice komai ba ya nufi dakin.
"Allah Kai Ka san dai-dai..."
Mami ta furta a hankali tana komawa cikin kitchen dan karasa wanke-wanken ta. Tana barin Rayyan daya taka har kofar dakin da Mami ta nuna mishi yana Kwankwasawa
"Layla!"
Ya kira yana saka Layla da tun da ta farka cikin dare, magungunan da aka bata a asibiti suka saketa ta rasa abinda yake mata dadi a duniyar gabaki daya. A islamiyya ta sha cin karo da darussan da sukayi magana akan al'ada, menene ita al'adar da hukunce-hukuncen ta a tsari na addinin musulunci. Kuma tun da suke aji biyu a sakandire ta kanji wasu a ajin suna zancen. Sai dai babu wanda taji yana labarin ana shan irin wahalar da take sha tun jiya, mararta take ji tamkar wani ya saka shebir a ciki yana kwashe duk wani abu da bai mishi ba.
Ko numfashi dakyar take iya fitar da shi, bayanta da cinyoyinta a rike su. Har suna sakata tunanin ko jijiyoyin duk dayane suka fara daga bayan nata zuwa cikin cinyoyinta. Ciwo ne da bata taba sanin irin shi ba. Dan ita kabarta da zazzabi, shima sai Mami tayi da gaske zata zauna waje daya. Bata taba wata rashin lafiya da ta kwantar da ita waje daya haka ba. Tana juye-juye ne taji muryar Rayyan, dan kara dakuna fuska tayi dan a tunanin ta cikin kanta ne, dan ko dazun tayi tunanin harya wuce makaranta.
"Layla!!"
Ya kara fadi yana doka kofar fiye da sau daya kamar yanda yayi da farko, bata san lokacin da ta sauko daga kan gadon tana karasawa inda kofa take ba, kama hannun tayi ta murza tana bude mishi
"Hamma..."
Ta fadi cike da mamaki, da gaske shine
"Me ya same ki?"
Rayyan ya furta da damuwa kwance a fuskar shi, yanayin da ya dirar mishi da bakunta tunda ba sabawa yayi ba, idanuwanta ta sauke cikin nashi
"Ki daina kallona!"
Yai maganar a tsawace yana sakata sadda kanta kasa, idanuwanta na fara tara hawaye, nashi idanuwan Rayyan ya lumshe yana bude su a kanta, dai-dai lokacin da mararta tai wata irin murdawa, sai da ta rike kofar tana kiran sunan Allah, ba ita kadai ta rikice ba, hatta shi Rayyan din yanayinta ya ruda shi
"Wai me yake damun ki? Me asibiti suka ce yana damun ki? Kin sha magani?"